Sashe 57
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Daddyyy.." ya ja ƙarshen sunan kamar me shirin faɗar abu me amfani.
"Ka ga Areef idan har za ka ɗauki matarka ne ku je wata ƙasar ina maraba da hakan. Dan na ze taɓa yiwuwa ka tafi wata ƙasar ka bar er mutane a cikin gidan nan ba. Idan kuwa har wannan ne kawai dalilinka toh ban amince ba. Se dai kuma idan har za ka tafi ne ba tare da izinina ba tun da yanzu ka girma." Shiru Bad Man ya yi ba tare da yace komai ba. Duk ya fahimci Daddyn ba ya son zuwa ko ina ne shi ɗaya. Shi ya sa yake ta kawo waɗannan ƙorafe ƙorafen. Shi kuma sa ya tafi da ita gwara gaba ɗaya ya haƙura da zuwa ko ma ina ne. Musamman ma kuma sa dama shi kansa ba son zuwa yake ba. Kawai dai yana ƙoƙarin bin umarnin Mom ne. Yanzu kuma da Daddy ya yi magana dole ya haƙura gaba ɗaya.
"Shi kenan.." ya ƙare daidai lokacin da ya miƙe yana kuma tura hannayensa cikin aljihun wandonsa.
"Ka da ka fita.. Akwai inda za ka raka ni anjima.."
"Tohm." Ya amsa a taƙaice yana ficewa daga ɗakin.
... Washegari kamar yanda suka yi da Bad Man ya shirya cikin shigar nan tasa. Zuwa lokacin tana zaune a kan gadon saboda Ummeey da ta hanata yawan kwanciyar. Sai dai ta kwantar da kanta ne a kan bangon gadon da alama tunani take yi. A nutse ya saci kallanta daga inda take zaune. Yanda ta sake zama wata shiru shiru hakan na matuƙar ba shi mamaki. Yana kuma sakawa duk ya ji jikinsa ya yi sanyi. Ya kuma dinga tunanin ko akwai wani abun da ke damunta? Da za ta iya ba shi dama da ya tambayeta ko wani abun na damunta ne ko kuma ta ba shi dama ya shiga rayuwarta sosai ko babu komai da yaddar Allah ze yi ƙoƙari wajen rage ko da kaso mara yawa ne daga yanayin da take ciki. Se dai kuma ya san ba ma za ta saurare shi ba musamman a yanzun da ko son ganinsa ba ta yi. Har a karon kansa kuma ba ya son yin nisa da ita bayan abin da ya faru. Duk da idan ya zauna ɗin ma ba wani abun za ta yarda ya yi mata ba. A nutse ya soma takawa zuwa wajen gadon. Ya ja side drawer ya zauna a kai yana cigaba da kallanta, duk da ba ya iya ganin fuskarta. Daidai lokacin da ta ɗago idanunta saboda motsin da ta ji se idanunta suka sauka a kansa. Ta sunkwui da kanta tana saka hannu ta ɗauke wata ƙwalla da ta sauka a gefen kumatunta.
"Ya ilahy.. Kuka ki ke? Me aka miki? Me yake damunki?" Duka ya jera tambayar ysvyi ts lokaci guda, duk da ya san ba lallai ta amsa masa ba. Jin shirun da ta yi kamar yanda ya tsammata ɗin kuwa ya sanya shi faɗin
"Ko Ammi ki ke so ki yi waya da ita? Ko kuma Afrah?" Ya tambaya yana kafeta da idanunsa. A yanda yake magana cike da rarrashi kai ba za ka taɓa cewa Gwani ba ne. Ba ta san lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi ba. Tana shirin cewa "Ehh" se kuma ta tuna abin da ya mata. Dan haka ta yi saurin maida kanta tana cuno baki daidai lokacin da idanunta suka tara ƙwalla. Ga samu ga rashi. Sauke numfashi ya yi yana kai hannunsa kan goshinsa ya ɗan murza sannan ya miƙe.
"Za ki kira su?" Karo na farko ts buɗe baki ba tare da ta kalle shi ba tace
"Ba na so.." Murmushi ya yi ko ba komai maganar ma da take masa ta fi shirun. Fiddo wayarsa ya yi daga cikin aljihu. Ya ajjeta kan gadon yace
"Ga shi nan ni zan fita.. Kar ma ki yi zaton ina cikin gidan nan ki ƙi ɗaukar wayar ki yi kira da ita.." ya ƙare yana soma takawa. Se kuma ya dakata ya yi shiru na en wasu mintuna kafin yace
"Amma ki sake min haƙuri.. Sannan ko ba dan komai ba ki min alƙawarin ba za ki faɗawa kowaccensu abin da ya faru ba." A karo na biyu yanzun ba ba shiri ta ɗaga ido ta kalle shi. Se ga idanunsu cikin na juna. Ya cije lips ɗinsa na ƙasa daidai lokacin da ya kashe mata ido ɗaya. Se ta yi saurin kawar da kanta tana maida kanta ta kwantar kamar wata munafuka. Au dama ya san ba ya so kowa ya ji me ya sa ya aikata? Se yanzu ze wani zo yace mata kar ta faɗa. Ehh tunda ma ga er iska ai dole ta je ta faɗa salon ita ma a koma yi mata kallan hakan.
A ranta tana sake mamakin halin Gwanin da ba su gano shi tun a makaranta ba se yanzu. Ta san kuma ko za ta kwana tana faɗawa wasu halin Gwanin na yanzu ba yadda za su yi ba. Burinta kawai ta neme shi cikin ɗakin ta rasa, dan har ga Allah tun da abin nan ya faru ita yanzu kallansa take kamar wani dodo. Sam ba ta ƙaunar ganinsa kusa da ita. Kamar kuwa ya san me take saƙawa se ya fice daga ɗakin yana murmushi. Se bayan wajen minti 3 da fitarsa sannan ta juya ta kalli kan gadon. Da gasken wayar tasa na ajjiye alamar ya barta ta yi kiranta. Ba ta san lokacin da murmushi ya ƙwace mata ba. Se ta yaye bargon da take lulluɓe ciki ta sauka a hankali dan har yanzu jikinta be gama warwarewa duka ba. Ƙaramin ɗakin nan ta shiga, wajen minti 2 ta dawo ta nemi waje ta zauna a kan gadon. Number Mommah da ke cikin takarda ta shigar cikin wayar tasa. Ta kara a kunnenta lokacin da ta soma ringing. Fatanta kawai a ɗaga ta ji muryar Didinta.
.. A ɗaya ɓangaren Mommah na zaune a ɗakinta kan kujera. Ya yin da Didi ke zaune a kan wata kujerar.
"Me kika shiryawa Abban naki?" Se da ta turo baki sannan tace
"Mommah yace wai Little kawai ze kawo.. Ze zo mana zuwa na musamman.."
"Toh madallah.. Allah Ya kawo su lafiya. Kin kira Ummeeyn kin mata ban gajiya?" Ɗaga ido Didi ta yi ta kalli Mommah, se kuma ta sauke su ƙasa.
"Mommah.." ta faɗa kamar me shirin faɗar wani abu, se kuma ta yi shiru.
"Babu damuwa.. in Sha Allah komai ze zo ƙarshe Uhmm? Kar ki damu.. ki cigaba da addu'a.. ki kuma cigaba da abin da kike yi ka da ki ce kin gaji. Areef na da wuyar sha'ani ne shi ya sa.." Murmushi kawai Didi ta yi. Har kullum mutuncin Mommahn ƙaruwa yake a idanunta. Musamman yanda ta iya amfani da kalaman rarrashi ko da ba ta da tabbaci a kan abun, duk dan ta kwantar mata da hankali.
"Ai se ki samu kirata ko a wayar Baba Atine ne.. Ba na so ne ki kirata a wayata saboda gudun tashin hankali, shi ya sa na ce ki karɓi tasa ki kirata. Se dai kuma tun da hakan be yiwuwa ba ki karɓi ta Baba Atinen se ki kirata.."
"Tohm shi kenan Mommah In Sha Allah.." Didi ta faɗa a sanyaye. Dan kuwa ita duk wani abu da ze haɗata da Mom ba son shi take yi ba. Se dai kuma a matsayinta na sirikarta yana da kyau duk abin da Mommahn ta sakata yi ta yi ko dan a zauna lafiya. Daidia lokacin kira ya shigo wayar Mommahn. Da yake tana kusa da ita se ta kalli me kiran. Jerin numbers ɗin da ta ga suna yawo a kan wayar su suka sanyata tsayawa tana kallan allon wayar. Dab da za ta tsinke ta ɗauka ta kara a kunnenta da sallama ɗauke a kan bakinta. Daga can ɓangaren Lulu da ta gama sarewa ta amsa sallamar. Da ƙyar ta iya tsayawa ta gaida Mommahn sannan ta ɗan yi shiru kafin tace kamar ba ita ba
"Don Allah ina neman Didina Afrah." Kallan Didi Mommah ta yi daidai lokacin da ta yi murmushi saboda jin muryar da ta yi sakk irin ta Didin.
"Bari a bata.." Daga haka ta miƙawa Didi wayar. Hannu Didi ta saka ta karɓa duk da bata san waye ba. Se dai haka nan kawai take ji a jikinta kamar er uwarta ce. Aikuwa tana kara wayar a kunnenta ta jiyo muryar Lulu.
"Luluna."
"Uhmm Didina.." Lulu ta faɗa a narke. Cikin lokaci ƙanƙani ƙwalla ta ciko idanun Didi. Ya yin da ita waccan uwar shagwaɓan ta kasa haƙura se da ta fashe da kuka.
"Me ya faru Lulu? Me ye kike kuka? Don Allah ki dena kin ji?" Ta tambayar tana bin bayan Mommah da ta miƙe ta bar wajen da kallo.
"Didi.."
"Na'am."
"Na yi kewarki sosai.. Ina ji kamar na yi tsintsuwa na zo na ganki." Murmushi me haɗe da hawaye Didi ta yi se kuma dan ta kawarwa da er uwar tata damuwa ya sanyata faɗin
"Ni ma haka Lulu.. Na ma fi yin kewarki fiye da yanda kika yi tawa. Amma kuma ma fa kullum ki na ganina.."
"Kaii.. yaushe ɗin?"
"Duk lokacin da kika kalli mudubi mana.." ta ƙare tana murmushi. Dariya Lulu ta yi sosai.
"Ka ga Areef idan har za ka ɗauki matarka ne ku je wata ƙasar ina maraba da hakan. Dan na ze taɓa yiwuwa ka tafi wata ƙasar ka bar er mutane a cikin gidan nan ba. Idan kuwa har wannan ne kawai dalilinka toh ban amince ba. Se dai kuma idan har za ka tafi ne ba tare da izinina ba tun da yanzu ka girma." Shiru Bad Man ya yi ba tare da yace komai ba. Duk ya fahimci Daddyn ba ya son zuwa ko ina ne shi ɗaya. Shi ya sa yake ta kawo waɗannan ƙorafe ƙorafen. Shi kuma sa ya tafi da ita gwara gaba ɗaya ya haƙura da zuwa ko ma ina ne. Musamman ma kuma sa dama shi kansa ba son zuwa yake ba. Kawai dai yana ƙoƙarin bin umarnin Mom ne. Yanzu kuma da Daddy ya yi magana dole ya haƙura gaba ɗaya.
"Shi kenan.." ya ƙare daidai lokacin da ya miƙe yana kuma tura hannayensa cikin aljihun wandonsa.
"Ka da ka fita.. Akwai inda za ka raka ni anjima.."
"Tohm." Ya amsa a taƙaice yana ficewa daga ɗakin.
... Washegari kamar yanda suka yi da Bad Man ya shirya cikin shigar nan tasa. Zuwa lokacin tana zaune a kan gadon saboda Ummeey da ta hanata yawan kwanciyar. Sai dai ta kwantar da kanta ne a kan bangon gadon da alama tunani take yi. A nutse ya saci kallanta daga inda take zaune. Yanda ta sake zama wata shiru shiru hakan na matuƙar ba shi mamaki. Yana kuma sakawa duk ya ji jikinsa ya yi sanyi. Ya kuma dinga tunanin ko akwai wani abun da ke damunta? Da za ta iya ba shi dama da ya tambayeta ko wani abun na damunta ne ko kuma ta ba shi dama ya shiga rayuwarta sosai ko babu komai da yaddar Allah ze yi ƙoƙari wajen rage ko da kaso mara yawa ne daga yanayin da take ciki. Se dai kuma ya san ba ma za ta saurare shi ba musamman a yanzun da ko son ganinsa ba ta yi. Har a karon kansa kuma ba ya son yin nisa da ita bayan abin da ya faru. Duk da idan ya zauna ɗin ma ba wani abun za ta yarda ya yi mata ba. A nutse ya soma takawa zuwa wajen gadon. Ya ja side drawer ya zauna a kai yana cigaba da kallanta, duk da ba ya iya ganin fuskarta. Daidai lokacin da ta ɗago idanunta saboda motsin da ta ji se idanunta suka sauka a kansa. Ta sunkwui da kanta tana saka hannu ta ɗauke wata ƙwalla da ta sauka a gefen kumatunta.
"Ya ilahy.. Kuka ki ke? Me aka miki? Me yake damunki?" Duka ya jera tambayar ysvyi ts lokaci guda, duk da ya san ba lallai ta amsa masa ba. Jin shirun da ta yi kamar yanda ya tsammata ɗin kuwa ya sanya shi faɗin
"Ko Ammi ki ke so ki yi waya da ita? Ko kuma Afrah?" Ya tambaya yana kafeta da idanunsa. A yanda yake magana cike da rarrashi kai ba za ka taɓa cewa Gwani ba ne. Ba ta san lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi ba. Tana shirin cewa "Ehh" se kuma ta tuna abin da ya mata. Dan haka ta yi saurin maida kanta tana cuno baki daidai lokacin da idanunta suka tara ƙwalla. Ga samu ga rashi. Sauke numfashi ya yi yana kai hannunsa kan goshinsa ya ɗan murza sannan ya miƙe.
"Za ki kira su?" Karo na farko ts buɗe baki ba tare da ta kalle shi ba tace
"Ba na so.." Murmushi ya yi ko ba komai maganar ma da take masa ta fi shirun. Fiddo wayarsa ya yi daga cikin aljihu. Ya ajjeta kan gadon yace
"Ga shi nan ni zan fita.. Kar ma ki yi zaton ina cikin gidan nan ki ƙi ɗaukar wayar ki yi kira da ita.." ya ƙare yana soma takawa. Se kuma ya dakata ya yi shiru na en wasu mintuna kafin yace
"Amma ki sake min haƙuri.. Sannan ko ba dan komai ba ki min alƙawarin ba za ki faɗawa kowaccensu abin da ya faru ba." A karo na biyu yanzun ba ba shiri ta ɗaga ido ta kalle shi. Se ga idanunsu cikin na juna. Ya cije lips ɗinsa na ƙasa daidai lokacin da ya kashe mata ido ɗaya. Se ta yi saurin kawar da kanta tana maida kanta ta kwantar kamar wata munafuka. Au dama ya san ba ya so kowa ya ji me ya sa ya aikata? Se yanzu ze wani zo yace mata kar ta faɗa. Ehh tunda ma ga er iska ai dole ta je ta faɗa salon ita ma a koma yi mata kallan hakan.
A ranta tana sake mamakin halin Gwanin da ba su gano shi tun a makaranta ba se yanzu. Ta san kuma ko za ta kwana tana faɗawa wasu halin Gwanin na yanzu ba yadda za su yi ba. Burinta kawai ta neme shi cikin ɗakin ta rasa, dan har ga Allah tun da abin nan ya faru ita yanzu kallansa take kamar wani dodo. Sam ba ta ƙaunar ganinsa kusa da ita. Kamar kuwa ya san me take saƙawa se ya fice daga ɗakin yana murmushi. Se bayan wajen minti 3 da fitarsa sannan ta juya ta kalli kan gadon. Da gasken wayar tasa na ajjiye alamar ya barta ta yi kiranta. Ba ta san lokacin da murmushi ya ƙwace mata ba. Se ta yaye bargon da take lulluɓe ciki ta sauka a hankali dan har yanzu jikinta be gama warwarewa duka ba. Ƙaramin ɗakin nan ta shiga, wajen minti 2 ta dawo ta nemi waje ta zauna a kan gadon. Number Mommah da ke cikin takarda ta shigar cikin wayar tasa. Ta kara a kunnenta lokacin da ta soma ringing. Fatanta kawai a ɗaga ta ji muryar Didinta.
.. A ɗaya ɓangaren Mommah na zaune a ɗakinta kan kujera. Ya yin da Didi ke zaune a kan wata kujerar.
"Me kika shiryawa Abban naki?" Se da ta turo baki sannan tace
"Mommah yace wai Little kawai ze kawo.. Ze zo mana zuwa na musamman.."
"Toh madallah.. Allah Ya kawo su lafiya. Kin kira Ummeeyn kin mata ban gajiya?" Ɗaga ido Didi ta yi ta kalli Mommah, se kuma ta sauke su ƙasa.
"Mommah.." ta faɗa kamar me shirin faɗar wani abu, se kuma ta yi shiru.
"Babu damuwa.. in Sha Allah komai ze zo ƙarshe Uhmm? Kar ki damu.. ki cigaba da addu'a.. ki kuma cigaba da abin da kike yi ka da ki ce kin gaji. Areef na da wuyar sha'ani ne shi ya sa.." Murmushi kawai Didi ta yi. Har kullum mutuncin Mommahn ƙaruwa yake a idanunta. Musamman yanda ta iya amfani da kalaman rarrashi ko da ba ta da tabbaci a kan abun, duk dan ta kwantar mata da hankali.
"Ai se ki samu kirata ko a wayar Baba Atine ne.. Ba na so ne ki kirata a wayata saboda gudun tashin hankali, shi ya sa na ce ki karɓi tasa ki kirata. Se dai kuma tun da hakan be yiwuwa ba ki karɓi ta Baba Atinen se ki kirata.."
"Tohm shi kenan Mommah In Sha Allah.." Didi ta faɗa a sanyaye. Dan kuwa ita duk wani abu da ze haɗata da Mom ba son shi take yi ba. Se dai kuma a matsayinta na sirikarta yana da kyau duk abin da Mommahn ta sakata yi ta yi ko dan a zauna lafiya. Daidia lokacin kira ya shigo wayar Mommahn. Da yake tana kusa da ita se ta kalli me kiran. Jerin numbers ɗin da ta ga suna yawo a kan wayar su suka sanyata tsayawa tana kallan allon wayar. Dab da za ta tsinke ta ɗauka ta kara a kunnenta da sallama ɗauke a kan bakinta. Daga can ɓangaren Lulu da ta gama sarewa ta amsa sallamar. Da ƙyar ta iya tsayawa ta gaida Mommahn sannan ta ɗan yi shiru kafin tace kamar ba ita ba
"Don Allah ina neman Didina Afrah." Kallan Didi Mommah ta yi daidai lokacin da ta yi murmushi saboda jin muryar da ta yi sakk irin ta Didin.
"Bari a bata.." Daga haka ta miƙawa Didi wayar. Hannu Didi ta saka ta karɓa duk da bata san waye ba. Se dai haka nan kawai take ji a jikinta kamar er uwarta ce. Aikuwa tana kara wayar a kunnenta ta jiyo muryar Lulu.
"Luluna."
"Uhmm Didina.." Lulu ta faɗa a narke. Cikin lokaci ƙanƙani ƙwalla ta ciko idanun Didi. Ya yin da ita waccan uwar shagwaɓan ta kasa haƙura se da ta fashe da kuka.
"Me ya faru Lulu? Me ye kike kuka? Don Allah ki dena kin ji?" Ta tambayar tana bin bayan Mommah da ta miƙe ta bar wajen da kallo.
"Didi.."
"Na'am."
"Na yi kewarki sosai.. Ina ji kamar na yi tsintsuwa na zo na ganki." Murmushi me haɗe da hawaye Didi ta yi se kuma dan ta kawarwa da er uwar tata damuwa ya sanyata faɗin
"Ni ma haka Lulu.. Na ma fi yin kewarki fiye da yanda kika yi tawa. Amma kuma ma fa kullum ki na ganina.."
"Kaii.. yaushe ɗin?"
"Duk lokacin da kika kalli mudubi mana.." ta ƙare tana murmushi. Dariya Lulu ta yi sosai.