Sashe 23
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh.." Daga haka ta fice daga ɗakin. Kai tsaye kitchen ta nufa. Yau ma cikin ƙanƙanin lokaci ta gama. Ta juyo shi cikin cup ɗin sannan ta fito. Tunani ta shiga yi ko yau ma ta yi abin da ta yi rannan? Se dai kuma tana tsoro ka da rana ɗaya ya ganota ba ta san abin da ze mata ba, dan ba ta ga alamar mutunci a tattare da shi ba. Se dai koma mene ne da dai ta shiga ɗakin gwara ta tsaya a nan ɗin, idan ya so koma mene ne ze biyo baya ta san se daga baya. Hakan ne ya sanyata ƙarasawa ta shiga knocking ƙofar. Daidai lokacin da ma yana shirin fitowa ne. Tana kuwa jin alamar za a buɗe ta yi sauri ta ajje a ƙasa, har tana shirin yin tuntuɓe garin neman wajen ɓuya. Ko kuma meye ne ya manta se kuma ya koma cikin ɗakin. Bayan wajen minti 1 ya dawo ya buɗe ƙofar. Da mamaki yake kallan cup ɗin dake ɗauke da coffee kamar wancan karon. Kenan Mom ce yau ɗin ma ta yi ta ajje masa a nan? Amma me yasa ba za ta bari ya tashi ba? Ya tambayi kansa. Cikin lokaci ƙanƙani ya nemo amsar hakan, wato.. ba ta san takura masa ne. Taɓe baki ya yi, kamar ze yi ficewarsa daga ɗakin, se kuma ya saka hannu ya ɗauka ya koma cikin ɗakin. Neman waje ya yi ya zauna, ya ɗauki wayarsa ya shiga dannawa yana ɗan shan coffee ɗin lokaci zuwa lokaci. Be san yanda aka yi yanzu Mom ta fi iya coffee ba, se dai be sani ba ko ta sake neman yanda za ta ƙware ne dan faranta masa. Ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yake shan coffee ɗin a ransa yana sake yaba daɗinsa, wanda idan a fuska kake kallansa ba zaka taɓa tunanin ya masa daɗi ba. Dan kuwa babu wata alama da ta nuna yana jin daɗin abin da yake sha ɗin.
... Little se wasansa yake a ɗakin hankalinsa kwance babu wata damuwa. Dan tunda ya tashi yake kuka, amma yana ganin Lulu kukan ya ɗauke gaba ɗaya. Tana nannaɗe cikin hijab ɗinta tana kallansa, lokaci lokaci ta kan yi murmushi, idan ya yi wani abun kuma ta yi dariya.
"Ba ki da lafiya?" Ya tambaya yana kallanta sanda ya tsaya da wasan da yake yi. Jinjina kai ta yi fuskarta a narke tace
"Ehh.."
"Toh ki sha magani.." ya faɗa a sakarce ba tare da bawa zancen nasa muhimmanci ba ya cigaba da abin da yake yi. Ta yunƙura za ta miƙe daga kan gadon ta jiyo muryarsa ya yi sallama cikin ɗakin. Shiru ta yi ba tare da ta amsa ba, se Little da ya amsa yana ƙarasawa ya rungume shi.
"Areef.." ya faɗa yana murmushi, se kuma ya ɗora da
"Ina Auntynka?"
"Tana kan gado. Ba ta da lafiya.."
"Je ka ce mata ta shirya mu tafi asibiti.." Gwani ya faɗa yana kallan Little. Dan tabbatar da ya ji abin da ya faɗa ya sanya shi faɗin
"Me za ka ce?" Se kuwa ya maimaita masa tiryan tiryan. Se a lokacin ya saki hannunsa, shi kuma ya tafi da sauri yana kiran sunan Lulu.
"Ya sayyadi yace ki zo ya kai ki asibiti.." ya faɗa yana yaye hijab ɗin da ta lulluɓa da shi.
"Je ka ce ba za ni ba.."
"A'ah.. ni dai ki taso mu je.." Galla masa harara ta yi tana miƙewa a kan gadon tace
"Wallahi zan ɓallaka idan ba ka bar wajen nan ba.." Hannu ya ɗaga ya kai kan idanunsa da suka fara yin rau rau. Ganin da gasken kuka ze yi ya sanyata saurin riƙo hannunsa tana faɗin
"Toh yi haƙuri na dena maka faɗa ka ji?" Ta tambaya tana narkar da fuskarta ita ma. Turo baki ya yi kawai be ce komai ba. Lulu tace
"Kaa ji sweetienah?" Ta faɗa tana jan kumatunsa. Se a lokacin ya yi murmushi sannan ya fice a guje ya koma wajen Gwani. Kamar yadda ta faɗa ɗin haka ya faɗa. Ya ɗan cije lips ɗinsa yana sauke ajiyar zuciya. Se kuma ya jinjina kai kawai be ce komai ba, ya kama hannun Little yace
"Je ka duba min me Ummeey take yi.." Babu musu Little ya fice daga ɗakin. Shi kuma ya wuce zuwa inda gadon yake.
"Na baki minti 10 ki shirya.. Idan ba haka ba in zo in shiryaki da kaina.." ya faɗa dan yanzu ya riga ya gane lagonta, idan kuwa har haka ne ze dinga amfani da hakan wajen sakata yin wasu abubuwan ko da kuwa ba ta yi niyya ba. Ɗaga ido ta yi ta maka masa harara a ɗan tsorace dan kar ya ganta. Se dai ba ta san sarai ya ganta ba, amma sam be nuna ya ganta ba. Ita yanzu ma idan ta yi abu dariya take ba shi musamman da ya lura duk wannan rashin kunyar ashe matsoraciyar banza ce.
"Kin zaɓi ɗayan kenan? Ya yi.." ya yi maganar yana soma takawa zuwa wajen gadon. Durowa ta yi daga kan gadon rai a ɓace duk da yanda ƙirjinta ke bugawa be hanata cewa
"Ai dai na ga jikina ne, kuma cikina ke ciwo. Ka ƙyale ni mana ai dama so nake na mutu a zo a ɗauki gawata a fitar da ita daga cikin gidan nan. Saboda haka ka fita a harkata ka ƙyale ni.." ta yi maganar cikin ƙarfin hali wanda a fuska ba za ka taɓa fahimtar hakan ba, se dai a zuciya ita kaɗai ta san tsoron da take ji. Ɗan luu Gwani ya yi da idanunsa kamar ze lumshesu se kuma ya buɗe su ya sauke su a kan Lulu. Yana mamakin jin furucin bakinta. Kenan tsanar da ta masa har ta kai ta dinga yi wa kanta fatan mutuwa. Ba ma iya nan ba, har ta yi abin da ta san ze janyo mata rashin lafiya may be ma daga nan ta rasa ranta? Kautad da idanunta ta yi saboda yanda ta ji bugun zuciyarta ya ƙaru tun lokacin da ya zuba mata idanun nan nasa.
"Ki chanja wata hanyar ba dai wannan ba, dan ba za ta ɓille miki ba. And magana ta ƙarshe.. ki wuce ki shirya, ko kuma wallahi ki ga abin da zan yi.." ya ƙare a ɗan fusace duk da yanda yake tausar zuciyarsa a kan Lulun. Banda haka da ƙyaleta ze yi ta yi abin da ta ga dama tunda har yanzu ba ta da hankali. Se dai koma mene ne tana ƙarƙashin kulawarsa ne, kuma daga lokacin da ya yi fatali da wannan nauyin dake kansa ya san shi ɗin me laifi ne. Jin yanda ya yi magana da kallan da yake jefa mata ya sanya yana ficewa daga ɗakin ta ɗauki hijab ta saka tana jin wani kuka na taho mata. Allah ma ya gani yanzu tsoron Gwanin take ji, ko da rashin kunyar za ta yi a tsorace take yinta. Ga shi yanzu ma ta ga kamar ba ya jin rashin kunyar, dan idan ma yana ji ita dai ba ta lura da hakan ba. Dan ko da za ta masa ɗin hakan ba ze hana shi yin abin da ya yi niyya ba. Se da ta ɗauki wajen minti 12 sannan ta fito tana ta ciccin magani. A tsakar gida ta taddasu shi da Ummeey har ma da Little. Ummeey na ganinta tace
"Sannu kin ji ɗiyata.. Wallahi ga shi kuwa har kin faɗa.. Sannu kin ji?" Ta faɗa tana kallanta.
"Yawwah.." shi ne kawai abin da Lulu ta faɗa tana riƙe hannun Little da ya je wajenta.
"Ummeey bari mu je.." Gwani ya faɗa cikin nutsuwa.
"Toh Allah ya tsare.. ya kuma ba da lafiya.." Ai tunda Little ya gansu cikin shirin fita ya ƙi yadda ya je wajen Ummeey, haka Ummeeyn ta haƙura tace su je tare. Hannun Little cikin na Lulu suka fito zuwa ƙofar gidan. Gwani na gaba yayin da su suke baya, Lulu se raka shi da wata uwar harara take yi, ga haushinsa dama da take ji ga kuma wata tafiya da yake yi kamar ɗan gidan sarakai ko wani me muƙami. Daidai lokacin da suka fito Abbati ma ya iso ƙofar gidan. Hango shi da Gwani ya yi ne ya sanya shi datakawa, yayin da Lulu da Little suka cigaba da tafiya. Tun daga nesa kuma se kallan Abbati ya koma kan Little da kuma Lulu, har wani ƙanƙance idanunsa yake yi dan yafi ganin daidai. Kallan Little Abbati ya sake yi, ya sake satar kallan Lulu da fuskarta ke a cunkushe kamar za ta kai wa duk wanda ya mata magana duka. Ɗaga idanunsa da Gwani ze yi se ya tsinci idanun Abbati a kan Lulun. Ya juya ya kalli Lulun dan tabbatarwa da gasken ita yake kalla? Se kuwa ya kama shi dumu_dumu yana kallan nata. Duk da ba sonta yake yi ba, amma ko babu komai matarsa ce a yanzun. Ko babu komai ba ze so ganin wani ɗa namiji na kallanta ba tunda dai matar aure ce. Shi ya sa tun ɗazu kafin su fito yake tunanin samo mata niƙab dan ta saka. Se dai kuma be san wata fassara za ta masa ba. Se dai koma mene ne daga yau ɗin ko wacce fassara za ta masa, kome kuma za tace ba za ta sake fita daga cikin gidan nan ba se da niƙab, dan ko babu komai yanzun mallakinsa ce. Shi kuma yana da wani abu, duk wani abu da ya kasance nasa, toh burinsa kawai ya kasance a killace a koyaushe. Kallan Little da ke ta kallan cikin layin nasu ya yi, ya kamo hannunsa da murmushin yaƙe yace
"Ku jira ni a can.." ya faɗa yana nuna masa wajen.
"Toh.." Little ya faɗa yana yin gaba. Kai tsaye wajen Lulu ya koma, da tun daga fara tafiya har ta gaji.
"Lulu wai mu jira shi a can.." ya yi maganar yana nuna mata wajen shi ma kamar yanda Gwanin ya nuna masa. Tsaki ta ja tana murguɗa baki kamar ba za ta motsa daga inda take ba, se kuma ta soma takawa zuwa wajen, ƙasa_ƙasa tana faɗin
... Little se wasansa yake a ɗakin hankalinsa kwance babu wata damuwa. Dan tunda ya tashi yake kuka, amma yana ganin Lulu kukan ya ɗauke gaba ɗaya. Tana nannaɗe cikin hijab ɗinta tana kallansa, lokaci lokaci ta kan yi murmushi, idan ya yi wani abun kuma ta yi dariya.
"Ba ki da lafiya?" Ya tambaya yana kallanta sanda ya tsaya da wasan da yake yi. Jinjina kai ta yi fuskarta a narke tace
"Ehh.."
"Toh ki sha magani.." ya faɗa a sakarce ba tare da bawa zancen nasa muhimmanci ba ya cigaba da abin da yake yi. Ta yunƙura za ta miƙe daga kan gadon ta jiyo muryarsa ya yi sallama cikin ɗakin. Shiru ta yi ba tare da ta amsa ba, se Little da ya amsa yana ƙarasawa ya rungume shi.
"Areef.." ya faɗa yana murmushi, se kuma ya ɗora da
"Ina Auntynka?"
"Tana kan gado. Ba ta da lafiya.."
"Je ka ce mata ta shirya mu tafi asibiti.." Gwani ya faɗa yana kallan Little. Dan tabbatar da ya ji abin da ya faɗa ya sanya shi faɗin
"Me za ka ce?" Se kuwa ya maimaita masa tiryan tiryan. Se a lokacin ya saki hannunsa, shi kuma ya tafi da sauri yana kiran sunan Lulu.
"Ya sayyadi yace ki zo ya kai ki asibiti.." ya faɗa yana yaye hijab ɗin da ta lulluɓa da shi.
"Je ka ce ba za ni ba.."
"A'ah.. ni dai ki taso mu je.." Galla masa harara ta yi tana miƙewa a kan gadon tace
"Wallahi zan ɓallaka idan ba ka bar wajen nan ba.." Hannu ya ɗaga ya kai kan idanunsa da suka fara yin rau rau. Ganin da gasken kuka ze yi ya sanyata saurin riƙo hannunsa tana faɗin
"Toh yi haƙuri na dena maka faɗa ka ji?" Ta tambaya tana narkar da fuskarta ita ma. Turo baki ya yi kawai be ce komai ba. Lulu tace
"Kaa ji sweetienah?" Ta faɗa tana jan kumatunsa. Se a lokacin ya yi murmushi sannan ya fice a guje ya koma wajen Gwani. Kamar yadda ta faɗa ɗin haka ya faɗa. Ya ɗan cije lips ɗinsa yana sauke ajiyar zuciya. Se kuma ya jinjina kai kawai be ce komai ba, ya kama hannun Little yace
"Je ka duba min me Ummeey take yi.." Babu musu Little ya fice daga ɗakin. Shi kuma ya wuce zuwa inda gadon yake.
"Na baki minti 10 ki shirya.. Idan ba haka ba in zo in shiryaki da kaina.." ya faɗa dan yanzu ya riga ya gane lagonta, idan kuwa har haka ne ze dinga amfani da hakan wajen sakata yin wasu abubuwan ko da kuwa ba ta yi niyya ba. Ɗaga ido ta yi ta maka masa harara a ɗan tsorace dan kar ya ganta. Se dai ba ta san sarai ya ganta ba, amma sam be nuna ya ganta ba. Ita yanzu ma idan ta yi abu dariya take ba shi musamman da ya lura duk wannan rashin kunyar ashe matsoraciyar banza ce.
"Kin zaɓi ɗayan kenan? Ya yi.." ya yi maganar yana soma takawa zuwa wajen gadon. Durowa ta yi daga kan gadon rai a ɓace duk da yanda ƙirjinta ke bugawa be hanata cewa
"Ai dai na ga jikina ne, kuma cikina ke ciwo. Ka ƙyale ni mana ai dama so nake na mutu a zo a ɗauki gawata a fitar da ita daga cikin gidan nan. Saboda haka ka fita a harkata ka ƙyale ni.." ta yi maganar cikin ƙarfin hali wanda a fuska ba za ka taɓa fahimtar hakan ba, se dai a zuciya ita kaɗai ta san tsoron da take ji. Ɗan luu Gwani ya yi da idanunsa kamar ze lumshesu se kuma ya buɗe su ya sauke su a kan Lulu. Yana mamakin jin furucin bakinta. Kenan tsanar da ta masa har ta kai ta dinga yi wa kanta fatan mutuwa. Ba ma iya nan ba, har ta yi abin da ta san ze janyo mata rashin lafiya may be ma daga nan ta rasa ranta? Kautad da idanunta ta yi saboda yanda ta ji bugun zuciyarta ya ƙaru tun lokacin da ya zuba mata idanun nan nasa.
"Ki chanja wata hanyar ba dai wannan ba, dan ba za ta ɓille miki ba. And magana ta ƙarshe.. ki wuce ki shirya, ko kuma wallahi ki ga abin da zan yi.." ya ƙare a ɗan fusace duk da yanda yake tausar zuciyarsa a kan Lulun. Banda haka da ƙyaleta ze yi ta yi abin da ta ga dama tunda har yanzu ba ta da hankali. Se dai koma mene ne tana ƙarƙashin kulawarsa ne, kuma daga lokacin da ya yi fatali da wannan nauyin dake kansa ya san shi ɗin me laifi ne. Jin yanda ya yi magana da kallan da yake jefa mata ya sanya yana ficewa daga ɗakin ta ɗauki hijab ta saka tana jin wani kuka na taho mata. Allah ma ya gani yanzu tsoron Gwanin take ji, ko da rashin kunyar za ta yi a tsorace take yinta. Ga shi yanzu ma ta ga kamar ba ya jin rashin kunyar, dan idan ma yana ji ita dai ba ta lura da hakan ba. Dan ko da za ta masa ɗin hakan ba ze hana shi yin abin da ya yi niyya ba. Se da ta ɗauki wajen minti 12 sannan ta fito tana ta ciccin magani. A tsakar gida ta taddasu shi da Ummeey har ma da Little. Ummeey na ganinta tace
"Sannu kin ji ɗiyata.. Wallahi ga shi kuwa har kin faɗa.. Sannu kin ji?" Ta faɗa tana kallanta.
"Yawwah.." shi ne kawai abin da Lulu ta faɗa tana riƙe hannun Little da ya je wajenta.
"Ummeey bari mu je.." Gwani ya faɗa cikin nutsuwa.
"Toh Allah ya tsare.. ya kuma ba da lafiya.." Ai tunda Little ya gansu cikin shirin fita ya ƙi yadda ya je wajen Ummeey, haka Ummeeyn ta haƙura tace su je tare. Hannun Little cikin na Lulu suka fito zuwa ƙofar gidan. Gwani na gaba yayin da su suke baya, Lulu se raka shi da wata uwar harara take yi, ga haushinsa dama da take ji ga kuma wata tafiya da yake yi kamar ɗan gidan sarakai ko wani me muƙami. Daidai lokacin da suka fito Abbati ma ya iso ƙofar gidan. Hango shi da Gwani ya yi ne ya sanya shi datakawa, yayin da Lulu da Little suka cigaba da tafiya. Tun daga nesa kuma se kallan Abbati ya koma kan Little da kuma Lulu, har wani ƙanƙance idanunsa yake yi dan yafi ganin daidai. Kallan Little Abbati ya sake yi, ya sake satar kallan Lulu da fuskarta ke a cunkushe kamar za ta kai wa duk wanda ya mata magana duka. Ɗaga idanunsa da Gwani ze yi se ya tsinci idanun Abbati a kan Lulun. Ya juya ya kalli Lulun dan tabbatarwa da gasken ita yake kalla? Se kuwa ya kama shi dumu_dumu yana kallan nata. Duk da ba sonta yake yi ba, amma ko babu komai matarsa ce a yanzun. Ko babu komai ba ze so ganin wani ɗa namiji na kallanta ba tunda dai matar aure ce. Shi ya sa tun ɗazu kafin su fito yake tunanin samo mata niƙab dan ta saka. Se dai kuma be san wata fassara za ta masa ba. Se dai koma mene ne daga yau ɗin ko wacce fassara za ta masa, kome kuma za tace ba za ta sake fita daga cikin gidan nan ba se da niƙab, dan ko babu komai yanzun mallakinsa ce. Shi kuma yana da wani abu, duk wani abu da ya kasance nasa, toh burinsa kawai ya kasance a killace a koyaushe. Kallan Little da ke ta kallan cikin layin nasu ya yi, ya kamo hannunsa da murmushin yaƙe yace
"Ku jira ni a can.." ya faɗa yana nuna masa wajen.
"Toh.." Little ya faɗa yana yin gaba. Kai tsaye wajen Lulu ya koma, da tun daga fara tafiya har ta gaji.
"Lulu wai mu jira shi a can.." ya yi maganar yana nuna mata wajen shi ma kamar yanda Gwanin ya nuna masa. Tsaki ta ja tana murguɗa baki kamar ba za ta motsa daga inda take ba, se kuma ta soma takawa zuwa wajen, ƙasa_ƙasa tana faɗin