Sashe 109
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shi kenan.. Na ji ko ma me ye ze faru, yanzu dai a lamunce min na taimaka miki zuwa toilet, daga nan kowanne hukunci za a min na amince." Ya yi maganar yana ɗan leƙa fuskarta. Ganin ta kalle shi ne ya sanya shi komawa yana murmushi. Se kawai ta maaze, cike da ƙarfin hali ta soma ƙoƙarin miƙewa. Gaba ɗaya jikinta ya yi tsami kamar wadda ta wuni da ciwon jiki. Dalili kenan da ya sanyata runtse idanunta tana bawa ƙwallar da ta ƙi dena taruwa a idanunta damar zubowa.
"Ohhh.." Ya faɗa yana ɗora hannunsa a kan goshinsa. Se ya miƙe tsaye sosai. Be jira tace ko ya sake cewa komai ba ya saka hannu ya saɓeta gaba ɗaya se toilet ɗin. Duk da yanda take ta zillewa haka ya basar ya kaita. Kai tsaye cikin bathtub ɗin ya sakata ciki, yana jinta tana ta en koke_kokenta. Duk da yanda matsanancin tausayinta ya kama shi hakan be sa ya cireta daga ciki ba. Ya ɗan dinga basarwa dan kar ya fusata ya maidata kan gadon. Ita dai yau Didi ta ga abubuwa, dan kuwa haka tana ji tana gani Bad Man ɗin ya saɓeta tass da sabulu. Tun tana kukan tana zillewa har ta gaji ta haƙura. Wai kuma se da ya gama komai sannan ya kalleta yana riƙe da ita yace
"Na yi laifi a yafe min." I zuwa yanzu ita kam har ta gaji da jin wannan kalmar. Ta daɗe da gano shi, wato ba ya tashi bayar da haƙuri se ya aikata abin da yake so, se ya zo yana marairaicewa. Duk da haka kuma be ƙyaleta ba se da ya samo mata wata riga ya zura mata kafin ya ɗauketa dan sauƙaƙa mata ya direta kan gado. I zuwa lokacin ta haƙura kawai ta zubawa sarautar Allah ido, dan ba ta ga alamar yana da niyyar dena duk abin da ya fara ba. Kawai se komawa ta yi ta kwanta, dan duk da ta ji daɗin jikinta amma har yanzu wani iri take jinta daban. Tashi ya yi ya koma kan gadon, ya saka hannunsa ya jata cikin jikinsa yana kallan idanunta da yau ɗin suka ƙi ko da gajiya ne da tara ƙwalla. Cikin kulawa yace
"Haba mana wifey, kukan ya isa haka. Girma ne fa ki ka yi. Kin ga yanzu kin taddo Afaaf, ni ma kuma na taddo ɗan uwa, yanzu haka kanmu ɗaya." Ya ƙare yana murmushin gefen baki. Ita dai waɗannan zancen nasa sake tsundumata suke cikin kunya da sake tuna abin da ya faru be sani ba. Shi kuma da alama ko a jikinsa. Da ze gane da ya yi shiru ya barta ta ji da abin da take ji. Ba ta gama dawowa daga wannan kunyar ba ta sake jiyo muryarsa yana faɗin
"Na san ni jarumi ne.. Yanzu haka da za a auna ki se an tabbatar mana da na yi ajiya.." Tun kafin ya kai karshen maganar tasa ta soma ɗan buga jikinta tana yi kamar za ta soma kuka, lokaci ɗaya kuma tana cusa kanta cikin ƙirjinsa tana jin wata matsananciyar kunya na kamata. Shi dai wallahi sam ba ya da kunya ko kaɗan. Ya gama abin da yake so ya barta da kunya da wahala, ga shi kuma ya zo se kunnota yake yi da maganganunsa da suke sawa ta ji kamar ƙasa ta tsage ta shige. Murmushi ya yi yana ɗan cije lips ɗinsa.
"Shi kenan na dena.." Ya ƙare yana sakin ƙayataccen murmushin gefen baki lokaci ɗaya yana sake rungumeta cike da matsananciyar ƙaunarta. Ita dai ko motsi ba ta yi ba, ta yi shiru a jikin nasa cike da fatan kar ya motsa. Dan idan tana waje ɗaya ta fi jinta normal, da zarar ta motsa kuma se ta ji kamar ta fashe da kuka saboda yanda take jin jikinta.
.. A karo na biyu ya sake kallanta, a nutse yace
"In zo in taimaka miki?" Girgiza kai ta yi tana runtse idanunta cike da fatan ta ji ta koma daidai, ta dena jin komai. Se dai kamar ɗazun yanzun ma komawa ta yi tana ɗan sauke numfashi. Miƙewa ya yi ya ƙaraso kan gadon, ya ranƙwafo yana ƙura mata idanunsa. Cikin kulawa, kuma muryarsa ƙasa ƙasa yace
"Har yanzu dai?" Se da ta buɗe lumsassun idanunta ta kalle shi, kafin ta jinjina kai a sanyaye tana sauke idanunta. Hannu ya miƙa mata yace
"Kama ki tashi mu ga." Miƙa masa hannun ta yi, ya taimaka mata ta miƙe yana lura da yanayinta. Ya ɗan sauke numfashi kafin ya maidata kan gadon daidai lokacin da yake faɗin
"Kwanta ina zuwa.." Babu musu ta koma ta kwanta ɗin. Dan da ma ta fi jin daɗin kwanciyar. Ya sake zuba mata idanunsa yana jin jikinsa na ƙara yin sanyi.
"Kar fa ya je ya yi wa er mutane illah?" Ya tambayi kansa har lokacin idanunsa na kanta. "Ko kuwa dai yanda ya kula da ita ne ba haka ake ba?" Ya tambayi kansa. Shiru ya yi yana nazari, toh yanzu Mommah ze je ya samu ko kuwa ya ya? "Lallai da na kasance tantirin mara kunya." Ya raya hakan cikin zuciyarsa. A fili kuma se ya sauke ajiyar zuciya, kafin a fili ya furta
"Yess!!." Kallan inda take kwance a kan gadon ya sake yi a karo na barkatai ya ɗan sauke numfashi kafin ya fice daga ɗakin.
.. A ɓangarensu Gwani kuwa tun washegarin ranar da Lulun ta dawo, se ya zamana kamar ana ƙara masa soyayyarta ne. Cikin kwanakin nan sosai ya zage dantse wajen janta a jiki ko dan ta samu ta saki jiki da shi, musamman da ya kasance har lokacin ta kasa sakin jikin da shi gaba ɗaya. Duk da ta san tana ƙaunar ta shi, amma har yanzu ba ta saki jikin ba. Shi kuma so yake shaƙuwa sosai ta shiga tsakaninsu, hakan ne ya sa yake iya ƙoƙarinsa wajen ganin ya samar da hakan.
Sanye take cikin wata riga da skirt na wani yadi mara nauyi, ɗan ƙaramin mayafi ne wanda ta yane kanta da shi. Ta yi mugun kyau, sosai fatarta ta sake fitowa ta yi kyau, ta kuma sake murjewa. Shi ne ya zaɓar mata kayan da kan shi, duk da ta so musawa saboda yanda kayan suka ɗan kamata ranar da ta fara gwadawa, amma se ta kasa kawai ta ɗauka ta saka ɗin. A karo na barkatai ya ɗaga kai ya kalleta, daidai lokacin da itama ta saci kallansa. Se suka sakarwa juna murmushi, tana shirin janye idanunta ya katseta da faɗin
"A'ah fa.." ya yi maganar yana girgiza kai. Turo ɗan ƙaramin bakinta ta yi tana gyara zama a inda take zaune. Daidai lokacin da aka soma knocking ɗin ƙofar ɗakin. Kallan ƙofar bedroom ɗin suka yi kusan a tare. Lulu na shirin miƙewa Gwani ya katseta da faɗin
"A'ah zauna na je na duba." Babu musu ta koma ta zauna. Ya bita da kallo har lokacin be dena fatan ta koma asalin Lulunta ba. Dan ya san ko ta koma Lulun da, rashin kunyar dai babu ita. Se dai har yanzun ba ta koma ba. Abin da yake ta ƙoƙari kenan ya ga ya samu. Se dai yanzun ne gaba ɗaya ta koma wata shiru shiru kamar ba ita ba. Littafin da yake rubutu cikinsa ya ajje kafin ya miƙe kai tsaye ya fice daga ɗakin. A bakin sashen nasu ya samu Bad Man dake kamar a hagitse, kamar kuma ba a hargitse ba.
"Wai da ma kai ne?" Gwani ya tambaya yana kallansa.
"Ni ne fa.." Ya ƙare yana ɗan ajje numfashi kaɗan.
"Toh ai ma je ciki koh?" Gwani ya faɗa yana kallansa. Girgiza kai ya yi kafin ya amsa da
"A'ah ɗan uwa, sauri nake yi wallahi.." Jinjina kai Gwani ya yi kafin yace
"Ohk.." Se da suka gaisa kafin Bad Man ya ɗan shafa sumar kansa kana cikin basarwa yace
"Bro Afaaf na ciki ne?" Da ɗan mamaki shimfiɗe kan fuskar Gwani yake kallan Bad Man. Ya sake babbasarwa yana gyara tsayuwarsa.
"Ehh.." Gwani ya amsa da hakan.
"Taimaka ka yi mata magana, Afrah na son ganinta." Se kuma Gwani ya yi dariya, dan yanda ɗan uwan nasa ya zama a kan mace shi kansa wani lokacin har mamaki abun ke ba shi. Kamar ya tambaye shi abin da ya faru, se dai kuma tun da be sanar da shi ba may be babu buƙatar ya sani ɗin ne. Dan haka yace
"Tohm." Daga haka ya juya ya koma ciki. Lokacin da ya shiga ta shiga cikin kitchen ne. Dan haka kai tsaye can ɗin ya nufa, daidai lokacin da ya zo shiga ita kuma ta zo fitowa, se ta yi baya dan ta ba shi damar wucewa, ya basar kamar be lura ba ya shiga cikin kitchen ɗin. Ƙarasawa ya yi inda take tsaye, kawai se ta saki baki da ido tana kallansa. Ya haɗe tazarar dake tsakaninsu sosai, ya zamana waje kaɗan ne ya raba su.
"Me ya tsorataki haka ne?" Ya tambaya yana kallanta cikin idanunta. Girgiza kai ta yi da sauri kafin tace
"Ba komai fa.."
"Ban yadda ba." Ya faɗa har lokacin yana kallanta. Kwaɓe fuska ta yi dan ba ta san kuma me za tace ba, ga shi kuma se ƙoƙarin haɗe er tazarar da ta yi ragowa a tsakaninsu yake.
"Ni fa tsoron nan ne ba na son gani." Ya yi maganar yana sake matsar da fuskarsa kusa da tata. Kawai se ta runtse idanunta dan ta saddaƙar, dan ta fahimci abin da yake shirin yi. Har ya kusa kaiwa dab da bakinta se kuma ya matsar da fuskarsa baya yana ɗan murmushi. Dena jin numfashinsa da ta yi a kan fuskarta ne ya sanyata buɗe ido. Ba ta san lokacin da ta sauke ajiyar zuciya ba.
"Matsoraciya." Ya faɗa yana lakutar hancinta. Kafin tace komai ya sake faɗin
"Ohhh.." Ya faɗa yana ɗora hannunsa a kan goshinsa. Se ya miƙe tsaye sosai. Be jira tace ko ya sake cewa komai ba ya saka hannu ya saɓeta gaba ɗaya se toilet ɗin. Duk da yanda take ta zillewa haka ya basar ya kaita. Kai tsaye cikin bathtub ɗin ya sakata ciki, yana jinta tana ta en koke_kokenta. Duk da yanda matsanancin tausayinta ya kama shi hakan be sa ya cireta daga ciki ba. Ya ɗan dinga basarwa dan kar ya fusata ya maidata kan gadon. Ita dai yau Didi ta ga abubuwa, dan kuwa haka tana ji tana gani Bad Man ɗin ya saɓeta tass da sabulu. Tun tana kukan tana zillewa har ta gaji ta haƙura. Wai kuma se da ya gama komai sannan ya kalleta yana riƙe da ita yace
"Na yi laifi a yafe min." I zuwa yanzu ita kam har ta gaji da jin wannan kalmar. Ta daɗe da gano shi, wato ba ya tashi bayar da haƙuri se ya aikata abin da yake so, se ya zo yana marairaicewa. Duk da haka kuma be ƙyaleta ba se da ya samo mata wata riga ya zura mata kafin ya ɗauketa dan sauƙaƙa mata ya direta kan gado. I zuwa lokacin ta haƙura kawai ta zubawa sarautar Allah ido, dan ba ta ga alamar yana da niyyar dena duk abin da ya fara ba. Kawai se komawa ta yi ta kwanta, dan duk da ta ji daɗin jikinta amma har yanzu wani iri take jinta daban. Tashi ya yi ya koma kan gadon, ya saka hannunsa ya jata cikin jikinsa yana kallan idanunta da yau ɗin suka ƙi ko da gajiya ne da tara ƙwalla. Cikin kulawa yace
"Haba mana wifey, kukan ya isa haka. Girma ne fa ki ka yi. Kin ga yanzu kin taddo Afaaf, ni ma kuma na taddo ɗan uwa, yanzu haka kanmu ɗaya." Ya ƙare yana murmushin gefen baki. Ita dai waɗannan zancen nasa sake tsundumata suke cikin kunya da sake tuna abin da ya faru be sani ba. Shi kuma da alama ko a jikinsa. Da ze gane da ya yi shiru ya barta ta ji da abin da take ji. Ba ta gama dawowa daga wannan kunyar ba ta sake jiyo muryarsa yana faɗin
"Na san ni jarumi ne.. Yanzu haka da za a auna ki se an tabbatar mana da na yi ajiya.." Tun kafin ya kai karshen maganar tasa ta soma ɗan buga jikinta tana yi kamar za ta soma kuka, lokaci ɗaya kuma tana cusa kanta cikin ƙirjinsa tana jin wata matsananciyar kunya na kamata. Shi dai wallahi sam ba ya da kunya ko kaɗan. Ya gama abin da yake so ya barta da kunya da wahala, ga shi kuma ya zo se kunnota yake yi da maganganunsa da suke sawa ta ji kamar ƙasa ta tsage ta shige. Murmushi ya yi yana ɗan cije lips ɗinsa.
"Shi kenan na dena.." Ya ƙare yana sakin ƙayataccen murmushin gefen baki lokaci ɗaya yana sake rungumeta cike da matsananciyar ƙaunarta. Ita dai ko motsi ba ta yi ba, ta yi shiru a jikin nasa cike da fatan kar ya motsa. Dan idan tana waje ɗaya ta fi jinta normal, da zarar ta motsa kuma se ta ji kamar ta fashe da kuka saboda yanda take jin jikinta.
.. A karo na biyu ya sake kallanta, a nutse yace
"In zo in taimaka miki?" Girgiza kai ta yi tana runtse idanunta cike da fatan ta ji ta koma daidai, ta dena jin komai. Se dai kamar ɗazun yanzun ma komawa ta yi tana ɗan sauke numfashi. Miƙewa ya yi ya ƙaraso kan gadon, ya ranƙwafo yana ƙura mata idanunsa. Cikin kulawa, kuma muryarsa ƙasa ƙasa yace
"Har yanzu dai?" Se da ta buɗe lumsassun idanunta ta kalle shi, kafin ta jinjina kai a sanyaye tana sauke idanunta. Hannu ya miƙa mata yace
"Kama ki tashi mu ga." Miƙa masa hannun ta yi, ya taimaka mata ta miƙe yana lura da yanayinta. Ya ɗan sauke numfashi kafin ya maidata kan gadon daidai lokacin da yake faɗin
"Kwanta ina zuwa.." Babu musu ta koma ta kwanta ɗin. Dan da ma ta fi jin daɗin kwanciyar. Ya sake zuba mata idanunsa yana jin jikinsa na ƙara yin sanyi.
"Kar fa ya je ya yi wa er mutane illah?" Ya tambayi kansa har lokacin idanunsa na kanta. "Ko kuwa dai yanda ya kula da ita ne ba haka ake ba?" Ya tambayi kansa. Shiru ya yi yana nazari, toh yanzu Mommah ze je ya samu ko kuwa ya ya? "Lallai da na kasance tantirin mara kunya." Ya raya hakan cikin zuciyarsa. A fili kuma se ya sauke ajiyar zuciya, kafin a fili ya furta
"Yess!!." Kallan inda take kwance a kan gadon ya sake yi a karo na barkatai ya ɗan sauke numfashi kafin ya fice daga ɗakin.
.. A ɓangarensu Gwani kuwa tun washegarin ranar da Lulun ta dawo, se ya zamana kamar ana ƙara masa soyayyarta ne. Cikin kwanakin nan sosai ya zage dantse wajen janta a jiki ko dan ta samu ta saki jiki da shi, musamman da ya kasance har lokacin ta kasa sakin jikin da shi gaba ɗaya. Duk da ta san tana ƙaunar ta shi, amma har yanzu ba ta saki jikin ba. Shi kuma so yake shaƙuwa sosai ta shiga tsakaninsu, hakan ne ya sa yake iya ƙoƙarinsa wajen ganin ya samar da hakan.
Sanye take cikin wata riga da skirt na wani yadi mara nauyi, ɗan ƙaramin mayafi ne wanda ta yane kanta da shi. Ta yi mugun kyau, sosai fatarta ta sake fitowa ta yi kyau, ta kuma sake murjewa. Shi ne ya zaɓar mata kayan da kan shi, duk da ta so musawa saboda yanda kayan suka ɗan kamata ranar da ta fara gwadawa, amma se ta kasa kawai ta ɗauka ta saka ɗin. A karo na barkatai ya ɗaga kai ya kalleta, daidai lokacin da itama ta saci kallansa. Se suka sakarwa juna murmushi, tana shirin janye idanunta ya katseta da faɗin
"A'ah fa.." ya yi maganar yana girgiza kai. Turo ɗan ƙaramin bakinta ta yi tana gyara zama a inda take zaune. Daidai lokacin da aka soma knocking ɗin ƙofar ɗakin. Kallan ƙofar bedroom ɗin suka yi kusan a tare. Lulu na shirin miƙewa Gwani ya katseta da faɗin
"A'ah zauna na je na duba." Babu musu ta koma ta zauna. Ya bita da kallo har lokacin be dena fatan ta koma asalin Lulunta ba. Dan ya san ko ta koma Lulun da, rashin kunyar dai babu ita. Se dai har yanzun ba ta koma ba. Abin da yake ta ƙoƙari kenan ya ga ya samu. Se dai yanzun ne gaba ɗaya ta koma wata shiru shiru kamar ba ita ba. Littafin da yake rubutu cikinsa ya ajje kafin ya miƙe kai tsaye ya fice daga ɗakin. A bakin sashen nasu ya samu Bad Man dake kamar a hagitse, kamar kuma ba a hargitse ba.
"Wai da ma kai ne?" Gwani ya tambaya yana kallansa.
"Ni ne fa.." Ya ƙare yana ɗan ajje numfashi kaɗan.
"Toh ai ma je ciki koh?" Gwani ya faɗa yana kallansa. Girgiza kai ya yi kafin ya amsa da
"A'ah ɗan uwa, sauri nake yi wallahi.." Jinjina kai Gwani ya yi kafin yace
"Ohk.." Se da suka gaisa kafin Bad Man ya ɗan shafa sumar kansa kana cikin basarwa yace
"Bro Afaaf na ciki ne?" Da ɗan mamaki shimfiɗe kan fuskar Gwani yake kallan Bad Man. Ya sake babbasarwa yana gyara tsayuwarsa.
"Ehh.." Gwani ya amsa da hakan.
"Taimaka ka yi mata magana, Afrah na son ganinta." Se kuma Gwani ya yi dariya, dan yanda ɗan uwan nasa ya zama a kan mace shi kansa wani lokacin har mamaki abun ke ba shi. Kamar ya tambaye shi abin da ya faru, se dai kuma tun da be sanar da shi ba may be babu buƙatar ya sani ɗin ne. Dan haka yace
"Tohm." Daga haka ya juya ya koma ciki. Lokacin da ya shiga ta shiga cikin kitchen ne. Dan haka kai tsaye can ɗin ya nufa, daidai lokacin da ya zo shiga ita kuma ta zo fitowa, se ta yi baya dan ta ba shi damar wucewa, ya basar kamar be lura ba ya shiga cikin kitchen ɗin. Ƙarasawa ya yi inda take tsaye, kawai se ta saki baki da ido tana kallansa. Ya haɗe tazarar dake tsakaninsu sosai, ya zamana waje kaɗan ne ya raba su.
"Me ya tsorataki haka ne?" Ya tambaya yana kallanta cikin idanunta. Girgiza kai ta yi da sauri kafin tace
"Ba komai fa.."
"Ban yadda ba." Ya faɗa har lokacin yana kallanta. Kwaɓe fuska ta yi dan ba ta san kuma me za tace ba, ga shi kuma se ƙoƙarin haɗe er tazarar da ta yi ragowa a tsakaninsu yake.
"Ni fa tsoron nan ne ba na son gani." Ya yi maganar yana sake matsar da fuskarsa kusa da tata. Kawai se ta runtse idanunta dan ta saddaƙar, dan ta fahimci abin da yake shirin yi. Har ya kusa kaiwa dab da bakinta se kuma ya matsar da fuskarsa baya yana ɗan murmushi. Dena jin numfashinsa da ta yi a kan fuskarta ne ya sanyata buɗe ido. Ba ta san lokacin da ta sauke ajiyar zuciya ba.
"Matsoraciya." Ya faɗa yana lakutar hancinta. Kafin tace komai ya sake faɗin