Sashe 66
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Idan kuma zancen ya je wajen wasu shi kenan fa kowa ya san waye ka..." Ai be jira ma ta gama ci masa mutuncin ba, bakin da ke magana ya sanya bakinsa ya riƙo shi cikin nasa. Ba da niyyar sumbata ya kama bakin nata ba, se dan ya hora bakin da ke faɗa masa magana. Se dai cikin ƙanƙanin lokaci hakan ya nemi ya sauya, amma ya ƙi bada dama. Rashin tsammatar hakan ya sanya zancen nata katsewa lokacin da ta ji bakinta cikin nasa, ya kama lips ɗin yana sumbata, se dai yana sane ya shiga kissing nata a zafafe yanda ya san tilas za ta ji zafin hakan. Ya kuma san ba lallai ta sake buɗe baki tace za ta masa magana ba. A'ah daga mugunta se ga ɗan mutumunku har da lumshe idanunsa se dai har lokacin a zafafen ya cigaba da abin da yake yi, be kuma saketa ba. Saboda yanda take jin zafin kissing ɗin har tsakiyar kanta ya sanya tuni hawaye sun gama wanke fuskarta. Idanunta sun fito sosai saboda tsananin mamakin abin da ke faruwa. Zuciyarta na bugawa da ƙarfin gaske saboda tsoron da ya kama ilahirin jikinta. Ban da ƙoƙarin zame bakinta babu abin da take yi, amma ko bi ta kanta be yi ba. Ya kai wajen minti ɗaya da rabi kafin ya sakar mata bakin ya ma saketa gaba ɗaya. Hannu ta yarfar lokacin da ya saketa ɗin tana ji kamar ya tsinke mata baki gaba ɗaya saboda azaba. A daddafe ta nemi hanyar fita ko gani sosai ba ta yi ta fice daga ɗakin. Kai tsaye ɗakinta ta wuce. Se a lokacin ta iya kai hannunta ta goge hawayen fuskarta na wannan muguntar da ya mata. Hannunta a kan bakinta da ya yi mugun ja kamar wadda ta ji ciwo. Kawai se ta kifa kanta a kan gadon tana fashewa da kuka mara sauti. Ita kam yau ta yi danasanin da ba ta taɓa yi ba. Ta yi danasanin shiga ɗakin, ta kuma yi danasanin tanka masa bayan ya kulata. Ga shi nan garin hakan ya kusa cire mata baki.
A ɓangarensa kuwa ɗora hannunsa ya yi a kan sumar kansa. Ba tare da ya shirya ba wani murmushin gefen baki ya suɓuce masa. A hankali ya cigaba da shafa sumar kan nasa yana tuna abin da ya faru. Se kuma ya ɗan yi gyaran murya kamar shi da wani ne a wajen, ya gyara tsayuwarsa yana haɗe face ya koma kan gado ya zauna. Ya ɗauki mintuna masu ɗan dama a wajen kafin ya kalli gefensa da ya ji motsi. Se a lokacin ma ya tuna da Little da ke cigaba da baccinsa hankali kwance. Se ya miƙe a hankali ya saka hannu ya ɗauke shi. Kai tsaye ɗakin Didi ya wuce. Zuwa lokacin ta haƙura, se dai ta shafawa bakinta man zafi kar ta je ya kumbure mata kafin gobe. (Lolz) Ta juya da niyyar kwantawa dan kuwa ta sanya a ranta babu abin da ze sake kaita ɗakin ɗauko Little. Ya daɗe be kwana a can ba, ita ɗaya za ta kwanta babu komai. Daidai lokacin ya turo ƙofar ɗakin ya shigo hannunsa ɗauke da Little. Kawai se ta tsaya ta kasa ko da jan bargo ne ta lulluɓe jikinta. Se ka ce wadda aka ƙamar kawai ta ƙame tana jira ta ga abin da ze yi. Idanuwan da ya ji a kansa ne ya sanya shi kallanta, ta yi saurin ɗauke kai tana jan bargo ta lulluɓa gaba ɗayanta. Kawai se ya ƙarasa har kan gadon ba tare da yace mata komai ba ya ajje Little. Daga haka ya juya ya fice daga ɗakin. Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya lokacin da ta ji fitarsa daga ɗakin.
... A ɗaya ɓangaren kuwa kwanaki 5 ciff aka kwashe ana bawa Maimuna kulawa ta musamman duk da taimakon Ammi da ke biyan kuɗin komai. Cikin ikon Allah se ga shi a kwana na biyar ɗin zancen farin ciki ya ziyarci Talatuwa. Shi ne na buɗewar bakin Maimuna. Farin ciki kamar za ta yi me. Haka ta shiga wajenta cikin matuƙar jin daɗi. Sun daɗe suna magana da Maimunan, duk da maganar tata a hankali take yinta kamar er koyo. Amma a haka suka yi maganganunsu.
Bayan wajen minti 10 Talatuwa ta fito tana murmushi, ta kalli Ammi tace
"Hajiya wai ki je tace tana son magana da ke."
"Ikon Allah! Ni ɗin?" Ammi ta faɗa tana mamakin wannan abu da ke faruwa. Ko me take ta so ta faɗa mata duk tsawon kwanakin nan? Kawai dai se ta miƙe ta kalli Gwaggo tace
"Gwaggo bari na je."
"Toh Allah ya jishshe mu alkhairi." Ba ta iya amsawa a fili ba se cikin zuciya. Haka ta kama jiki zuwa cikin ɗakin. Tun daga nesa Maimuna ta hangeta kasancewar idanunta na kan ƙofa ne. Ba ta san lokacin da ta yi dariya ba tana ji kamar ta tashi ta ƙaraso da Ammin. Da sauri Ammi ta ƙarasa dan kar Maimunan tace za ta tashi zaune. Kujera ta ja ta matsar da ita dab da gadon ta zauna. Hannunta riƙe da na Maimuna tace
"Ba se kin tashi ba ai gani nan." Jinjina kai Maimuna ta yi har lokacin fuskarta da murmushi a kai.
"Ina jin ki ga ni." In ji Ammi. Se da Maimuna ta sauke ajiyar zuciya sannan tace da muryarta da ba ta gama fita duka ba. Se dai ana iya fahimtar duk wani abu da zata faɗa
"Ki yi haƙuri na zaunar da ke da muka yi. Hajiya taimako nake buƙata don Allah bayan wannan uban taimakon da kika yi mana.. Kae ji gaji don Allah.. Wato na daɗe da damuwa cikin raina. Ban tashi soma son zuwa Kano ba saboda wani dalili se da na soma rashin lafiya. Hakan ne ya sa hakan ya ƙi yiwuwa saboda ciwon nan da ya same ni. Ga shi ni ba iya rubutu na yi ba ballantana na rubuta abin da ke cikin raina har ya je inda nake so ya isa ba. Ban kuma san yanda zan faɗawa Talatuwa Kano nake so na je ba. Se da zuwanki na ji an ce a Kano kike shi ya sa duk na ruɗe. Na ji tamkar a lokacin na warke ne saboda tsananin farin ciki. Na ɗauka Talatuwa za ta fahimci wani abun, se dai ban ga hakan ba. Se dai yanzu da bakina yake a buɗe ina me neman alfarmarki.. ina me neman amincewarki da ki zo ki taya ni duban wani gida da nake da tabbacin In Sha Allah za ki iya sanin shi. Ina so na je wajen masu gidan.. shi ne kaɗai burina. Ban da shi babu komai." Daga haka ta yi shiru tana amfani da hannunta lafiyayye wajen goge fuskarta da ta jiƙe sharkaff da gumi da kuma hawaye. Tun da ta fara magana Ammi ke kallanta har ta ƙarasa. Ganin irin kallan da Ammin ke mata ne ya sanyata cigaba da faɗin
"Ban san da wane irin baki zan buɗe na miki bayani ba, dan ban san yanda za ki ɗauki zancen ba. Ni dai fatana ki taimaka min ki kai ni Kano se mu nemi gidan tun da ke kin san garin. Don Allah ki taimake ni kar ki ce a'ah. Kamar yanda kika taimaka min a kan wannan ciwon nawa ki taimaka ki kai ni Kano. Ban taɓa zaton bakina ze kuma buɗewa ba. Ban taɓa tunanin zan kuma zama na yi magana kamar yanda mutane ke yi ba. Ba na so na butulcewa Allah, haƙiƙa Allah na sona, shi ya sa ya sake ara min baki a lokacin da ban yi tsammani ba. Ban sani ba ko dan ya ba ni damar gyara kuskurena ne."
Se a lokacin sannan Ammi tace
"A haka za ki je har wani garin?" Ammi ta faɗa cike da mamakin maganganun Maimunan da suka matuƙar jefata cikin tunani. Lokaci ɗaya kuma tana kallan Maimunan da ke kwance kan gado ko tashi ba ta iya yi, take zancen tana so ta je Kano. Hawaye ne suka zubo daga cikin idanun Maimuna tace
"Ai shi ya sa nake cewa ki taimaka min don girman Allah. Ko da wannan ɗin ita ce alfarma ta ƙarshe da za ki iya min ki yi min ita." Shiru Ammi ta sake yi na tsawon sakanni kafin ta sauke ajiyar zuciya tace
"A kan wane gida kike magana? Gidan na da wani suna ne da za a iya gane shi da shi?" Jinjina kai Maimuna ta yi tana ji kamar ta tashi zaune ta ƙarasa maganar. Se dai kasancewar ta san hakan ba me yiwuwa ba ne ya sanyata faɗin
"Na sani.. Sunan me gidan Alhaji Matawalle.."
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO60*
___ "Alhaji Matawalle.." Ammi ta maimaita sunan tana jinjina kai.
"Ehh haka sunan yake." Talatuwa ta sake faɗa.
"Shi kenan.. zan taimaka miki." Hawaye sosai Maimunatu ta shiga yi tana godewa Ammi, tana ji tamkar ta tashi ta ɗauketa ta yi ta juyi da ita a bayanta. Kai tsaye Ammi na fitowa number Abba ta nema ta sanar da shi abin da ya faru.
"Alhaji Matawalle..?" Shi ma ya maimaita sunan cike da mamaki.
"Toh ai gidan surukan Afrah ne take nufi kenan." Numfashi Ammi ta sauke tana faɗin
"Tabbas.. Dan kaf Kano babu wani me irin sunan bayan shi."
"Ikon Allah.. Toh Allah ya sa lafiya. Yanzu ke me kika yanke?"
"Duk abin da ka ce Yallaɓai." Murmushi Abba ya yi yace
"Toh shi kenan.. Idan ze yiwu ku samu ku taho Kano ɗin zuwa gobe, idan likitocin za su baku ita mara lafiyar. Allah ya bada lada."
"Ameen Ameen Abbansu. Amma ka na ganin babu komai idan na je gidan?" Girgiza kai Abba ya yi kamar Ammin na gabansa yace
"A'ah babu komai.."
"Tohm." Daga haka suka yi sallama.
.. Cikin ƙanƙanin lokaci Ammi ta soma haɗa kaya. Ta bar Aunty Maryam ta cigaba da kula da lafiyar Gwaggo kafin ta samu sauƙi sosai a nemo mata sabuwar er aiki. Da yake jikin Maimunan ya yi sauƙi shi ne dalilin da ya sa suka barta bayan an bata ɗaya daga cikin kujerar da wani bawan Allah ke bayarwa a raba saboda guragu da masu irin lalurarta.
A ɓangarensa kuwa ɗora hannunsa ya yi a kan sumar kansa. Ba tare da ya shirya ba wani murmushin gefen baki ya suɓuce masa. A hankali ya cigaba da shafa sumar kan nasa yana tuna abin da ya faru. Se kuma ya ɗan yi gyaran murya kamar shi da wani ne a wajen, ya gyara tsayuwarsa yana haɗe face ya koma kan gado ya zauna. Ya ɗauki mintuna masu ɗan dama a wajen kafin ya kalli gefensa da ya ji motsi. Se a lokacin ma ya tuna da Little da ke cigaba da baccinsa hankali kwance. Se ya miƙe a hankali ya saka hannu ya ɗauke shi. Kai tsaye ɗakin Didi ya wuce. Zuwa lokacin ta haƙura, se dai ta shafawa bakinta man zafi kar ta je ya kumbure mata kafin gobe. (Lolz) Ta juya da niyyar kwantawa dan kuwa ta sanya a ranta babu abin da ze sake kaita ɗakin ɗauko Little. Ya daɗe be kwana a can ba, ita ɗaya za ta kwanta babu komai. Daidai lokacin ya turo ƙofar ɗakin ya shigo hannunsa ɗauke da Little. Kawai se ta tsaya ta kasa ko da jan bargo ne ta lulluɓe jikinta. Se ka ce wadda aka ƙamar kawai ta ƙame tana jira ta ga abin da ze yi. Idanuwan da ya ji a kansa ne ya sanya shi kallanta, ta yi saurin ɗauke kai tana jan bargo ta lulluɓa gaba ɗayanta. Kawai se ya ƙarasa har kan gadon ba tare da yace mata komai ba ya ajje Little. Daga haka ya juya ya fice daga ɗakin. Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya lokacin da ta ji fitarsa daga ɗakin.
... A ɗaya ɓangaren kuwa kwanaki 5 ciff aka kwashe ana bawa Maimuna kulawa ta musamman duk da taimakon Ammi da ke biyan kuɗin komai. Cikin ikon Allah se ga shi a kwana na biyar ɗin zancen farin ciki ya ziyarci Talatuwa. Shi ne na buɗewar bakin Maimuna. Farin ciki kamar za ta yi me. Haka ta shiga wajenta cikin matuƙar jin daɗi. Sun daɗe suna magana da Maimunan, duk da maganar tata a hankali take yinta kamar er koyo. Amma a haka suka yi maganganunsu.
Bayan wajen minti 10 Talatuwa ta fito tana murmushi, ta kalli Ammi tace
"Hajiya wai ki je tace tana son magana da ke."
"Ikon Allah! Ni ɗin?" Ammi ta faɗa tana mamakin wannan abu da ke faruwa. Ko me take ta so ta faɗa mata duk tsawon kwanakin nan? Kawai dai se ta miƙe ta kalli Gwaggo tace
"Gwaggo bari na je."
"Toh Allah ya jishshe mu alkhairi." Ba ta iya amsawa a fili ba se cikin zuciya. Haka ta kama jiki zuwa cikin ɗakin. Tun daga nesa Maimuna ta hangeta kasancewar idanunta na kan ƙofa ne. Ba ta san lokacin da ta yi dariya ba tana ji kamar ta tashi ta ƙaraso da Ammin. Da sauri Ammi ta ƙarasa dan kar Maimunan tace za ta tashi zaune. Kujera ta ja ta matsar da ita dab da gadon ta zauna. Hannunta riƙe da na Maimuna tace
"Ba se kin tashi ba ai gani nan." Jinjina kai Maimuna ta yi har lokacin fuskarta da murmushi a kai.
"Ina jin ki ga ni." In ji Ammi. Se da Maimuna ta sauke ajiyar zuciya sannan tace da muryarta da ba ta gama fita duka ba. Se dai ana iya fahimtar duk wani abu da zata faɗa
"Ki yi haƙuri na zaunar da ke da muka yi. Hajiya taimako nake buƙata don Allah bayan wannan uban taimakon da kika yi mana.. Kae ji gaji don Allah.. Wato na daɗe da damuwa cikin raina. Ban tashi soma son zuwa Kano ba saboda wani dalili se da na soma rashin lafiya. Hakan ne ya sa hakan ya ƙi yiwuwa saboda ciwon nan da ya same ni. Ga shi ni ba iya rubutu na yi ba ballantana na rubuta abin da ke cikin raina har ya je inda nake so ya isa ba. Ban kuma san yanda zan faɗawa Talatuwa Kano nake so na je ba. Se da zuwanki na ji an ce a Kano kike shi ya sa duk na ruɗe. Na ji tamkar a lokacin na warke ne saboda tsananin farin ciki. Na ɗauka Talatuwa za ta fahimci wani abun, se dai ban ga hakan ba. Se dai yanzu da bakina yake a buɗe ina me neman alfarmarki.. ina me neman amincewarki da ki zo ki taya ni duban wani gida da nake da tabbacin In Sha Allah za ki iya sanin shi. Ina so na je wajen masu gidan.. shi ne kaɗai burina. Ban da shi babu komai." Daga haka ta yi shiru tana amfani da hannunta lafiyayye wajen goge fuskarta da ta jiƙe sharkaff da gumi da kuma hawaye. Tun da ta fara magana Ammi ke kallanta har ta ƙarasa. Ganin irin kallan da Ammin ke mata ne ya sanyata cigaba da faɗin
"Ban san da wane irin baki zan buɗe na miki bayani ba, dan ban san yanda za ki ɗauki zancen ba. Ni dai fatana ki taimaka min ki kai ni Kano se mu nemi gidan tun da ke kin san garin. Don Allah ki taimake ni kar ki ce a'ah. Kamar yanda kika taimaka min a kan wannan ciwon nawa ki taimaka ki kai ni Kano. Ban taɓa zaton bakina ze kuma buɗewa ba. Ban taɓa tunanin zan kuma zama na yi magana kamar yanda mutane ke yi ba. Ba na so na butulcewa Allah, haƙiƙa Allah na sona, shi ya sa ya sake ara min baki a lokacin da ban yi tsammani ba. Ban sani ba ko dan ya ba ni damar gyara kuskurena ne."
Se a lokacin sannan Ammi tace
"A haka za ki je har wani garin?" Ammi ta faɗa cike da mamakin maganganun Maimunan da suka matuƙar jefata cikin tunani. Lokaci ɗaya kuma tana kallan Maimunan da ke kwance kan gado ko tashi ba ta iya yi, take zancen tana so ta je Kano. Hawaye ne suka zubo daga cikin idanun Maimuna tace
"Ai shi ya sa nake cewa ki taimaka min don girman Allah. Ko da wannan ɗin ita ce alfarma ta ƙarshe da za ki iya min ki yi min ita." Shiru Ammi ta sake yi na tsawon sakanni kafin ta sauke ajiyar zuciya tace
"A kan wane gida kike magana? Gidan na da wani suna ne da za a iya gane shi da shi?" Jinjina kai Maimuna ta yi tana ji kamar ta tashi zaune ta ƙarasa maganar. Se dai kasancewar ta san hakan ba me yiwuwa ba ne ya sanyata faɗin
"Na sani.. Sunan me gidan Alhaji Matawalle.."
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO60*
___ "Alhaji Matawalle.." Ammi ta maimaita sunan tana jinjina kai.
"Ehh haka sunan yake." Talatuwa ta sake faɗa.
"Shi kenan.. zan taimaka miki." Hawaye sosai Maimunatu ta shiga yi tana godewa Ammi, tana ji tamkar ta tashi ta ɗauketa ta yi ta juyi da ita a bayanta. Kai tsaye Ammi na fitowa number Abba ta nema ta sanar da shi abin da ya faru.
"Alhaji Matawalle..?" Shi ma ya maimaita sunan cike da mamaki.
"Toh ai gidan surukan Afrah ne take nufi kenan." Numfashi Ammi ta sauke tana faɗin
"Tabbas.. Dan kaf Kano babu wani me irin sunan bayan shi."
"Ikon Allah.. Toh Allah ya sa lafiya. Yanzu ke me kika yanke?"
"Duk abin da ka ce Yallaɓai." Murmushi Abba ya yi yace
"Toh shi kenan.. Idan ze yiwu ku samu ku taho Kano ɗin zuwa gobe, idan likitocin za su baku ita mara lafiyar. Allah ya bada lada."
"Ameen Ameen Abbansu. Amma ka na ganin babu komai idan na je gidan?" Girgiza kai Abba ya yi kamar Ammin na gabansa yace
"A'ah babu komai.."
"Tohm." Daga haka suka yi sallama.
.. Cikin ƙanƙanin lokaci Ammi ta soma haɗa kaya. Ta bar Aunty Maryam ta cigaba da kula da lafiyar Gwaggo kafin ta samu sauƙi sosai a nemo mata sabuwar er aiki. Da yake jikin Maimunan ya yi sauƙi shi ne dalilin da ya sa suka barta bayan an bata ɗaya daga cikin kujerar da wani bawan Allah ke bayarwa a raba saboda guragu da masu irin lalurarta.