Sashe 85
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuwa can Gwani ya ɗaga kansa da ke sara masa, daidai lokacin da Bad Man ya kalle shi. Kallan kallo aka shiga yi tsakanin Gwani da Bad Man, kowanne mamaki ya kasa barinsa, ta yanda har se da ya bayyana a kan fuskar kowannensu. Ganin abun suke kamar almara, su ɗin en biyu ne? Ashe sun kwashe lokaci suna tare ba tare da sun san cewa su ɗin jini ɗaya ba ne? Jini ɗayan ma kuma en biyu? Waɗanda suka rayu cikin ciki a lokaci guda, se da ranar zuwansu duniya ta yi ƙaddara ta raba su. Lallai ikon Allah ya wuce misali.
Har i zuwa lokacin Mommah ba ta sake cewa komai ba, ta bawa Affan ɗin lokaci ne ya gama fita daga shock ɗin da ya shiga yau ɗin. Ta riga ta san dole ne ƙwaƙwalwarsa ta kasa samun nutsuwa, ta kuma damu saboda jin wannan abu. Abun da be taɓa kawo yiwuwarsa ba se ga shi ya faru. A gefe guda kuma yau ɗin Mommah jinta take tamkar ta fi kowacce mace farin ciki a ranar. Jinta take daban, ta kasa bayyana wani irin farin ciki take ciki a ranar. Amma ita kaɗai ta san abin da take ji. Godiya ga Allah kam ta yi ta har ba ta san adadi ba. Daga zarar ta kalli en biyunta zaune a waje ɗaya tana kallansu kawai se ta lumshe ido, a kan laɓɓanta tace
"Alhamdulillah.." Idan dai ba ikon Allah ba wa ya isa ya yi mata wannan kyautar. A rana ɗaya ta gano tana da 'ya'ya har biyu bayan tsayin shekarun da ta ɗauka tana tunanin ba ta da ɗa ko ɗaya. Se ga shi a rana ɗaya ta haɗu da 'ya'yan nata. Cikin hikima kuma ta Ubangiji se ga shi wanda ya tashi a cikin gidan da take be samu tarbiyya kamar yanda wanda ya tashi a wani waje can daban ya samu ba. Wato ko haka ya ishi mutum ishara, Allah Ya sa mu dace. Ba tare da Ummeey ta yadda kowa ya ganta ba, bayan ta faki idanunsu ta ga hankalin kowa na wani wajen se ta miƙe ta faɗa cikin ɗaki. Tuni zuciyarta ta daɗe da karyewa, ban da bugu babu abin da zuciyarta ke yi. Ita kanta ta daɗe tana fatan idan dai har iyayen Affan ɗin na raye Allah Ya bayyanasu. Se dai yau ɗin da suka bayyana se ga shi zuciyarta ta kasa jurewa. Kawai se ta runtse idanunta tana barin kukan da ke ta taho mata hawayen suka shiga sauka a kan fuskarta. Ta riga ta san iyayensa sun zo dan su ɗauke shi ne, dan ta san tsawon shekarun nan da suka ɗauka yanzu haka suna mararin kasancewa ne da shi, musamman ma mahaifiyarsa. Se dai duk da haka tsoronta guda ɗaya ne shi ne yanda za a rabata da Affan ɗinta, ɗanta guda ɗaya ƙwallin ƙwal, ɗanta da take so take ƙauna kamar ita ta haife shi. Ita ta ma daɗe da manta cewar ba ita ta haife shi ba, kullum kallansa take yi a ɗan da ta tsuguna ta haifa. Se ga shi rana ɗaya wannan soyayyar na neman rabuwa a cikin yini guda, ba ta tunanin zuciyarta za ta iya jurewa..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO70*
___Bayan shuɗewar wasu mintuna babu wanda ya sake cewa komai a tsakar gidan. Zuwa can Gwani ya miƙe ya shiga ɗakin Ummeey. A zaune ya sameta ta yi shiru, zuwa lokacin ta dena kuka, se dai ta yi shiru da alama tunani take yi. Ƙarasawa ya yi ya zauna a kan tabarmar. Ya saka hannunsa ya kamo na Ummeeyn. Ya kalleta da jajayen idanunsa yace
"Ummeey.." Kawai se ta ji zuciyarta ta sake karyewa. Ta lumshe idanunta tana buɗewa lokaci guda. Da ƙyar ta iya furta
"Affan.." Cikin son bata ƙwarin gwuiwa duk da shi ma nasa kaɗan ne yace
"Ummeey ki dena kuka haka nan.. Don Allah ki dena." Murmushin yaƙe Ummeey ta yi tana girgiza kai.
"Dole ne na yi kuka Affan.. Ya zan yi? Bar ni na yi kukan, duk da ba wai ina butulcewa Allah ba ne, a'ah kawai yana zuwa ne dan kansa ba da sanina ba. Ka ga kuwa yinsa ya zama dole." Shiru kawai ya yi, dan ya ma rasa wace amsa ze baiwa Ummeeyn. Kawai se ya cigaba da kallanta, tausayinta da nasa har ma da na Abeey na kama shi. Cigaba suka yi da zama cikin ɗakin kowa da abin da yake tunani. Zuwa can Abeey ya shigo ɗakin, shi ma kawai mazewa yake yi, amma shi kaɗai ya san abin da yake ji cikin zuciyarsa. Umarni ya basu da su fito waje, babu musu kuwa suka fito. Gyaran murya Daddy ya yi kafin ya soma magana.
"Wato har abada ba za mu taɓa samun abin da za mu biya ku da shi ba. Ba kuma mu da bakin da za mu iya gode muku a bisa wannan abu da kuka mana. Kun taimakemu, kun ɗauki Affan..yanzu ga abin da ya zama.. Yaron da har abada ba za ka dena alfahari da shi ba. Ni ma kuma kaina daga rana irinta yau zan soma alfahari da shi har na koma ga mahaliccina, kuma duk ta sanadiyyarku ce hakan ta faru. Allah Ya saka da alkhairi, Allah Ya biya muku dukkanin buƙatunku na alkhairi.." Addu'a sosai Daddy ya shiga zuba musu, Mommah na taya shi. Sun rasa da bakin da za su gode musu. A yanzu haka kuma sun ma rasa me ya kamata su yi musu wanda ze sanyasu cikin farin cikin da suka sanyasu ciki a yau.
"Affan ze cigaba da zama a wajenku kamar da.. dan duk da mu ne iyayensa amma mun yi kaɗan mu raba ku.." Daddy ya ƙare yana murmushi. Idan na ce Abeey ko Ummeey a cikinsu ga wanda ya fi farin ciki toh na yi ƙarya. Dan kuwa kowannensu wani shahararren farin ciki ne ya ziyarce shi.
"Ubangiji Allah Ya bar zumunci.. Allah Ya saka da alkhairi.." Makamantan waɗannan addu'o'in Ummeey da Abeey suka shiga yi. Mommah ta yi murmushi tana jin daɗin farin cikin da suka saka su a ciki, gefe guda kuma tana sake jinjina irin ƙaunar da sukewa Affan ɗin.
"Kun fi ƙarfin haka.. don Allah ku dena godiya.. Se dai alfarma ɗaya nake nema idan babu damuwa.. Ku ba ni Affan da matarsa na tsawon sati 1 ko da dangi ne su gan shi su ma." Duk se kunya ta kama Ummeey, wai Mommahn da kanta ke neman alfarma a kan ɗanta. Ta girgiza kai tana faɗin
"Ki dena irin wannan maganar don Allah.. wallahi duk se na ji na muzanta.."
"A'ah hakan shi ne daidai.. Dan har gobe ke ce za ki cigaba da amsa sunan mahaifiyar Affan."
"Ina godiya sosai.. Ina godiya.. Allah Ya bar zumunci." Ummeey ta faɗa muryarta a sanyaye. Se bayan isha'i sannan suka fara shirin barin gidan. Duk da tafiyar ta sati ɗaya ce kamar yanda Mommah ta faɗa, amma haka nan kawai ya ji ba daɗi, duk da ba wannan ne karonsa na farko na zuwa wani wajen ya kwana ba, se yake ji yau ɗin kamar yana shirin rabuwa ne da su Ummeey. Haka dai aka yi sallama cikin mutunci suka bar gidan. Daga Mommah har Daddy babu wanda ya ajje musu komai, dan ba sa so su ga kamar suna neman biyansu abin da suka yi ne. Dan haka kowanne yana tsara abin da ya kamata ya yi musu na musamman. Har ƙofar gida Abeey ya rakosu. Se da suka shiga mota dukaninsu kafin yace
"Allah Ya tsare.."
"Ameen.. Allah Ya saka da alkhairi.." godiyar da ya kasa dena fita daga bakinsu Daddy ta sake fita yanzun ma. Murmushi kawai Abeey ya yi yana juyawa ya koma cikin gida, shi kuma Daddy ya ja motar suka bar layin. Tun da suka fara tafiya Mommah na lura da 'ya'yanta da ta kasa ɗauke idanu a kansu. Sosai take ankare da Bad Man tun da suka soma tafiya. Duk da wani lokacin ya kan saci kallan Didi, Amma daga zarar ya ga za a iya ganinsa se ya basar yana wani muzurai.
"Zan yi maganinka ne Areef.." Mommah ta faɗa tana murmushi gami da girgiza kai. Lokaci ɗaya kuma se ta lumshe idanunta a kan laɓɓanta ta furta
"Allah Ya shirya min kai.." A yanzu ba ta da wani fata da ya wuce ta ga Areef ɗin ya shiryu, ya koma kamar ɗan uwansa, ko da ba duka ba ne. Fatanta Allah Ya sa lokacin shiriyarsa ne ya zo, Ya sa ɗan uwansa ya zam wani ɓangare da ze taimaka mata wajen ganin sun ceto Areef ɗin.
... Cikin gidan Alhaji Matawallen babu wanda ya san abin da ke faruwa. Se dai wasu daga ciki sun ɗan fara tsarguwa, musamman da suka ga shigar en sanda gidan, daga baya kuma gaba ɗaya en gidan suka zo suka fice. Daddy na parking motarsa, tuni aka zo aka fara bubbuɗe musu ƙofa. Didi farin ciki kamar ze sheƙeta dan daɗi, yau ga ta ga er uwarta. Ita ma Lulu na kusa da er uwatta, kan cinyarta kuma Little ya ɗora kansa ya soma baccin da ya fara fuzgarsa. Kallan gidan Lulu ta yi lokacin da suka sauka daga motar, a ranta tana mamakin nan ɗin ne gidan da aka kawo Didi kenan? A nan Didinta ke rayuwa? Ta tambayi kanta.
"Dukka ku je ku yi bacci ku huta.. Zuwa gobe za mu samu mu yi magana."
"Toh Yallaɓai.. Allah Ya tashe mu lafiya." Mommah ta amsa da hakan.
"Ameen." Ya amsa da hakan yana maida dubansa kan Bad Man yace
"Ka tafi da ɗan uwanka sashenka.. Ku samu ku samu bacci yau ɗin nan.."
"Ohk.." Bad ya amsa da hakan. Daga haka Daddy ya wuce, masu tsaron lafiyarsa na bin bayansa zuwa sashensa.
"Daughter ku wuce mu je sashena.. Areef ku je tare da Affan ku yi bacci cikin nutsuwa, ba na son dogon tunani. A bar komai se zuwa gobe kamar yanda Daddynku ya faɗa. Uhmm?"
"Toh Mommah.." Bad Man ya amsa da hakan, yana fata a ce ta manta da abin da ya faru ɗazu. Be dai fahimci hakan ba, dan kuwa maida dubanta ta yi kan Gwani daidai lokacin da ya furta
Har i zuwa lokacin Mommah ba ta sake cewa komai ba, ta bawa Affan ɗin lokaci ne ya gama fita daga shock ɗin da ya shiga yau ɗin. Ta riga ta san dole ne ƙwaƙwalwarsa ta kasa samun nutsuwa, ta kuma damu saboda jin wannan abu. Abun da be taɓa kawo yiwuwarsa ba se ga shi ya faru. A gefe guda kuma yau ɗin Mommah jinta take tamkar ta fi kowacce mace farin ciki a ranar. Jinta take daban, ta kasa bayyana wani irin farin ciki take ciki a ranar. Amma ita kaɗai ta san abin da take ji. Godiya ga Allah kam ta yi ta har ba ta san adadi ba. Daga zarar ta kalli en biyunta zaune a waje ɗaya tana kallansu kawai se ta lumshe ido, a kan laɓɓanta tace
"Alhamdulillah.." Idan dai ba ikon Allah ba wa ya isa ya yi mata wannan kyautar. A rana ɗaya ta gano tana da 'ya'ya har biyu bayan tsayin shekarun da ta ɗauka tana tunanin ba ta da ɗa ko ɗaya. Se ga shi a rana ɗaya ta haɗu da 'ya'yan nata. Cikin hikima kuma ta Ubangiji se ga shi wanda ya tashi a cikin gidan da take be samu tarbiyya kamar yanda wanda ya tashi a wani waje can daban ya samu ba. Wato ko haka ya ishi mutum ishara, Allah Ya sa mu dace. Ba tare da Ummeey ta yadda kowa ya ganta ba, bayan ta faki idanunsu ta ga hankalin kowa na wani wajen se ta miƙe ta faɗa cikin ɗaki. Tuni zuciyarta ta daɗe da karyewa, ban da bugu babu abin da zuciyarta ke yi. Ita kanta ta daɗe tana fatan idan dai har iyayen Affan ɗin na raye Allah Ya bayyanasu. Se dai yau ɗin da suka bayyana se ga shi zuciyarta ta kasa jurewa. Kawai se ta runtse idanunta tana barin kukan da ke ta taho mata hawayen suka shiga sauka a kan fuskarta. Ta riga ta san iyayensa sun zo dan su ɗauke shi ne, dan ta san tsawon shekarun nan da suka ɗauka yanzu haka suna mararin kasancewa ne da shi, musamman ma mahaifiyarsa. Se dai duk da haka tsoronta guda ɗaya ne shi ne yanda za a rabata da Affan ɗinta, ɗanta guda ɗaya ƙwallin ƙwal, ɗanta da take so take ƙauna kamar ita ta haife shi. Ita ta ma daɗe da manta cewar ba ita ta haife shi ba, kullum kallansa take yi a ɗan da ta tsuguna ta haifa. Se ga shi rana ɗaya wannan soyayyar na neman rabuwa a cikin yini guda, ba ta tunanin zuciyarta za ta iya jurewa..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO70*
___Bayan shuɗewar wasu mintuna babu wanda ya sake cewa komai a tsakar gidan. Zuwa can Gwani ya miƙe ya shiga ɗakin Ummeey. A zaune ya sameta ta yi shiru, zuwa lokacin ta dena kuka, se dai ta yi shiru da alama tunani take yi. Ƙarasawa ya yi ya zauna a kan tabarmar. Ya saka hannunsa ya kamo na Ummeeyn. Ya kalleta da jajayen idanunsa yace
"Ummeey.." Kawai se ta ji zuciyarta ta sake karyewa. Ta lumshe idanunta tana buɗewa lokaci guda. Da ƙyar ta iya furta
"Affan.." Cikin son bata ƙwarin gwuiwa duk da shi ma nasa kaɗan ne yace
"Ummeey ki dena kuka haka nan.. Don Allah ki dena." Murmushin yaƙe Ummeey ta yi tana girgiza kai.
"Dole ne na yi kuka Affan.. Ya zan yi? Bar ni na yi kukan, duk da ba wai ina butulcewa Allah ba ne, a'ah kawai yana zuwa ne dan kansa ba da sanina ba. Ka ga kuwa yinsa ya zama dole." Shiru kawai ya yi, dan ya ma rasa wace amsa ze baiwa Ummeeyn. Kawai se ya cigaba da kallanta, tausayinta da nasa har ma da na Abeey na kama shi. Cigaba suka yi da zama cikin ɗakin kowa da abin da yake tunani. Zuwa can Abeey ya shigo ɗakin, shi ma kawai mazewa yake yi, amma shi kaɗai ya san abin da yake ji cikin zuciyarsa. Umarni ya basu da su fito waje, babu musu kuwa suka fito. Gyaran murya Daddy ya yi kafin ya soma magana.
"Wato har abada ba za mu taɓa samun abin da za mu biya ku da shi ba. Ba kuma mu da bakin da za mu iya gode muku a bisa wannan abu da kuka mana. Kun taimakemu, kun ɗauki Affan..yanzu ga abin da ya zama.. Yaron da har abada ba za ka dena alfahari da shi ba. Ni ma kuma kaina daga rana irinta yau zan soma alfahari da shi har na koma ga mahaliccina, kuma duk ta sanadiyyarku ce hakan ta faru. Allah Ya saka da alkhairi, Allah Ya biya muku dukkanin buƙatunku na alkhairi.." Addu'a sosai Daddy ya shiga zuba musu, Mommah na taya shi. Sun rasa da bakin da za su gode musu. A yanzu haka kuma sun ma rasa me ya kamata su yi musu wanda ze sanyasu cikin farin cikin da suka sanyasu ciki a yau.
"Affan ze cigaba da zama a wajenku kamar da.. dan duk da mu ne iyayensa amma mun yi kaɗan mu raba ku.." Daddy ya ƙare yana murmushi. Idan na ce Abeey ko Ummeey a cikinsu ga wanda ya fi farin ciki toh na yi ƙarya. Dan kuwa kowannensu wani shahararren farin ciki ne ya ziyarce shi.
"Ubangiji Allah Ya bar zumunci.. Allah Ya saka da alkhairi.." Makamantan waɗannan addu'o'in Ummeey da Abeey suka shiga yi. Mommah ta yi murmushi tana jin daɗin farin cikin da suka saka su a ciki, gefe guda kuma tana sake jinjina irin ƙaunar da sukewa Affan ɗin.
"Kun fi ƙarfin haka.. don Allah ku dena godiya.. Se dai alfarma ɗaya nake nema idan babu damuwa.. Ku ba ni Affan da matarsa na tsawon sati 1 ko da dangi ne su gan shi su ma." Duk se kunya ta kama Ummeey, wai Mommahn da kanta ke neman alfarma a kan ɗanta. Ta girgiza kai tana faɗin
"Ki dena irin wannan maganar don Allah.. wallahi duk se na ji na muzanta.."
"A'ah hakan shi ne daidai.. Dan har gobe ke ce za ki cigaba da amsa sunan mahaifiyar Affan."
"Ina godiya sosai.. Ina godiya.. Allah Ya bar zumunci." Ummeey ta faɗa muryarta a sanyaye. Se bayan isha'i sannan suka fara shirin barin gidan. Duk da tafiyar ta sati ɗaya ce kamar yanda Mommah ta faɗa, amma haka nan kawai ya ji ba daɗi, duk da ba wannan ne karonsa na farko na zuwa wani wajen ya kwana ba, se yake ji yau ɗin kamar yana shirin rabuwa ne da su Ummeey. Haka dai aka yi sallama cikin mutunci suka bar gidan. Daga Mommah har Daddy babu wanda ya ajje musu komai, dan ba sa so su ga kamar suna neman biyansu abin da suka yi ne. Dan haka kowanne yana tsara abin da ya kamata ya yi musu na musamman. Har ƙofar gida Abeey ya rakosu. Se da suka shiga mota dukaninsu kafin yace
"Allah Ya tsare.."
"Ameen.. Allah Ya saka da alkhairi.." godiyar da ya kasa dena fita daga bakinsu Daddy ta sake fita yanzun ma. Murmushi kawai Abeey ya yi yana juyawa ya koma cikin gida, shi kuma Daddy ya ja motar suka bar layin. Tun da suka fara tafiya Mommah na lura da 'ya'yanta da ta kasa ɗauke idanu a kansu. Sosai take ankare da Bad Man tun da suka soma tafiya. Duk da wani lokacin ya kan saci kallan Didi, Amma daga zarar ya ga za a iya ganinsa se ya basar yana wani muzurai.
"Zan yi maganinka ne Areef.." Mommah ta faɗa tana murmushi gami da girgiza kai. Lokaci ɗaya kuma se ta lumshe idanunta a kan laɓɓanta ta furta
"Allah Ya shirya min kai.." A yanzu ba ta da wani fata da ya wuce ta ga Areef ɗin ya shiryu, ya koma kamar ɗan uwansa, ko da ba duka ba ne. Fatanta Allah Ya sa lokacin shiriyarsa ne ya zo, Ya sa ɗan uwansa ya zam wani ɓangare da ze taimaka mata wajen ganin sun ceto Areef ɗin.
... Cikin gidan Alhaji Matawallen babu wanda ya san abin da ke faruwa. Se dai wasu daga ciki sun ɗan fara tsarguwa, musamman da suka ga shigar en sanda gidan, daga baya kuma gaba ɗaya en gidan suka zo suka fice. Daddy na parking motarsa, tuni aka zo aka fara bubbuɗe musu ƙofa. Didi farin ciki kamar ze sheƙeta dan daɗi, yau ga ta ga er uwarta. Ita ma Lulu na kusa da er uwatta, kan cinyarta kuma Little ya ɗora kansa ya soma baccin da ya fara fuzgarsa. Kallan gidan Lulu ta yi lokacin da suka sauka daga motar, a ranta tana mamakin nan ɗin ne gidan da aka kawo Didi kenan? A nan Didinta ke rayuwa? Ta tambayi kanta.
"Dukka ku je ku yi bacci ku huta.. Zuwa gobe za mu samu mu yi magana."
"Toh Yallaɓai.. Allah Ya tashe mu lafiya." Mommah ta amsa da hakan.
"Ameen." Ya amsa da hakan yana maida dubansa kan Bad Man yace
"Ka tafi da ɗan uwanka sashenka.. Ku samu ku samu bacci yau ɗin nan.."
"Ohk.." Bad ya amsa da hakan. Daga haka Daddy ya wuce, masu tsaron lafiyarsa na bin bayansa zuwa sashensa.
"Daughter ku wuce mu je sashena.. Areef ku je tare da Affan ku yi bacci cikin nutsuwa, ba na son dogon tunani. A bar komai se zuwa gobe kamar yanda Daddynku ya faɗa. Uhmm?"
"Toh Mommah.." Bad Man ya amsa da hakan, yana fata a ce ta manta da abin da ya faru ɗazu. Be dai fahimci hakan ba, dan kuwa maida dubanta ta yi kan Gwani daidai lokacin da ya furta