Sashe 20
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh madallah.." Baba Atine ta faɗa tana neman waje ta zauna. Se ta kamo hannun Didi ta zaunar da ita kan gadon sannan tace
"Maganar da muka yi.. Ki tashi ki je kitchen ki haɗa coffee ɗin ki kai masa." Ita da ma tunda Baban ta shigo ta ji jikinta ya yi sanyi. Har ga Allah ba ta son zancen nan, ba ta son sake shiga harkar mutumin. Se dai ta riga ta yi wa kanta alƙawarin yin biyayya a wannan auren da Abba ya ɗaura mata, dan haka ta buɗe baki da ƙyar tace
"Toh.."
"Yawwah ɗiyar albarka mu je na raka ki.." Baba Atine ta faɗa tana miƙewa. Babu musu Didi ta bita, se dai dukkan wata gaɓa ta jikinta a sanyaye take. Haka dai take ta giggimtsewa ka da ta bari zuciyarta ta karye tun yanzun. Har kitchen Baba Atinen ta rakata, sannan ta kalleta tace
"Wanne iri za ki yi?" Shiru Didi ta yi na en sakanni, kafin ta buɗe baki a sanyaye tace
"Cuppocino.." Jinjina kai Baba Atine ta yi tace
"Toh ya yi. Bari na je na dawo.."
"Toh.." Didi ta faɗa tana binta da kallo sanda take ficewa daga kitchen ɗin. Se a lokacin ta lumshe idanunta ƙirjinta na ɗan bugawa. Numfashi ta ja da ƙarfi ko za ta samu ta dena jin karyewar zuciyar, se dai har lokacin ba ta dena ji ba. Hakan ne ya sanyata juyawa ta shiga kallan cikin kitchen ɗin kamar me son gane abubuwan dake cikinsa.
A daidai bakin ƙofar sashen Baba Atine suka yi kaciɓus da Mom dake ƙoƙarin shigowa sashen. Tsayawa Mom ta yi tana kallanta da mamaki a kan fuskarta.
"Barka da wannan lokacin Hajiya.." Baba Atine ta faɗa cike da girmamawa. Kamar jira take yi, se a lokacin ta buɗe baki tace
"Me ya kawo ki nan?" Ta ƙare maganar tana buɗe hannunta alamar "mene ne"
"Amm Hajiya da ma.. da..ma.."
"Ke yi min shiru dallah.. munafunci ne ya kawo ki koh? Ko kuma ke ce er leƙen asirin da aka turo sashen nan? Munafuka?" Mom ta ƙare a zafafe. Girgiza kai Baba Atine ta yi kafin ta buɗe baki tace
"A'ah Hajiya, ba haka ba ne. Amma ki yi haƙuri.."
"Ɓace min da gani malama. An girma ba a dena munafunci ba." Ta ƙare tana sakin wani dogon tsaki kamar za ta tsinke harshenta. Jan ƙafafunta ta yi ta fice daga ɗakin, tana sake jin zafin maganganun da Mom ɗin ta faɗa mata. Ko babu komai ai ta girmeta. Ko da tana aiki ƙarƙashinsu be kamata ta dinga yi mata haka ba. Da wani banzan kallo Mom ta bi Baba Atine da shi, se da ta fice sannan ta dawo da dubanta cikin ɗakin tana sake sakin tsaki. Soma takawa ta yi, har zuwa inda ɗakin da Bad Man ya shiga yake. Knocking ta fara yi cike da fatan ba bacci yake ba. A daidai lokacin kuwa yana zaune kan bowl chair, gabansa kuma wata haɗaɗɗiyar kwalba ce da har wani sheƙi take yi kamar ba kwalba ba. Cups ne a gefen kwalbar har guda 3 duka ƙanana. Ɗaya na hannunsa ya watsa a cikin bakinsa idanunsa a lumshe. Kamar daga sama ya ji ana knocking ƙofar tasa. Kamar ba ze kula me knocking ɗin ba se kuma a hankali ya ɗaga kansa ya kalli ƙofar. Sake bugawar da aka yi ne ya sanya shi ɗan cije gefen lips ɗinsa sannan ya buɗe bakinsa yace
"Waye ne?" Ya faɗa da muryarsa da ta ɗan yi ƙasa.
"Ur Mom.. ka buɗe min ƙofar mana Boy.." Sake lumshe idanunsa ya yi, sannan ya dawo da dubansa kan abubuwan dake gabansa, kana ya ɗaga kansa ya sake maidawa kan ƙofar yace
"Bacci.."
"Ohhh sorry my dear.. Sleep well.. I will be back later.." ta faɗa cike da kulawa dan ba ta son abin da ze hana ɗan nata jin daɗi. Daga haka ta bar ƙofar ɗakin ta wuce part ɗinta.
Ba ta ɗauki mintuna masu yawa ba, ta fito daga cikin kitchen ɗin hannunta ɗauke da ƙaramin cup ɗin dake ɗauke da coffee ɗin dake ta tururi. Kallan ƙofar ɗakin ta yi, tana tunanin mafita. Dan ba ta san zuwa ɗakin bare ta gan shi. Se can wata dabara ta faɗo mata, dan haka ta cigaba da takawa zuwa ɗakin nasa. Ta kai wajen minti ɗaya tsaye ba tare da ta yi ƙoƙarin yin komai ba. Se kuma daga baya ta ɗaga hannunta ta shiga knocking ɗin ƙofar. Sake kallan ƙofar ya yi cike da mamakin abin da ya hana Mom ɗin tafiya. Ya ɗan fesar da iska daga bakinsa hannunsa cikin sumar kansa yana ɗan yamutsata. Kamar ba ze miƙe ba, kamar ba ze yi wani abu ba se kawai ya miƙe ya soma takawa zuwa bakin ƙofar, ya saka hannunsa dan buɗe ƙofar bayan ya yi blocking ko ina. Tunda ta ji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar se ta yi saurin ajje coffee ɗin ta koma gefe a guje ta ɓoye dan kar ya ganta. Da mamaki yake kallan cikin ɗakin sanda ya gama buɗe ƙofar ya ga babu kowa. Toh ina Mom ɗin take kenan? Kawai se ya taɓe baki yana ɗaga kafaɗarsa. Yana ƙoƙarin juyawa idanunsa suka sauka a kan coffee ɗin. Kamar me nazari ya zubawa coffee ɗin ido, se dai shi abin da ya ba shi mamaki, ashe duk wannan bugun tana yi ne kawai dan ta ba shi coffee? Lallai ma Mom.
"Oh god.." ya faɗa yana dafe goshinsa. Har ze tafi ya bar coffee ɗin se kuma ya juyo ya ɗauka ya koma cikin ɗakin. Ya ajje shi a gefe guda sannan ya cigaba da abin da yake yi. Se da ya sha ya yi tatil har se da kansa ya soma sara masa kamar yanda yake masa a kwanakin nan sannan ya ajje gefe. Ya koma ya kwantar da bayansa a kan kujera idanunsa a lumshe. Chewing gum ya fito da shi daga cikin wata er ƙaramar jaka me kyau. Yana shirin jefawa cikin bakinsa idanunsa suka sauka a kan wannan coffee ɗin. Kamar ya share, se kuma ya ji yana da buƙatarsa, musamman ma da Mom ɗin za ta ji daɗi idan ta ga ya sha. Hakan ne ya sanya shi ɗauka ya buɗe, take tururin da be gama fita ba ya soma tashi. Se da ya ɗan lumshe idanunsa sannan ya kai bakinsa ya soma sha. Ɗan yamutse fuska ya shiga yi jin ɗanɗanon ya fita daban da wanda Mom ɗin ke masa. Hakan ne ya sanya shi sauko da shi ya shiga kalla, kamar anan ze ga ainahin wadda ta yi shi. Se dai kuma da ya tuna ɗanɗano kan iya chanjawa, bugu da ƙari kuma ɗanɗanon ya masa daɗi se kawai ya kafa shi a bakinsa ya shanye tass..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO34*
___Wata ƙatuwar ajiyar zuciya Didi ta sauke sanda ta ji motsin rufe ƙofar. A hankali ta fito daga inda ta ɓoye tana kallan ƙofar, a tunaninta za ta ga kofin a inda ta ajje shi. Se dai ga mamakinta se ta ga babu komai a wajen. Sake dubawa ta yi ko dai ba ta gani da kyau ba, ta ga dai ba ta gan shi ba.
"Kenan ya ɗauka?" Ta tambayi kanta kamar tana jira wani ya ba ta amsa. Da dai ta ga babu me bata amsar se ta ɗauki ƙafarta ta soma takawa zuwa ɗakin da take zaune a ciki. Kai tsaye kan gado ta nufa ta haye. Babu ɓata lokaci ta ja bargo ta lulluɓe jikinta cike da fatan bacci ya zo ya ɗauketa, dan ba ta so Baba Atine ta dawo ta tambayeta yanda aka yi. Ba za ta iya mata ƙarya ba idan ta tambayeta, ba ta so kuma ta ga kamar ba ta isa da ita ba ne shi yasa taƙi shiga ɗakin. Runtse idanunta ta yi tana karanto addu'oi. Babu daɗewa kuwa bacci ya kwasheta me cike da mafarkin en gidansu da ta matuƙar yin kewarsu.
... Baccin da ya yi yau me yawa ne, dan shi kansa se da ya yi mamaki lokacin da ya farka ya ga tsawon awannin da ya kwashe yana baccin. Ya ɗan lumshe lumsassun idanunsa da suka ɗan ƙanƙance suka ƙara kyau, sanda ya gama shiryawa ya haɗe cikin wasu haɗaɗɗun tsadadddun kaya. Fitowa ya yi daga cikin ɗakin hannunsa ɗauke da wayarsa yana dannawa, da alama wani abun yake dubawa cikin wayar. Ko tsakiyar parlourn be kai ba Mommah ta shigo cikin sashen kamar ko yaushe ta yi kyau cikin wata tsadaddiyar atamfa da aka mata ɗinki me kyau. Be damu da motsin mutum ɗin da ya ji ba, se cigaba da takawa da ya yi, daidai ze giftata tace
"Areef.." Dakatawa ya yi saboda muryar da ya ji, ya kalleta da mamaki a kan fuskarsa. Be amsa kiran da ta masa ba se cewa ya yi
"Wani abu?" Girgiza kai Mommah ta yi tana murmushi tace
"A'ah kawai dai na zo wajen ɗiyata ne.."
"Ɗiyarki?" Ya tambaya yana kallanta. Se da ta gyara tsayuwarta sannan tace
"Wace ce ɗiyata kuma banda matarka Areef?" A kan laɓɓansa ya maimaita kalmar "Matata." Se kuma ya yi yaƙe yace bayan shi ma ya gyara tsayuwarsa
"Ina ganin mutuncinki Mommah.. So pls stay away from this matter.. Har yanzu am single, ba ni da wani abu me makamancin wannan sunan.." ya ƙare a fusace cike da jin haushin Mommahn. Girgiza kai Mommah ta yi tana sake mamakin halin Areef ɗin, da ba kowa ce sanadin lalacewarsa ba face mahaifiyarsa, wadda idan da za a kwana ana faɗar hakan ba za ta taɓa yarda ba.
"Banda abinka Areef me ye na.."
"Maganar da muka yi.. Ki tashi ki je kitchen ki haɗa coffee ɗin ki kai masa." Ita da ma tunda Baban ta shigo ta ji jikinta ya yi sanyi. Har ga Allah ba ta son zancen nan, ba ta son sake shiga harkar mutumin. Se dai ta riga ta yi wa kanta alƙawarin yin biyayya a wannan auren da Abba ya ɗaura mata, dan haka ta buɗe baki da ƙyar tace
"Toh.."
"Yawwah ɗiyar albarka mu je na raka ki.." Baba Atine ta faɗa tana miƙewa. Babu musu Didi ta bita, se dai dukkan wata gaɓa ta jikinta a sanyaye take. Haka dai take ta giggimtsewa ka da ta bari zuciyarta ta karye tun yanzun. Har kitchen Baba Atinen ta rakata, sannan ta kalleta tace
"Wanne iri za ki yi?" Shiru Didi ta yi na en sakanni, kafin ta buɗe baki a sanyaye tace
"Cuppocino.." Jinjina kai Baba Atine ta yi tace
"Toh ya yi. Bari na je na dawo.."
"Toh.." Didi ta faɗa tana binta da kallo sanda take ficewa daga kitchen ɗin. Se a lokacin ta lumshe idanunta ƙirjinta na ɗan bugawa. Numfashi ta ja da ƙarfi ko za ta samu ta dena jin karyewar zuciyar, se dai har lokacin ba ta dena ji ba. Hakan ne ya sanyata juyawa ta shiga kallan cikin kitchen ɗin kamar me son gane abubuwan dake cikinsa.
A daidai bakin ƙofar sashen Baba Atine suka yi kaciɓus da Mom dake ƙoƙarin shigowa sashen. Tsayawa Mom ta yi tana kallanta da mamaki a kan fuskarta.
"Barka da wannan lokacin Hajiya.." Baba Atine ta faɗa cike da girmamawa. Kamar jira take yi, se a lokacin ta buɗe baki tace
"Me ya kawo ki nan?" Ta ƙare maganar tana buɗe hannunta alamar "mene ne"
"Amm Hajiya da ma.. da..ma.."
"Ke yi min shiru dallah.. munafunci ne ya kawo ki koh? Ko kuma ke ce er leƙen asirin da aka turo sashen nan? Munafuka?" Mom ta ƙare a zafafe. Girgiza kai Baba Atine ta yi kafin ta buɗe baki tace
"A'ah Hajiya, ba haka ba ne. Amma ki yi haƙuri.."
"Ɓace min da gani malama. An girma ba a dena munafunci ba." Ta ƙare tana sakin wani dogon tsaki kamar za ta tsinke harshenta. Jan ƙafafunta ta yi ta fice daga ɗakin, tana sake jin zafin maganganun da Mom ɗin ta faɗa mata. Ko babu komai ai ta girmeta. Ko da tana aiki ƙarƙashinsu be kamata ta dinga yi mata haka ba. Da wani banzan kallo Mom ta bi Baba Atine da shi, se da ta fice sannan ta dawo da dubanta cikin ɗakin tana sake sakin tsaki. Soma takawa ta yi, har zuwa inda ɗakin da Bad Man ya shiga yake. Knocking ta fara yi cike da fatan ba bacci yake ba. A daidai lokacin kuwa yana zaune kan bowl chair, gabansa kuma wata haɗaɗɗiyar kwalba ce da har wani sheƙi take yi kamar ba kwalba ba. Cups ne a gefen kwalbar har guda 3 duka ƙanana. Ɗaya na hannunsa ya watsa a cikin bakinsa idanunsa a lumshe. Kamar daga sama ya ji ana knocking ƙofar tasa. Kamar ba ze kula me knocking ɗin ba se kuma a hankali ya ɗaga kansa ya kalli ƙofar. Sake bugawar da aka yi ne ya sanya shi ɗan cije gefen lips ɗinsa sannan ya buɗe bakinsa yace
"Waye ne?" Ya faɗa da muryarsa da ta ɗan yi ƙasa.
"Ur Mom.. ka buɗe min ƙofar mana Boy.." Sake lumshe idanunsa ya yi, sannan ya dawo da dubansa kan abubuwan dake gabansa, kana ya ɗaga kansa ya sake maidawa kan ƙofar yace
"Bacci.."
"Ohhh sorry my dear.. Sleep well.. I will be back later.." ta faɗa cike da kulawa dan ba ta son abin da ze hana ɗan nata jin daɗi. Daga haka ta bar ƙofar ɗakin ta wuce part ɗinta.
Ba ta ɗauki mintuna masu yawa ba, ta fito daga cikin kitchen ɗin hannunta ɗauke da ƙaramin cup ɗin dake ɗauke da coffee ɗin dake ta tururi. Kallan ƙofar ɗakin ta yi, tana tunanin mafita. Dan ba ta san zuwa ɗakin bare ta gan shi. Se can wata dabara ta faɗo mata, dan haka ta cigaba da takawa zuwa ɗakin nasa. Ta kai wajen minti ɗaya tsaye ba tare da ta yi ƙoƙarin yin komai ba. Se kuma daga baya ta ɗaga hannunta ta shiga knocking ɗin ƙofar. Sake kallan ƙofar ya yi cike da mamakin abin da ya hana Mom ɗin tafiya. Ya ɗan fesar da iska daga bakinsa hannunsa cikin sumar kansa yana ɗan yamutsata. Kamar ba ze miƙe ba, kamar ba ze yi wani abu ba se kawai ya miƙe ya soma takawa zuwa bakin ƙofar, ya saka hannunsa dan buɗe ƙofar bayan ya yi blocking ko ina. Tunda ta ji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar se ta yi saurin ajje coffee ɗin ta koma gefe a guje ta ɓoye dan kar ya ganta. Da mamaki yake kallan cikin ɗakin sanda ya gama buɗe ƙofar ya ga babu kowa. Toh ina Mom ɗin take kenan? Kawai se ya taɓe baki yana ɗaga kafaɗarsa. Yana ƙoƙarin juyawa idanunsa suka sauka a kan coffee ɗin. Kamar me nazari ya zubawa coffee ɗin ido, se dai shi abin da ya ba shi mamaki, ashe duk wannan bugun tana yi ne kawai dan ta ba shi coffee? Lallai ma Mom.
"Oh god.." ya faɗa yana dafe goshinsa. Har ze tafi ya bar coffee ɗin se kuma ya juyo ya ɗauka ya koma cikin ɗakin. Ya ajje shi a gefe guda sannan ya cigaba da abin da yake yi. Se da ya sha ya yi tatil har se da kansa ya soma sara masa kamar yanda yake masa a kwanakin nan sannan ya ajje gefe. Ya koma ya kwantar da bayansa a kan kujera idanunsa a lumshe. Chewing gum ya fito da shi daga cikin wata er ƙaramar jaka me kyau. Yana shirin jefawa cikin bakinsa idanunsa suka sauka a kan wannan coffee ɗin. Kamar ya share, se kuma ya ji yana da buƙatarsa, musamman ma da Mom ɗin za ta ji daɗi idan ta ga ya sha. Hakan ne ya sanya shi ɗauka ya buɗe, take tururin da be gama fita ba ya soma tashi. Se da ya ɗan lumshe idanunsa sannan ya kai bakinsa ya soma sha. Ɗan yamutse fuska ya shiga yi jin ɗanɗanon ya fita daban da wanda Mom ɗin ke masa. Hakan ne ya sanya shi sauko da shi ya shiga kalla, kamar anan ze ga ainahin wadda ta yi shi. Se dai kuma da ya tuna ɗanɗano kan iya chanjawa, bugu da ƙari kuma ɗanɗanon ya masa daɗi se kawai ya kafa shi a bakinsa ya shanye tass..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO34*
___Wata ƙatuwar ajiyar zuciya Didi ta sauke sanda ta ji motsin rufe ƙofar. A hankali ta fito daga inda ta ɓoye tana kallan ƙofar, a tunaninta za ta ga kofin a inda ta ajje shi. Se dai ga mamakinta se ta ga babu komai a wajen. Sake dubawa ta yi ko dai ba ta gani da kyau ba, ta ga dai ba ta gan shi ba.
"Kenan ya ɗauka?" Ta tambayi kanta kamar tana jira wani ya ba ta amsa. Da dai ta ga babu me bata amsar se ta ɗauki ƙafarta ta soma takawa zuwa ɗakin da take zaune a ciki. Kai tsaye kan gado ta nufa ta haye. Babu ɓata lokaci ta ja bargo ta lulluɓe jikinta cike da fatan bacci ya zo ya ɗauketa, dan ba ta so Baba Atine ta dawo ta tambayeta yanda aka yi. Ba za ta iya mata ƙarya ba idan ta tambayeta, ba ta so kuma ta ga kamar ba ta isa da ita ba ne shi yasa taƙi shiga ɗakin. Runtse idanunta ta yi tana karanto addu'oi. Babu daɗewa kuwa bacci ya kwasheta me cike da mafarkin en gidansu da ta matuƙar yin kewarsu.
... Baccin da ya yi yau me yawa ne, dan shi kansa se da ya yi mamaki lokacin da ya farka ya ga tsawon awannin da ya kwashe yana baccin. Ya ɗan lumshe lumsassun idanunsa da suka ɗan ƙanƙance suka ƙara kyau, sanda ya gama shiryawa ya haɗe cikin wasu haɗaɗɗun tsadadddun kaya. Fitowa ya yi daga cikin ɗakin hannunsa ɗauke da wayarsa yana dannawa, da alama wani abun yake dubawa cikin wayar. Ko tsakiyar parlourn be kai ba Mommah ta shigo cikin sashen kamar ko yaushe ta yi kyau cikin wata tsadaddiyar atamfa da aka mata ɗinki me kyau. Be damu da motsin mutum ɗin da ya ji ba, se cigaba da takawa da ya yi, daidai ze giftata tace
"Areef.." Dakatawa ya yi saboda muryar da ya ji, ya kalleta da mamaki a kan fuskarsa. Be amsa kiran da ta masa ba se cewa ya yi
"Wani abu?" Girgiza kai Mommah ta yi tana murmushi tace
"A'ah kawai dai na zo wajen ɗiyata ne.."
"Ɗiyarki?" Ya tambaya yana kallanta. Se da ta gyara tsayuwarta sannan tace
"Wace ce ɗiyata kuma banda matarka Areef?" A kan laɓɓansa ya maimaita kalmar "Matata." Se kuma ya yi yaƙe yace bayan shi ma ya gyara tsayuwarsa
"Ina ganin mutuncinki Mommah.. So pls stay away from this matter.. Har yanzu am single, ba ni da wani abu me makamancin wannan sunan.." ya ƙare a fusace cike da jin haushin Mommahn. Girgiza kai Mommah ta yi tana sake mamakin halin Areef ɗin, da ba kowa ce sanadin lalacewarsa ba face mahaifiyarsa, wadda idan da za a kwana ana faɗar hakan ba za ta taɓa yarda ba.
"Banda abinka Areef me ye na.."