Sashe 74
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da takatsantsan ta sake tura ƙofar a hankali. Kamar yanda ta bar Mommahn yanzun ma tana kwance kan gadon kai ba za ka taɓa cewa akwai rai a tattare da ita ba. Amma saboda shegiyar zuciya irinta Maimuna ko kaɗan hakan be dameta ba, ita burinta ɗaya shi ne ta cika umarnin uwar ɗakinta. Ƙarasawa ta yi inda jinjirayen suke cikin zanin gado. Ta ƙarasa tana kallansu. Se ta yi maza ta ajje jaririn Mom a gefensu bayan ta gyara su ta haɗe su waje ɗaya, dan kuwa tun ɗazu da ta zo ta same su kowanne yana inda yake. Duk da yanda take sauri ta fice daga ɗakin, hakan be hanata ƙare musu kallo ba. Ɗaya idanunsa a rufe yake da alama ya yi kuka har ya gaji bacci ya ɗauke shi. Ya yin da ɗayan idanunsa biyu yana kukan da ba ya fita sosai. Dan ko sautinsa ba a iya ji sosai se ka matso kusa da shi. Ta jinjina kai lokacin da ta ga wani tsantar kyau a tattare da jariran, duk da ko a yanzun za ka fahimci babu kama ko kaɗan a tare da su amma kowanne Allah ya zuba kyau a tare da shi. Kuma ba za ka iya tantance wanda ya fi kyau ba, dan kuwa kowanne kyawunsa daban yake. Duk da a lokacin aka haife su hakan be hana komai fitowa ba tarr tarr ba, kamar misalin siririn dogon hanci, mitsitin baki da kuma manyan idanu. Ta kalli ɗan gidan Mom a fili ta furta
"Ikon Allah!!" Dan kuwa yaron ba dai hanci ba. Hancinsa irin na en gidansu Mom ne kamar an saka guduma an maida shi ciki. Duk da ko kaɗan be ɗauko kamar Mom ba amma a fizge yana kama da en gidansu Mom ɗin, har warɓeɓen bakin. (Astagfirullah)
Tuna kasassaɓar da take ƙoƙarin aikatawa ne ya sanyata juyawa ta kalli ƙofar ɗakin, kafin ta dawo da dubanta cikin ɗakin. Hannunta na wani irin karkarwa ta saka ta ɗauke su. Ta sanya su cikin hijab duk da yanda ƙafarta ta yi sanyi hakan be hanata ficewa daga ɗakin ba ƙirjinta na bugawa. Amma haka ta daure, ba tare da ta juya ba ta shige sashen Mom. Wata ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke lokacin da ta ganta cikin ɗakin Mom ɗin. Da sauri da sauri ta ƙarasa tana cigaba da sauke numfashi ta buɗe hijab ɗinta ta fito da su. Kawai miƙawa Mom da tun da ta shigo take kallanta ta yi ba tare da tace komai ba. Mom ta saka hannu ta karɓe su tana wata irin dariya saboda tsananin farin cikin da ta ji. Ta kalli yaran, irin kyawun da Allah ya basu kaɗai ya isa ya sa ta ji abin da ta aikata shi ne daidai. Kawai se ta rungumesu a ƙirjinta a fili tana furta
"Uwar biyu.." Ta ƙare tana murmushi.
"Kar ki yi haka Hajiya. Kar ki bar wata kafa da za ta kawo zargi a kan wannan haihuwar. Ki maida mata da yaro ɗaya, ko kuma ki san yanda za ki yi da shi. Amma dai kar ki riƙe su duka a matsayin kin haifi 'ya'ya biyu." Shiru Mom ta yi tanaa nazarin maganar Maimunan. Ta wani ɓangaren kamar ta faɗi gaskiya ne. Kar ta je hakan ya janyo zargi, ko kuma dai can wata matsalar daban. Ta sauke ajiyar zuciya tana juyawa ta kalli Maimuna
"Ya za a yi yanzu?" Shiru Maimuna ta yi tana tunanin abin da za tace. Kafin ta gama tunanin Mom ta sauko da jinjirayen tana kallansu. Ɗayan wanda yanzun ya yi shiru har kuma lokacin idanunsa a buɗe suke, se dai yana ta mutsu mutsu alamar ze iya cigaba da kukan da ya yi shiru yanzun shi Mom ta sake riƙewa. Ta kalli ɗayan da har lokacin yake bacci abinsa. Se ta miƙawa Maimuna shi tana faɗin
"Riƙe shi ki ga.." Babu musu ta saka hannu ta karɓe shi.
"Ki fitar da shi daga gidan nan. Duk inda za ki je ki je da shi. Yanzu ban san abin da zan ce a masa ba, zuwa anjima idan hankalina ya dawo jikina za ki ji kirana."
"Hakan mafita ce kuwa Hajiya?"
"Sosai kuwa.. Ke dai ɗauke shi kawai ki je." Se da ta sake sauke ajiyar zuciya sannan ta saka hannu ta ɗauke shi ta fice daga ɗakin duk da har lokacin tsoro ne fall a cikin ranta. Ba ta fita daga cikin gidan ba se da ta tabbatar babu wanda ya lura da jinjirin da ta ɓoye cikin hijab, kafin ta fice daga cikin gidan. Fitarta ke da wuya Baba Atine ta shigo cikin gidan, kai tsaye ɗakin Mommah ta wuce dan ta sanar da ita saƙon matar da ta aiketa wajenta. Se dai ta ji shiru cikin ɗakin. Hakan nan kawai ta ji hankalinta be kwanta ba, dan kuwa idan dai har sashen Mommahn a buɗe yake toh idanunta biyu, tana sallama za ta amsa ta fito, se kuma yau ta ji shiru Mommahn ba ta amsa ba, ga kuma ƙofar bedroom ɗin kusan a buɗe. Se ta ji tamkar ta shiga cikin ɗakin. Amma kuma hakan ba huruminta ba ne. Se kawai ta nemi waje ta zauna bayan ta sake yin sallama ba a amsa ba. Ta ɗauki wajen minti 10 zaune a palourn kafin daga bisani ta miƙe saboda yanda zuciyarta ta ƙi na'am da shirun Mommahn. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga. Se kuwa ta hangi Mommahn kwance, ga wani abu da take hanga kamar jinjiri cikin jini. Da sauri ta ƙarasa tana kiran sunan Allah. Kamar yanda idanunta suka nuna mata haka ɗin ne kuwa. Tsoro ya kamata ganin daga jinjirin har Mommahn babu wanda ke da alamar rai a tattare da shi. Jikinta na wani irin rawa ta fice daga ɗakin, sam ta ma manta akwai wasu halittun cikin gidan bayan su, kawai ta faɗa wani gida dake kusa da su. Bayan wajen minti 2 se ga ta sun dawo tare da maƙociyar tasu. Babu ɓata lokaci driver ya ɗauki Mommahn da Baba Atine se asibiti. Tun a mota Baba Atine ta karɓi wayar drivern babu ɓata lokaci ta kira Daddy ta sanar da shi abin da ke faruwa. Cikin tashin hankali ya baro inda yake, ko neman wani be yi ba da kansa ya hau mota dan wucewa asibitin. A kan hanya ya kira wayar Mom. Se dai ita ɗin ma se take sanar da shi babu lafiya. Tsoro ya kama shi, kawai se ya chanja akalarsa zuwa gidan, tun da ko babu komai ita yanzu Mommah za ta samu kulawar likitoci. Ita kuma Mom ta shaida masa babu kowa cikin gidan. Hakan ne ya sa ya wuce can ɗin. Da kukan jariri ya soma cin karo, be san lokacin da murmushi ya ƙwace masa ba. Ya ƙarasa yana karɓarsa daga hannun Mom ɗin. Se kuwa ta koma ta kwanta tana sauke numfashi a wahalce. Duk da dai da gasken jikinta babu daɗi, amma tana sane take ƙarawa dan Daddyn ya tausaya mata.
"Sannu Yallaɓiya.." Daddy ya faɗa yana kallanta. Se ta jinjina kai kawai ba tare da tace komai ba. Daddy ya rungume jinjirin duk da jikinsa babu kaya kuma ba a gyara shi ba, yana jin wata irin ƙaunarsa na ratsa shi. Be ɓata lokaci ba ya taimakawa Mom ɗin ya sanyata cikin mota se asibiti.
.. Kai tsaye lokacin da su Baba Atine suka isa asibitin ɗaki na musamman aka wuce da Mommah. Cikin lokaci ƙanƙani aka shiga bata taimakon gaggawa. Ya yin da tun gwadawar farko da likita ta yi wa jaririn ta tabbatar babu rai a tare da shi. Babu daɗewa su Daddy suka isa asibitin. Ita ma Mom ɗin karɓarta aka yi daga ita har jaririn dan duba lafiyarsa shi ma.
... "Ya jikin wife ɗin tawa?" Daddy ya faɗa yana kallan Likitar.
"Alhamdulillah jikinta da sauƙi.. Kuma In Sha Allah nan ba da jimawa ba za ta warke ma gaba ɗaya. Abin ne ya zo mata a juye.. Ga shi haihuwar fari, ga shi kuma a gida babu kowa. Hakan ya taka muhimmiyar rawa. Gaskiya dai Yallaɓai ba zan ɓoye maka ba ta ji jiki.. Se dai muna mata fatan samun lafiya ingantacciya nan ba da jimawa ba." Likitar ta ƙare tana jinjina kai. Fesar da iska Daddy ya yi daga bakinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya yace
"Allah Ya amince.. Zan iya ganinta?"
"Ehh babu damuwa Yallaɓai za ka iya ganinta.." ta ba shi amsa tana murmushi.
"Toh godiya nake.. Abin da ta haifa fa?" Daddy ya yi tambayar. Se ta ɗan yi shiru kamar ba za tace komai ba, se kuma ta ɗaga kai ta kalli Daddyn tace
"A yi haƙuri Alhaji.. Amma Allah ya yi masa rasuwa gaskiya tun da daɗewa kafin zuwansu asibiti."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un..!" Shi ne abin da Daddy ya faɗa har cikin ransa yana jin babu daɗi. Ya ɗan zame hularsa yana shafa kansa a hankali. Duk da yanda ya so ganin ɗan Mommahn da rai da lafiya, yanzu kuma ake faɗa masa ya rasu, hakan be kai yanda ya ji tausayin Mommahn ya kama shi ba.
"Allah Ya sa me ceto ne." Likitar ta faɗa tana kallan Daddy lokacin da ya miƙe.
"Ameen." Ya amsa da hakan yana ficewa daga Office ɗin.
A hankali ya ƙarasa cikin ɗakin yana kallan Mommahn da ke kwance idanunta a rufe tana bacci, kai da ka ganta ka san babu ƙarya ta sha wahala. Dan kuwa hatta a baccin da take za ka iya ganin yanda idanunta suka yi ciki, baccin kuma da ka gani za ka fahimci kawai tana yinsa ne ba dan tana jin daɗinsa ba. Wani sabon tausayinta ya kama shi, ya ƙarasa ya nemi waje ya zauna yana cigaba da kallanta cike da tausayawa. Ya kai wajen minti 5 cikin ɗakin kafin ya tashi ya fita daga ɗakin. Se a lokacin da ya ga gawar yaron ma sannan ya sake tausayawa Mommah. Ya sumbaci goshin yaron a fili ya furta
"Allah Ya bata wani me albarka.. Ya kuma ba ta lafiya.. Kai kuma Allah Ya sa me ceto ne."
"Ikon Allah!!" Dan kuwa yaron ba dai hanci ba. Hancinsa irin na en gidansu Mom ne kamar an saka guduma an maida shi ciki. Duk da ko kaɗan be ɗauko kamar Mom ba amma a fizge yana kama da en gidansu Mom ɗin, har warɓeɓen bakin. (Astagfirullah)
Tuna kasassaɓar da take ƙoƙarin aikatawa ne ya sanyata juyawa ta kalli ƙofar ɗakin, kafin ta dawo da dubanta cikin ɗakin. Hannunta na wani irin karkarwa ta saka ta ɗauke su. Ta sanya su cikin hijab duk da yanda ƙafarta ta yi sanyi hakan be hanata ficewa daga ɗakin ba ƙirjinta na bugawa. Amma haka ta daure, ba tare da ta juya ba ta shige sashen Mom. Wata ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke lokacin da ta ganta cikin ɗakin Mom ɗin. Da sauri da sauri ta ƙarasa tana cigaba da sauke numfashi ta buɗe hijab ɗinta ta fito da su. Kawai miƙawa Mom da tun da ta shigo take kallanta ta yi ba tare da tace komai ba. Mom ta saka hannu ta karɓe su tana wata irin dariya saboda tsananin farin cikin da ta ji. Ta kalli yaran, irin kyawun da Allah ya basu kaɗai ya isa ya sa ta ji abin da ta aikata shi ne daidai. Kawai se ta rungumesu a ƙirjinta a fili tana furta
"Uwar biyu.." Ta ƙare tana murmushi.
"Kar ki yi haka Hajiya. Kar ki bar wata kafa da za ta kawo zargi a kan wannan haihuwar. Ki maida mata da yaro ɗaya, ko kuma ki san yanda za ki yi da shi. Amma dai kar ki riƙe su duka a matsayin kin haifi 'ya'ya biyu." Shiru Mom ta yi tanaa nazarin maganar Maimunan. Ta wani ɓangaren kamar ta faɗi gaskiya ne. Kar ta je hakan ya janyo zargi, ko kuma dai can wata matsalar daban. Ta sauke ajiyar zuciya tana juyawa ta kalli Maimuna
"Ya za a yi yanzu?" Shiru Maimuna ta yi tana tunanin abin da za tace. Kafin ta gama tunanin Mom ta sauko da jinjirayen tana kallansu. Ɗayan wanda yanzun ya yi shiru har kuma lokacin idanunsa a buɗe suke, se dai yana ta mutsu mutsu alamar ze iya cigaba da kukan da ya yi shiru yanzun shi Mom ta sake riƙewa. Ta kalli ɗayan da har lokacin yake bacci abinsa. Se ta miƙawa Maimuna shi tana faɗin
"Riƙe shi ki ga.." Babu musu ta saka hannu ta karɓe shi.
"Ki fitar da shi daga gidan nan. Duk inda za ki je ki je da shi. Yanzu ban san abin da zan ce a masa ba, zuwa anjima idan hankalina ya dawo jikina za ki ji kirana."
"Hakan mafita ce kuwa Hajiya?"
"Sosai kuwa.. Ke dai ɗauke shi kawai ki je." Se da ta sake sauke ajiyar zuciya sannan ta saka hannu ta ɗauke shi ta fice daga ɗakin duk da har lokacin tsoro ne fall a cikin ranta. Ba ta fita daga cikin gidan ba se da ta tabbatar babu wanda ya lura da jinjirin da ta ɓoye cikin hijab, kafin ta fice daga cikin gidan. Fitarta ke da wuya Baba Atine ta shigo cikin gidan, kai tsaye ɗakin Mommah ta wuce dan ta sanar da ita saƙon matar da ta aiketa wajenta. Se dai ta ji shiru cikin ɗakin. Hakan nan kawai ta ji hankalinta be kwanta ba, dan kuwa idan dai har sashen Mommahn a buɗe yake toh idanunta biyu, tana sallama za ta amsa ta fito, se kuma yau ta ji shiru Mommahn ba ta amsa ba, ga kuma ƙofar bedroom ɗin kusan a buɗe. Se ta ji tamkar ta shiga cikin ɗakin. Amma kuma hakan ba huruminta ba ne. Se kawai ta nemi waje ta zauna bayan ta sake yin sallama ba a amsa ba. Ta ɗauki wajen minti 10 zaune a palourn kafin daga bisani ta miƙe saboda yanda zuciyarta ta ƙi na'am da shirun Mommahn. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga. Se kuwa ta hangi Mommahn kwance, ga wani abu da take hanga kamar jinjiri cikin jini. Da sauri ta ƙarasa tana kiran sunan Allah. Kamar yanda idanunta suka nuna mata haka ɗin ne kuwa. Tsoro ya kamata ganin daga jinjirin har Mommahn babu wanda ke da alamar rai a tattare da shi. Jikinta na wani irin rawa ta fice daga ɗakin, sam ta ma manta akwai wasu halittun cikin gidan bayan su, kawai ta faɗa wani gida dake kusa da su. Bayan wajen minti 2 se ga ta sun dawo tare da maƙociyar tasu. Babu ɓata lokaci driver ya ɗauki Mommahn da Baba Atine se asibiti. Tun a mota Baba Atine ta karɓi wayar drivern babu ɓata lokaci ta kira Daddy ta sanar da shi abin da ke faruwa. Cikin tashin hankali ya baro inda yake, ko neman wani be yi ba da kansa ya hau mota dan wucewa asibitin. A kan hanya ya kira wayar Mom. Se dai ita ɗin ma se take sanar da shi babu lafiya. Tsoro ya kama shi, kawai se ya chanja akalarsa zuwa gidan, tun da ko babu komai ita yanzu Mommah za ta samu kulawar likitoci. Ita kuma Mom ta shaida masa babu kowa cikin gidan. Hakan ne ya sa ya wuce can ɗin. Da kukan jariri ya soma cin karo, be san lokacin da murmushi ya ƙwace masa ba. Ya ƙarasa yana karɓarsa daga hannun Mom ɗin. Se kuwa ta koma ta kwanta tana sauke numfashi a wahalce. Duk da dai da gasken jikinta babu daɗi, amma tana sane take ƙarawa dan Daddyn ya tausaya mata.
"Sannu Yallaɓiya.." Daddy ya faɗa yana kallanta. Se ta jinjina kai kawai ba tare da tace komai ba. Daddy ya rungume jinjirin duk da jikinsa babu kaya kuma ba a gyara shi ba, yana jin wata irin ƙaunarsa na ratsa shi. Be ɓata lokaci ba ya taimakawa Mom ɗin ya sanyata cikin mota se asibiti.
.. Kai tsaye lokacin da su Baba Atine suka isa asibitin ɗaki na musamman aka wuce da Mommah. Cikin lokaci ƙanƙani aka shiga bata taimakon gaggawa. Ya yin da tun gwadawar farko da likita ta yi wa jaririn ta tabbatar babu rai a tare da shi. Babu daɗewa su Daddy suka isa asibitin. Ita ma Mom ɗin karɓarta aka yi daga ita har jaririn dan duba lafiyarsa shi ma.
... "Ya jikin wife ɗin tawa?" Daddy ya faɗa yana kallan Likitar.
"Alhamdulillah jikinta da sauƙi.. Kuma In Sha Allah nan ba da jimawa ba za ta warke ma gaba ɗaya. Abin ne ya zo mata a juye.. Ga shi haihuwar fari, ga shi kuma a gida babu kowa. Hakan ya taka muhimmiyar rawa. Gaskiya dai Yallaɓai ba zan ɓoye maka ba ta ji jiki.. Se dai muna mata fatan samun lafiya ingantacciya nan ba da jimawa ba." Likitar ta ƙare tana jinjina kai. Fesar da iska Daddy ya yi daga bakinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya yace
"Allah Ya amince.. Zan iya ganinta?"
"Ehh babu damuwa Yallaɓai za ka iya ganinta.." ta ba shi amsa tana murmushi.
"Toh godiya nake.. Abin da ta haifa fa?" Daddy ya yi tambayar. Se ta ɗan yi shiru kamar ba za tace komai ba, se kuma ta ɗaga kai ta kalli Daddyn tace
"A yi haƙuri Alhaji.. Amma Allah ya yi masa rasuwa gaskiya tun da daɗewa kafin zuwansu asibiti."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un..!" Shi ne abin da Daddy ya faɗa har cikin ransa yana jin babu daɗi. Ya ɗan zame hularsa yana shafa kansa a hankali. Duk da yanda ya so ganin ɗan Mommahn da rai da lafiya, yanzu kuma ake faɗa masa ya rasu, hakan be kai yanda ya ji tausayin Mommahn ya kama shi ba.
"Allah Ya sa me ceto ne." Likitar ta faɗa tana kallan Daddy lokacin da ya miƙe.
"Ameen." Ya amsa da hakan yana ficewa daga Office ɗin.
A hankali ya ƙarasa cikin ɗakin yana kallan Mommahn da ke kwance idanunta a rufe tana bacci, kai da ka ganta ka san babu ƙarya ta sha wahala. Dan kuwa hatta a baccin da take za ka iya ganin yanda idanunta suka yi ciki, baccin kuma da ka gani za ka fahimci kawai tana yinsa ne ba dan tana jin daɗinsa ba. Wani sabon tausayinta ya kama shi, ya ƙarasa ya nemi waje ya zauna yana cigaba da kallanta cike da tausayawa. Ya kai wajen minti 5 cikin ɗakin kafin ya tashi ya fita daga ɗakin. Se a lokacin da ya ga gawar yaron ma sannan ya sake tausayawa Mommah. Ya sumbaci goshin yaron a fili ya furta
"Allah Ya bata wani me albarka.. Ya kuma ba ta lafiya.. Kai kuma Allah Ya sa me ceto ne."