Sashe 15
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh.. Ikon Allah.. Faɗeta mu ji.. Allah dai ya sa lafiya.." Mommahn da ke sanye cikin wani haɗaɗɗen lace ɗinkin buba da ta matuƙar karɓar jikinta kasancewarta me ɗan jiki haka dai ba can ba. Ta yi ɗaurin ture ka ga tsiya wanda ya matuƙar zaunawa cass a kan fuskarta da duk da yanayin shekarunta hakan be hana zallar kyawunta fitowa zam zam ba. Kai se ka ɗauka er shekara talatin da wani abun ce zaune a wajen, ta faɗa tana kallan Atinen. Gyara zama Atine ta yi, bayan ta sauke ajiyar zuciya tace
"Dama a kan maganar Areef ne da matarsa.."
"Tirƙashi.. wani abu ya faru ne bayan zuwanki sashen?" Da sauri Atine ta girgiza kai tace
"A'ah Rankiyadaɗe, babu abin da ya faru.. kawai dai ina so ne idan da dama mu shiga cikin lamarin ko dan ceto rayuwar auren waɗannan yara.." Girgiza kai Mommah ta shiga yi tana murmushin yaƙe.
"Ni za a janyowa baƙin jini Atine.. Ba na son abin da ze janyo na dinga shiga maganarsu ita da ɗanta musamman ma dai a yanzu.. Saboda haka ki barsu idan Allah ya yadda da kansu za su shirya kansu ba tare da saka hannun kowa ba.." Shiru Atine ta yi na tsawon sakanni, kafin tace
"Rankiyadaɗe kin san bauɗaɗɗen hali irin na Areef. Idan dai har ba shiga cikin lamarin nan muka yi ba mahaifiyarsa ba za ta taɓa nuna masa daidai ba."
"Toh mu bar su mana su yi abin da suke so Atine.." Mommah ta faɗa a hankali, se dai ita ma har cikin ranta da za ta samu dama da ta yi wani abun a kan auren Areef ɗin. Saboda tun zuwan Didi ta ji ta kwanta mata a rai sosai. Ba ma ita kaɗai ba, ita kanta Atine yarinyar ce ta burgeta, hankalinta da nutsuwarta komai abin burgewa ne.
"Ko da wannan ze kasance abu na ƙarshe da za ki sake shiga a kan Areef.. toh ki yi mana Hajiya. Ba don kowa ba se don Allah.." Shiru Mommah ta yi, kamar ba za tace komai ba se kuma can tace
"Shi kenan.. Allah ya taimaka.."
"Na gode sosai Hajiya.. Allah ya ƙara girma.." Atine ta faɗa cikin farin ciki, wanda har cikin muryarta se da farin cikin ya bayyana.
"Ni ma shishshigi na yi Atine.. Amma dai Allah ya ga zuciyarmu.. Allah ya taimaka.."
"Ameen.." Atine ta faɗa tana miƙewa, bayan ta yi wa Mommahn sallama ta fice daga ɗakin. Binta da kallo Mommah ta yi kamar me nazarin wani abu, se kuma daga baya ta dawo da dubanta cikin ɗakin tana sauke ajiyar zuciya.
Kai tsaye part ɗin Didi ta wuce, daidai lokacin da Bad Man ya tura ƙofar wani ɗaki ya shiga. Se da ta kalle shi sannan ta girgiza kai ta wuce ɗakin da Didi ke ciki. Kamar yanda ta batta tana zaune a kan dadduma tun bayan da ta idar da Sallah. Gaba ɗaya jinta take wata iri kamar ba ita ba. Har kuma lokacin ji take kamar mafarki take yi, za ta farka ta fahimci hakan. Se kuma ta yi ƙoƙarin tunanin Kaseem se ta tuna idan kuma da gaske ne an yi aurenta ba mafarki take yi ba fa? Hakan ne yake sanyata basar da tunanin nasa ta cigaba da zama kawai tana tunanin da yanzun ya zame mata aboki.
Duk wani motsinta tana lura da shi, yanda take komai a nutse a kuma sanyaye ya sa ta ƙara burgeta. Se da ta gama abin da za ta yi sannan ta kalli Atinen kamar jiya tace
"Baba ba za ki kwanta anan ɗin ba?" Girgiza kai ta yi tana buɗe ido daga inda take zaune
"Rufa min asiri Afrah.. Ina ni ina kwana tare da matar masu gida?" Ta faɗa tana murmushi. Ita kam Didi matar burgeta take yi saboda yanda take da barkwanci da kirki. Dan tun jiya ta fahimci hakan, mace ce me kirki.
"Kai Baba.." Didi ta faɗa tana neman waje a kan gadon ta zauna. Ganin tana ƙoƙarin kwanciya ne ya sanya Atinen faɗin
"Wai ni kam ba aure ne ya kawo ki gidan nan ba..?" Ta faɗa sanda ta ƙaraso kusa da gadon ta zauna tana kallan Didi. Shiru Didi ta yi kawai tana kallanta. Ganin haka ne ya sanya Atinen faɗin
"Tun zuwanki gidan nan kin ga mijin naki?" Shirun dai Didi ta sake yi, se kuma can ta girgiza kai a sanyaye.
"Amma shi ne kike zaune? Ba ki taɓa zuwa kin ga a wane hali yake ba? Kuma ga shi kina ƙoƙarin sake kwana a cikin ɗakin nan dan kawai shi be neme ki ba?" Se ta dakata anan tana ɗan girgiza kai sannan ta ɗora da
"Ke yarinya ce Afrah, ba za ki gane abin da nake son nuna miki ba. Amma dai ba wannan ba, kawai tashi ki je ɗakin mijinki ko da gaishe shi ne ki yi ya san dai kin tuna da shi, idan ya so na san zuwa gobe za ki koma can ɗin ma gaba ɗaya, tun da dai ba kya cigaba da zama cikin ɗakin nan ba bayan shi mijin naki yana cikin wani.."
"Baba.." ta faɗa sanda fuskarta ta wani irin narke kamar za ta yi kuka. Ƙoƙarin faɗa mata take yi ita sam ba ma ta san shi ba, ba ta san yanda aka yi auren ba, amma Atine ta katseta da faɗin
"Maza tashi kin ji 'yata.. Kar ki min gardama kin ji?" Ta faɗa tana matsawa kusa da ita ta riƙo hannunta dan miƙar da ita.
"Amma Baba don Allah.."
"Ki yi abin da na ce kin ji?" Atinen ta sake faɗa tana kallanta lokaci ɗaya tana lumshe mata idanu, dan bata ƙwarin gwuiwa a kan abin da take faɗa. Shiru Didi kawai ta yi, tana ji kamar ta rusa ihu, ba ta so ta sake yiwa dattijuwar matar musu, se dai abin da ta sakata yi ɗin ba ƙaramin abu ba ne. Tun da ita dai ba ta san mutumin ba, ba ta taɓa ganinsa ba, ba ta san waye shi ba. Dan har yanzu ita ba ta fahimci wanda aka aura mata ba. Idanunta cike da narkakkiyar ƙwalla ta juyo ta kalli Atine sanda take faɗin
"Ki saka mayafi mana.." Girgiza kai ta yi da sauri, dan ta kasa cewa komai. Se dai ganin Atinen na ƙoƙarin sake cewa wani abu ya sanyata faɗin
"Don Allah Baba ki bar ni da hijab ɗin.." ta faɗa muryarta a raunane.
"Shi kenan.. Hakan ma kin yi kyau sosai.." Atine ta faɗa tana sake feshe Didin ta wani daddaɗan turare me sanyin ƙamshi.
"Mu je na raka ki.." Atine ta faɗa tana yin gaba. Se da suka fito sannan Atine ta ƙarasa dinning, ta ɗakko wani haɗaɗɗen ƙaramin jug na coffee. Se ƙananan cups guda biyu su ma mallakin jug ɗin. Ta miƙa mata tana faɗin
"Yawwah.. riƙe ki gani.. Ki samu ki kai masa wannan na san ze ji daɗi.." Hannu Didi ta saka ta karɓa har lokacin jikinta a matuƙar sanyaye. Atine ta nuno mata ɗakin da ta ga Bad Man ya shiga tace
"Toh je ki 'yata.. Yana ciki.." Kallan ɗakin da Atinen ta nuna mata Didi ta yi, jikinta har rawa yake yi, dan haka kawai ta ji fargaba na kamata. Kawai se ta runtse idanunta sannan ta buɗe, a hankali ta soma takawa zuwa ɗakin hannunta ɗauke da coffee ɗin..
A yi manage da wannan. Shi ma dan masu Comments na yi.😐
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO32*
___ Cigaba ta yi da tafiya har lokacin tana jin yanda jikinta ke rawa. Ta ɗan dakata na tsawon minti guda tana kallan ɗakin kamar me son ganin abin da ke cikinta. Se kawai ta yi shahada ta cigaba da takawa. Dakatawa ta yi sanda ta ƙarasa bakin ƙofar, ta ɗan lumshe idanunta tana ji kamar ta fashe da kuka. Se dai kawai ta sake yin shahada ta ɗaga hannunta ta shiga knocking na ƙofar. Yana zaune a kan er ƙaramar kujerar dake gefen gado sanye cikim riga mara hannu da wandon da yake dab da gwuiwarsa se dai be ƙarasa kan gwuiwar tasa ba, hannunsa ɗauke da wata er ƙaramar farar leda. Da mamaki ya juya ya kalli ƙofar yana tunanin ko waye? Toh ko dai Mom ce? Ya tambayi kansa, dan ya san babu wanda ze zo ɗakin idan ba Mom ɗin ba, hakan ne ya sanya shi miƙewa ya ajje ledar nan kan kujerar ya ƙarasa inda mirror ɗin ɗakin ke nan, lokaci ɗaya yana faɗin
"Come in.." Sautin muryarsa se da ya fita tare da bugun zuciyarta. Yanda ta ji zuciyarta ta wani harba kamar za ta faɗo daga ƙirjinta. Ta sake runtse idanunta tana ƙoƙari wajen ganin ta saita bugun zuciyarta, se dai abun ya citira. Hakan ne ya sanyata ɗora hannunta a kan ƙofar kawai ta turata har lokacin idanunta a rufe. Taku ɗaya ta yi cikin ɗakin ta dakata ba ta sake yin wani ba. Ta ɗan ɗaga idanunta ta sauke su a cikin ɗakin sannan cikin dakiya tace
"Salamu Alaikum.." ta faɗa cikin sanyayyiyar muryarta dake rawa. Juyawa ya yi a mamakance ya sauke idanunsa a kan Didi. Se ya ƙanƙance idanunsa yana kallanta cike da mamakin ƙarfin hali irin nata. Takawa ya shiga yi yana matsawa zuwa inda take tsaye. A yanzu kam suma ne kawai ba ta yi ba lokacin da ta fara jin sautin takawar shi, wanda shi ma ke takawa tare da bugun zuciyarta. Se kuma ya dakata kafin ya ƙaraso inda take. Cikin kakkaura kuma daddaɗar muryarsa yace
"Kee..!!" ya faɗa kamar wani abun aka saka cikin muryar tasa dan har se da ta amsa. Hakan ne ya saka abin da ke hannun Didi suka ɗauki girgiɗi saboda hannunta dake rawa. Babu shiri ta yi maza ta ajje su a ƙasa saboda tsaro ka da ta zubar dasu, ba ta kuma san me ze biyo baya ba.
"Me ya kawo ki ɗakin nan? Wa kike tunanin ke ce? Fita a ɗakin kafin na yi ball dake.." ya ƙare cikin er ɗaga murya. A hankali ta ɗan buɗe idanunta sosai se dai ta kasa ɗaga ido ta kalle shi. Cikin karyayyiyar murya tace
"Baba ce tace na kawo..."
"Dama a kan maganar Areef ne da matarsa.."
"Tirƙashi.. wani abu ya faru ne bayan zuwanki sashen?" Da sauri Atine ta girgiza kai tace
"A'ah Rankiyadaɗe, babu abin da ya faru.. kawai dai ina so ne idan da dama mu shiga cikin lamarin ko dan ceto rayuwar auren waɗannan yara.." Girgiza kai Mommah ta shiga yi tana murmushin yaƙe.
"Ni za a janyowa baƙin jini Atine.. Ba na son abin da ze janyo na dinga shiga maganarsu ita da ɗanta musamman ma dai a yanzu.. Saboda haka ki barsu idan Allah ya yadda da kansu za su shirya kansu ba tare da saka hannun kowa ba.." Shiru Atine ta yi na tsawon sakanni, kafin tace
"Rankiyadaɗe kin san bauɗaɗɗen hali irin na Areef. Idan dai har ba shiga cikin lamarin nan muka yi ba mahaifiyarsa ba za ta taɓa nuna masa daidai ba."
"Toh mu bar su mana su yi abin da suke so Atine.." Mommah ta faɗa a hankali, se dai ita ma har cikin ranta da za ta samu dama da ta yi wani abun a kan auren Areef ɗin. Saboda tun zuwan Didi ta ji ta kwanta mata a rai sosai. Ba ma ita kaɗai ba, ita kanta Atine yarinyar ce ta burgeta, hankalinta da nutsuwarta komai abin burgewa ne.
"Ko da wannan ze kasance abu na ƙarshe da za ki sake shiga a kan Areef.. toh ki yi mana Hajiya. Ba don kowa ba se don Allah.." Shiru Mommah ta yi, kamar ba za tace komai ba se kuma can tace
"Shi kenan.. Allah ya taimaka.."
"Na gode sosai Hajiya.. Allah ya ƙara girma.." Atine ta faɗa cikin farin ciki, wanda har cikin muryarta se da farin cikin ya bayyana.
"Ni ma shishshigi na yi Atine.. Amma dai Allah ya ga zuciyarmu.. Allah ya taimaka.."
"Ameen.." Atine ta faɗa tana miƙewa, bayan ta yi wa Mommahn sallama ta fice daga ɗakin. Binta da kallo Mommah ta yi kamar me nazarin wani abu, se kuma daga baya ta dawo da dubanta cikin ɗakin tana sauke ajiyar zuciya.
Kai tsaye part ɗin Didi ta wuce, daidai lokacin da Bad Man ya tura ƙofar wani ɗaki ya shiga. Se da ta kalle shi sannan ta girgiza kai ta wuce ɗakin da Didi ke ciki. Kamar yanda ta batta tana zaune a kan dadduma tun bayan da ta idar da Sallah. Gaba ɗaya jinta take wata iri kamar ba ita ba. Har kuma lokacin ji take kamar mafarki take yi, za ta farka ta fahimci hakan. Se kuma ta yi ƙoƙarin tunanin Kaseem se ta tuna idan kuma da gaske ne an yi aurenta ba mafarki take yi ba fa? Hakan ne yake sanyata basar da tunanin nasa ta cigaba da zama kawai tana tunanin da yanzun ya zame mata aboki.
Duk wani motsinta tana lura da shi, yanda take komai a nutse a kuma sanyaye ya sa ta ƙara burgeta. Se da ta gama abin da za ta yi sannan ta kalli Atinen kamar jiya tace
"Baba ba za ki kwanta anan ɗin ba?" Girgiza kai ta yi tana buɗe ido daga inda take zaune
"Rufa min asiri Afrah.. Ina ni ina kwana tare da matar masu gida?" Ta faɗa tana murmushi. Ita kam Didi matar burgeta take yi saboda yanda take da barkwanci da kirki. Dan tun jiya ta fahimci hakan, mace ce me kirki.
"Kai Baba.." Didi ta faɗa tana neman waje a kan gadon ta zauna. Ganin tana ƙoƙarin kwanciya ne ya sanya Atinen faɗin
"Wai ni kam ba aure ne ya kawo ki gidan nan ba..?" Ta faɗa sanda ta ƙaraso kusa da gadon ta zauna tana kallan Didi. Shiru Didi ta yi kawai tana kallanta. Ganin haka ne ya sanya Atinen faɗin
"Tun zuwanki gidan nan kin ga mijin naki?" Shirun dai Didi ta sake yi, se kuma can ta girgiza kai a sanyaye.
"Amma shi ne kike zaune? Ba ki taɓa zuwa kin ga a wane hali yake ba? Kuma ga shi kina ƙoƙarin sake kwana a cikin ɗakin nan dan kawai shi be neme ki ba?" Se ta dakata anan tana ɗan girgiza kai sannan ta ɗora da
"Ke yarinya ce Afrah, ba za ki gane abin da nake son nuna miki ba. Amma dai ba wannan ba, kawai tashi ki je ɗakin mijinki ko da gaishe shi ne ki yi ya san dai kin tuna da shi, idan ya so na san zuwa gobe za ki koma can ɗin ma gaba ɗaya, tun da dai ba kya cigaba da zama cikin ɗakin nan ba bayan shi mijin naki yana cikin wani.."
"Baba.." ta faɗa sanda fuskarta ta wani irin narke kamar za ta yi kuka. Ƙoƙarin faɗa mata take yi ita sam ba ma ta san shi ba, ba ta san yanda aka yi auren ba, amma Atine ta katseta da faɗin
"Maza tashi kin ji 'yata.. Kar ki min gardama kin ji?" Ta faɗa tana matsawa kusa da ita ta riƙo hannunta dan miƙar da ita.
"Amma Baba don Allah.."
"Ki yi abin da na ce kin ji?" Atinen ta sake faɗa tana kallanta lokaci ɗaya tana lumshe mata idanu, dan bata ƙwarin gwuiwa a kan abin da take faɗa. Shiru Didi kawai ta yi, tana ji kamar ta rusa ihu, ba ta so ta sake yiwa dattijuwar matar musu, se dai abin da ta sakata yi ɗin ba ƙaramin abu ba ne. Tun da ita dai ba ta san mutumin ba, ba ta taɓa ganinsa ba, ba ta san waye shi ba. Dan har yanzu ita ba ta fahimci wanda aka aura mata ba. Idanunta cike da narkakkiyar ƙwalla ta juyo ta kalli Atine sanda take faɗin
"Ki saka mayafi mana.." Girgiza kai ta yi da sauri, dan ta kasa cewa komai. Se dai ganin Atinen na ƙoƙarin sake cewa wani abu ya sanyata faɗin
"Don Allah Baba ki bar ni da hijab ɗin.." ta faɗa muryarta a raunane.
"Shi kenan.. Hakan ma kin yi kyau sosai.." Atine ta faɗa tana sake feshe Didin ta wani daddaɗan turare me sanyin ƙamshi.
"Mu je na raka ki.." Atine ta faɗa tana yin gaba. Se da suka fito sannan Atine ta ƙarasa dinning, ta ɗakko wani haɗaɗɗen ƙaramin jug na coffee. Se ƙananan cups guda biyu su ma mallakin jug ɗin. Ta miƙa mata tana faɗin
"Yawwah.. riƙe ki gani.. Ki samu ki kai masa wannan na san ze ji daɗi.." Hannu Didi ta saka ta karɓa har lokacin jikinta a matuƙar sanyaye. Atine ta nuno mata ɗakin da ta ga Bad Man ya shiga tace
"Toh je ki 'yata.. Yana ciki.." Kallan ɗakin da Atinen ta nuna mata Didi ta yi, jikinta har rawa yake yi, dan haka kawai ta ji fargaba na kamata. Kawai se ta runtse idanunta sannan ta buɗe, a hankali ta soma takawa zuwa ɗakin hannunta ɗauke da coffee ɗin..
A yi manage da wannan. Shi ma dan masu Comments na yi.😐
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO32*
___ Cigaba ta yi da tafiya har lokacin tana jin yanda jikinta ke rawa. Ta ɗan dakata na tsawon minti guda tana kallan ɗakin kamar me son ganin abin da ke cikinta. Se kawai ta yi shahada ta cigaba da takawa. Dakatawa ta yi sanda ta ƙarasa bakin ƙofar, ta ɗan lumshe idanunta tana ji kamar ta fashe da kuka. Se dai kawai ta sake yin shahada ta ɗaga hannunta ta shiga knocking na ƙofar. Yana zaune a kan er ƙaramar kujerar dake gefen gado sanye cikim riga mara hannu da wandon da yake dab da gwuiwarsa se dai be ƙarasa kan gwuiwar tasa ba, hannunsa ɗauke da wata er ƙaramar farar leda. Da mamaki ya juya ya kalli ƙofar yana tunanin ko waye? Toh ko dai Mom ce? Ya tambayi kansa, dan ya san babu wanda ze zo ɗakin idan ba Mom ɗin ba, hakan ne ya sanya shi miƙewa ya ajje ledar nan kan kujerar ya ƙarasa inda mirror ɗin ɗakin ke nan, lokaci ɗaya yana faɗin
"Come in.." Sautin muryarsa se da ya fita tare da bugun zuciyarta. Yanda ta ji zuciyarta ta wani harba kamar za ta faɗo daga ƙirjinta. Ta sake runtse idanunta tana ƙoƙari wajen ganin ta saita bugun zuciyarta, se dai abun ya citira. Hakan ne ya sanyata ɗora hannunta a kan ƙofar kawai ta turata har lokacin idanunta a rufe. Taku ɗaya ta yi cikin ɗakin ta dakata ba ta sake yin wani ba. Ta ɗan ɗaga idanunta ta sauke su a cikin ɗakin sannan cikin dakiya tace
"Salamu Alaikum.." ta faɗa cikin sanyayyiyar muryarta dake rawa. Juyawa ya yi a mamakance ya sauke idanunsa a kan Didi. Se ya ƙanƙance idanunsa yana kallanta cike da mamakin ƙarfin hali irin nata. Takawa ya shiga yi yana matsawa zuwa inda take tsaye. A yanzu kam suma ne kawai ba ta yi ba lokacin da ta fara jin sautin takawar shi, wanda shi ma ke takawa tare da bugun zuciyarta. Se kuma ya dakata kafin ya ƙaraso inda take. Cikin kakkaura kuma daddaɗar muryarsa yace
"Kee..!!" ya faɗa kamar wani abun aka saka cikin muryar tasa dan har se da ta amsa. Hakan ne ya saka abin da ke hannun Didi suka ɗauki girgiɗi saboda hannunta dake rawa. Babu shiri ta yi maza ta ajje su a ƙasa saboda tsaro ka da ta zubar dasu, ba ta kuma san me ze biyo baya ba.
"Me ya kawo ki ɗakin nan? Wa kike tunanin ke ce? Fita a ɗakin kafin na yi ball dake.." ya ƙare cikin er ɗaga murya. A hankali ta ɗan buɗe idanunta sosai se dai ta kasa ɗaga ido ta kalle shi. Cikin karyayyiyar murya tace
"Baba ce tace na kawo..."