Sashe 46
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
___Sabon al'amarin da ta ji wanda ba ta taɓa zata ba, ba kuma ta yi tsammani ba ya sanyata saurin wara idanunta. A matuƙar tsorace zuciyarta na wani irin harbawa kamar za ta bar ƙirjinta. Cikin sakannin da basu wuce a ƙirga su ba ta sanya hannunta bayan ta tattaro duk wani ƙarfi da take da shi ta sanya hannunta tana ƙoƙarin ture shi daidai lokacin da jikinta ya ɗauki rawa. Ba da niyyar komai ya haɗe bakin nasu waje ɗaya ba se dan kar ta yi ihun da ta saba. Se dai kuma yanda ya ji tana cigaba da ture shi a haukace ya sanya shi kamo lips ɗinta na ƙasa ya shiga kissing nata a nutse yana ƙoƙarin ganin ya saka idanunsa cikin ƙwayar idanunta. Se dai yanda cikin ƙanƙanin lokaci wata irin kasala ta rufe shi ya sanya shi lumshe idanunsa daidai lokacin da ya saki lips ɗin nata da niyyar sumbatar na sama. Ta yi wani yunƙuri ta janye bakinta da ƙarfi sannan cikin ƙarfin halin da ta aro ta zame jikinta daga nasa ba tare da samun wani tsaiko ba. Dan kuwa yanayin yanda ilahirin jikinta ke karkarwa ya fahimtar da shi yanda take a tsorace. Don haka kawai se ya saketa har lokacin idanunsa na a lumshe ne. Jikinta na wata irin karkarwa kamar wadda aka watsawa ruwa me masifaffan sanyi ta faɗa cikin wannan ƙaramin ɗakin wanda a nan aka zuba mata kayan kitchen ɗinta kamar wadda aka tunkuɗo. Wani marayan kuka ta fashe da shi lokacin da ta zube a ƙasa kamar wadda aka yi wa mutuwa. Ta kwantar da kanta a dandagaryar simintin ɗakin ta shiga rera kukan cikin matuƙar tsoro da bugun zuciyar da har yanzun be saitu ba. Kuka take kamar wadda aka ce mahaifiyarta ko mahaifinta ya rasu. Kuka irin me tsuma zuciyar me sauraro ɗin nan. Duka hannayenta biyun na kan laɓɓanta tana gogewa da ƙarfi kamar wadda za ta tsinka leɓen. Ta kasa dena kukan, ta kasa yin shiru. Ta kuma kasa dena goge bakinta da take ji har abada Gwanin ya gama cutarta. Hannu ta kai ta taɓa kanta dake a buɗe, ta kuma kalli jikinta dake a buɗe babu hijab bayan ta san da shi ta kwana, kenan duk shi ne ya cire mata? Ta sake fashewa da wani sabon kukan tana curewa waje ɗaya. Ba ta taɓa zaton ɗan iska ba ne shi se yau. Ta sake kai hannunta kan bakinta a karo na barkatai tana kuma dirjewa kamar me wanki. Manyan idanun nan nata sun yi luhu_luhu, har kuma lokacin ba ta dena kukan ba.
Zazzafar iska Gwani ya fesar lokacin da ya ji ta fashe da kukan. Be yi tunanin za ta ɗauki tsawon lokaci tana irin wannan kukan na tashin hankali ba. Dan kuwa har wani tsayawa take yi ta ajje wasu taggwan ajiyar zuciya sannan ta ɗora.
"Ya ilahy.." ya yi maganar yana ɗan shafa goshinsa. Yana zaune yana jiyo ta tana cigaba da kukan kamar ba ta da niyyar denawa. So yake ya tashi ya je duk da ya san ba ze iya rarrashinta ba ko me kuwa ze yi. Dan ya san idan ma zuwa ya yi dan rarrashin nata se dai ta tara masa jama'a. Kai yana ma da tabbacin ba za ta saurare shi ba. Ya ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa lokacin da ya gama tunanin. Lumshe idanunsa ya sake yi jin da ya yi har yanzu akwai zaƙin bakinta a kan nasa. Kamar wadda ta saka wani abu me zaƙi a kan laɓɓan nata. Ya miƙa hannu ya ɗan shafi lips ɗin, ya kalli hannun kafin ya ɗan yi wani murmushin yaƙe kana ya girgiza kai. Har bayan shuɗewar wasu mintuna masu yawa Lulu ba ta dena kuka ba. Se dai ba kamar ɗazu ba yanzu ta rage sautin ne da alama muryarta ta soma gajiya. A hankali ya miƙe daga kan gadon ya shiga takawa a nutse zuwa dakin. Tana zaune cure waje ɗaya tana cigaba da raira kukanta. Hannayensa duka biyun saƙale a ƙirjinsa ya shiga kallanta kamar me nazari.
"Ita wai ba ta gajiya da kuka ne?" Ya tambayi kansa har lokacin yana kallanta.
"Ki yi shiru ki dena kukan.." ya yi ƙarfin halin faɗin hakan a nutse. A matuƙar zabure ta miƙar da kanta daga kan cinyarta ta juya dan tabbatar da muryar da ta ji. Se kuwa suka yi 4 eyes. Ta buɗe baki da niyyar ƙwalla ƙara saboda yanda ta tsorata. Se ta tuna abin da ya faru yanzun nan, abin da ya sanyata fasawa kenan. Se ja da baya da ta yi a tsorace cikin muryarta da ta dashe saboda kukan da ta sha tace
"Ka fita.. ka fita.. ni ka fita.." ta faɗa tana girgiza kai wasu hawaye na zubowa a kan fuskarta lokaci ɗaya tana sake ƙanƙame jikinta. Ya gaji da ganin kukan gaba ɗaya dan haka cikin kwantar da murya yace
"Shi kenan.. Amma dai ki dena kukan nan" Daga haka ya fice daga ɗakin cike da mamaki. Shi kam har yanzu idan Lulun ta yi wani abu se ya dinga ganin kamar ba ita ba. Da ma haka take? Se tsiwa amma tsoro kamar farar kura. Daga sumbata kawai duk ta bi ta susuce ta rikirkice. Cigaba da zama ya yi a kan gadon se dai gaba ɗaya hankalinsa na cikin ɗakin ne. Ta ɓangarenta kuwa ko dan kar ya yi tunanin maganarsa ta ji shi ya sa ta dena yin kukan ya sanyata cigaba da yi cike da haushinsa da ya kasa sakinta. Har se da ta yi me isarta, ta gaji, jikinta ya mutu, kuzarinta ya ƙare sannan ta yi shiru ta koma sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin sannan shi ma ya sauke wata ajiyar zuciya yana sake furzar da iska daga bakinsa.
"Wannan yarinya.. Wannan yarinya.." ya faɗa a kan laɓɓansa yana girgiza kai.
Har wajen asuba daga shi har ita babu wanda ya runtsa. Shi hankalinsa gaba ɗaya na kanta, yayin da ita kuma take tsoron ta kwanta abin da ya faru ɗazu ya sake faruwa. Duk da wani irin gumi da take ta haɗawa cikin ɗakin saboda babu fanka amma hakan be sanyata fita daga ciki ba. Kafin asubar ta yi se ya miƙe ya faɗa toilet ya yi wanka kafin ya ɗauro alwala kamar ko yaushe. Be kalli ɗakin da take ba kai tsaye ya fice dan zuwa Masallaci. Ita sam ba ma ta san da fitarsa ba. Haka ta cigaba da zama cikin ɗakin kamar wata marainiya. Mintuna masu ɗan dama ya kwashe a masallacin kafin ya dawo duk dan saboda kar ya zauna ya dawo ya tarar da ita ba ta motsa a inda ya barta ba. Aikuwa kamar yanda ya tsammata ko da ya leƙa ɗakin tana nan zaune inda ya barta kamar wadda aka dasata. Ya girgiza kai yana sauke ajiyar zuciya.
"Tashi ki je ki yi sallah.." ya yi maganar lokacin da ya koma ainahin Gwaninsa. Shiru ta yi kamar ba ta ji ba tana cuccuno baki gami da haɗe rai. Ya fahimci ta ji abin da ya faɗa hakan ne ya sanya shi ƙarasa shigowa cikin ɗakin yace
"Shi kenan yi zamanki bari na taimaka miki.." ya yi maganar yana nufarta gadan gadan. A million ta miƙe jikinta na soma rawa ta fice daga ɗakin har kusan tuntuɓe ta yi. Ya yi murmushi me ƙayatarwa yana girgiza kai. Ficewa ya yi daga ɗakin ya nemi waje ya zauna dan yin karatu. Be sake bi ta kanta ba ya barta dan ta samu ta yi abin da ya dace. Aikuwa hakan ba ƙaramin daɗi ya mata ba. Dan kuwa har wanka se da ta yi, sannan ta dawo ta ɗebi kayanta ta wuce wannan ɗakin da yanzun zan iya kiransa da kitchen saboda kayan da ke cikinsa. Ko bayan ta gama abin da zata yi ma se ta cigaba da zama a ciki tunani fall cikin zuciyarta.
... "Ki ɗauka ki kira Abbanki.." ya yi maganar yana ajje mata wayar a gabanta. Ba ta ɗaga ido ta kalle shi ba se murguɗa baki da ta yi tana ɗauke kai. Shi ma be jira amsarta ba ya fice daga ɗakin. Bayan wajen minti 20 be sake shigowa cikin ɗakin ba. Wayar tasa kuma na ajje kusa da itan dai. Se a lokacin ta saci kallan wayar tasa. Se kuma a hankali ta miƙe cikin takatsantsan ta shiga leƙa palour dan tabbatar da yana ciki ko baya nan. Se da ta tabbatar baya nan sannan ta dawo ta ɗauki wayar cikin zumuɗi ta danno number Abba. Tun da ta soma ringing fuskarta take murmushi har zuwa lokacin da ya ɗaga.
"Hello Abba." Ta faɗa tana jin wani irin rauni na zuwar mata.
"Na'am Afaaf..." Daga can ɓangaren Abba ya faɗa yana jin daɗin jin muryar ɗiyar tasa. Kawai se ta shiga rera kuka kamar wadda aka yi wa wani abu. Miƙewa Abba ya yi daga inda yake zaune yace
"Me ya faru Lulu? Wani abun ya faru ne?" Girgiza kai ta shiga yi kamar Abban na gabanta. Se da ƙyar ta buɗe baki tace
"A'ah Abba babu komai.. Barka da wannan lokaci.." ta yi maganar a haɗe lokacin da ta goge hawayen fuskarta. Se a lokacin sannan Abba ya sauke ajiyar zuciya a ransa yana fata da addu'ar Allah ya sa i zuwa yanzu ɗiyar tasa ta yi haƙuri ta dangana da wannan aure.
"Toh kukan ya isa haka uhmm?" Kamar yana gabanta ta sake ɗaga kai tana murmushi. Babu laifi sun taɓa hira sosai irin wadda rabon da su yi ta tun kafin aurensu Lulun. Kafin daga bisani ya haɗata da Ammi dan su gaisa. Sosai suka yi hira inda Ammin ke sanar da ita ɗazun suka gama waya da Didi. Se da Lulu ta yi yanda za ta yi ta karɓi number da za ta samu Didi sannan suka cigaba da hirar.
"Babu dai wata damuwa koh?" Ammi ta tambaya cikin kulawa. Hannu Lulu ta saka ta sake goge bakinta se kace wadda aka ce mata Ammin za ta iya fahimtar wani abu. A shagwaɓe tace
"Babu komai Ammi."
Zazzafar iska Gwani ya fesar lokacin da ya ji ta fashe da kukan. Be yi tunanin za ta ɗauki tsawon lokaci tana irin wannan kukan na tashin hankali ba. Dan kuwa har wani tsayawa take yi ta ajje wasu taggwan ajiyar zuciya sannan ta ɗora.
"Ya ilahy.." ya yi maganar yana ɗan shafa goshinsa. Yana zaune yana jiyo ta tana cigaba da kukan kamar ba ta da niyyar denawa. So yake ya tashi ya je duk da ya san ba ze iya rarrashinta ba ko me kuwa ze yi. Dan ya san idan ma zuwa ya yi dan rarrashin nata se dai ta tara masa jama'a. Kai yana ma da tabbacin ba za ta saurare shi ba. Ya ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa lokacin da ya gama tunanin. Lumshe idanunsa ya sake yi jin da ya yi har yanzu akwai zaƙin bakinta a kan nasa. Kamar wadda ta saka wani abu me zaƙi a kan laɓɓan nata. Ya miƙa hannu ya ɗan shafi lips ɗin, ya kalli hannun kafin ya ɗan yi wani murmushin yaƙe kana ya girgiza kai. Har bayan shuɗewar wasu mintuna masu yawa Lulu ba ta dena kuka ba. Se dai ba kamar ɗazu ba yanzu ta rage sautin ne da alama muryarta ta soma gajiya. A hankali ya miƙe daga kan gadon ya shiga takawa a nutse zuwa dakin. Tana zaune cure waje ɗaya tana cigaba da raira kukanta. Hannayensa duka biyun saƙale a ƙirjinsa ya shiga kallanta kamar me nazari.
"Ita wai ba ta gajiya da kuka ne?" Ya tambayi kansa har lokacin yana kallanta.
"Ki yi shiru ki dena kukan.." ya yi ƙarfin halin faɗin hakan a nutse. A matuƙar zabure ta miƙar da kanta daga kan cinyarta ta juya dan tabbatar da muryar da ta ji. Se kuwa suka yi 4 eyes. Ta buɗe baki da niyyar ƙwalla ƙara saboda yanda ta tsorata. Se ta tuna abin da ya faru yanzun nan, abin da ya sanyata fasawa kenan. Se ja da baya da ta yi a tsorace cikin muryarta da ta dashe saboda kukan da ta sha tace
"Ka fita.. ka fita.. ni ka fita.." ta faɗa tana girgiza kai wasu hawaye na zubowa a kan fuskarta lokaci ɗaya tana sake ƙanƙame jikinta. Ya gaji da ganin kukan gaba ɗaya dan haka cikin kwantar da murya yace
"Shi kenan.. Amma dai ki dena kukan nan" Daga haka ya fice daga ɗakin cike da mamaki. Shi kam har yanzu idan Lulun ta yi wani abu se ya dinga ganin kamar ba ita ba. Da ma haka take? Se tsiwa amma tsoro kamar farar kura. Daga sumbata kawai duk ta bi ta susuce ta rikirkice. Cigaba da zama ya yi a kan gadon se dai gaba ɗaya hankalinsa na cikin ɗakin ne. Ta ɓangarenta kuwa ko dan kar ya yi tunanin maganarsa ta ji shi ya sa ta dena yin kukan ya sanyata cigaba da yi cike da haushinsa da ya kasa sakinta. Har se da ta yi me isarta, ta gaji, jikinta ya mutu, kuzarinta ya ƙare sannan ta yi shiru ta koma sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin sannan shi ma ya sauke wata ajiyar zuciya yana sake furzar da iska daga bakinsa.
"Wannan yarinya.. Wannan yarinya.." ya faɗa a kan laɓɓansa yana girgiza kai.
Har wajen asuba daga shi har ita babu wanda ya runtsa. Shi hankalinsa gaba ɗaya na kanta, yayin da ita kuma take tsoron ta kwanta abin da ya faru ɗazu ya sake faruwa. Duk da wani irin gumi da take ta haɗawa cikin ɗakin saboda babu fanka amma hakan be sanyata fita daga ciki ba. Kafin asubar ta yi se ya miƙe ya faɗa toilet ya yi wanka kafin ya ɗauro alwala kamar ko yaushe. Be kalli ɗakin da take ba kai tsaye ya fice dan zuwa Masallaci. Ita sam ba ma ta san da fitarsa ba. Haka ta cigaba da zama cikin ɗakin kamar wata marainiya. Mintuna masu ɗan dama ya kwashe a masallacin kafin ya dawo duk dan saboda kar ya zauna ya dawo ya tarar da ita ba ta motsa a inda ya barta ba. Aikuwa kamar yanda ya tsammata ko da ya leƙa ɗakin tana nan zaune inda ya barta kamar wadda aka dasata. Ya girgiza kai yana sauke ajiyar zuciya.
"Tashi ki je ki yi sallah.." ya yi maganar lokacin da ya koma ainahin Gwaninsa. Shiru ta yi kamar ba ta ji ba tana cuccuno baki gami da haɗe rai. Ya fahimci ta ji abin da ya faɗa hakan ne ya sanya shi ƙarasa shigowa cikin ɗakin yace
"Shi kenan yi zamanki bari na taimaka miki.." ya yi maganar yana nufarta gadan gadan. A million ta miƙe jikinta na soma rawa ta fice daga ɗakin har kusan tuntuɓe ta yi. Ya yi murmushi me ƙayatarwa yana girgiza kai. Ficewa ya yi daga ɗakin ya nemi waje ya zauna dan yin karatu. Be sake bi ta kanta ba ya barta dan ta samu ta yi abin da ya dace. Aikuwa hakan ba ƙaramin daɗi ya mata ba. Dan kuwa har wanka se da ta yi, sannan ta dawo ta ɗebi kayanta ta wuce wannan ɗakin da yanzun zan iya kiransa da kitchen saboda kayan da ke cikinsa. Ko bayan ta gama abin da zata yi ma se ta cigaba da zama a ciki tunani fall cikin zuciyarta.
... "Ki ɗauka ki kira Abbanki.." ya yi maganar yana ajje mata wayar a gabanta. Ba ta ɗaga ido ta kalle shi ba se murguɗa baki da ta yi tana ɗauke kai. Shi ma be jira amsarta ba ya fice daga ɗakin. Bayan wajen minti 20 be sake shigowa cikin ɗakin ba. Wayar tasa kuma na ajje kusa da itan dai. Se a lokacin ta saci kallan wayar tasa. Se kuma a hankali ta miƙe cikin takatsantsan ta shiga leƙa palour dan tabbatar da yana ciki ko baya nan. Se da ta tabbatar baya nan sannan ta dawo ta ɗauki wayar cikin zumuɗi ta danno number Abba. Tun da ta soma ringing fuskarta take murmushi har zuwa lokacin da ya ɗaga.
"Hello Abba." Ta faɗa tana jin wani irin rauni na zuwar mata.
"Na'am Afaaf..." Daga can ɓangaren Abba ya faɗa yana jin daɗin jin muryar ɗiyar tasa. Kawai se ta shiga rera kuka kamar wadda aka yi wa wani abu. Miƙewa Abba ya yi daga inda yake zaune yace
"Me ya faru Lulu? Wani abun ya faru ne?" Girgiza kai ta shiga yi kamar Abban na gabanta. Se da ƙyar ta buɗe baki tace
"A'ah Abba babu komai.. Barka da wannan lokaci.." ta yi maganar a haɗe lokacin da ta goge hawayen fuskarta. Se a lokacin sannan Abba ya sauke ajiyar zuciya a ransa yana fata da addu'ar Allah ya sa i zuwa yanzu ɗiyar tasa ta yi haƙuri ta dangana da wannan aure.
"Toh kukan ya isa haka uhmm?" Kamar yana gabanta ta sake ɗaga kai tana murmushi. Babu laifi sun taɓa hira sosai irin wadda rabon da su yi ta tun kafin aurensu Lulun. Kafin daga bisani ya haɗata da Ammi dan su gaisa. Sosai suka yi hira inda Ammin ke sanar da ita ɗazun suka gama waya da Didi. Se da Lulu ta yi yanda za ta yi ta karɓi number da za ta samu Didi sannan suka cigaba da hirar.
"Babu dai wata damuwa koh?" Ammi ta tambaya cikin kulawa. Hannu Lulu ta saka ta sake goge bakinta se kace wadda aka ce mata Ammin za ta iya fahimtar wani abu. A shagwaɓe tace
"Babu komai Ammi."