Sashe 81
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.." Shi ne kaɗai abin da Mommah ke maimaitawa hawaye na cigaba da zuba a kan fuskarta, ƙirjinta na bugawar da ya zarce ƙa'ida fiye da tunani. Da gasken kenan giya yake sha? Tsawon wane lokaci ya ɗauka yana sha se yanzu ta sani? Wace irin rayuwa Areef ɗin yake? Shin tsawon wane lokaci ya ɗauka yana wannan ɗab'iar? Mom ta sani? Idan ta sani ya aka yi ba ta tsawatar masa ba? Idan kuma ba ta sani ba ya aka yi ta yi sake hakan ya faru, duk da yanda take nuna kamar ta fi kowa iya kula da ɗa? Shin wacce irin ɗab'ia Areef ɗin ke da ita saboda samun sakacin kulawar uwa? Shaye_shaye? Shaye_shaye a cikin gida ba tare da kowa ya sani ba? Shaye_shaye a matsayinsa na musulmi me ilimin addini? Shin me ya kamata ta yi a irin wannan lokaci. Se ta shiga girgiza kai tana jin wani jiri na kwasarta, wanda ke barazanar kayar da ita. Haka ta daure ta ja jikinta da ƙyar ta nemi waje ta zauna gefen gadon. Ta ɗaga jajayen idanunta ta kalle shi, muryarta na rawa tace
"Areef..." Se ta kasa furta komai dan tsananin tashin hankalin da ta tsinci kanta a ciki.
"Ki yi haƙuri Mommah.. Ba na shan me bugarwa.. ina sha ne kawai dan na saba da rayuwa da ita tun a U.S."
"U.S" Mom ta maimaita tana kafe shi da idanunta. Maganar da ya faɗa yanzun ita ce ta sake ɗaga mata hankali, yana sha ne dan ya saba rayuwa da ita. Kenan duk tsawon rayuwarsa yana sha ko kuwa me yake nufi? Kawai se ta kifa kanta a kan hannunta wasu hawaye masu ɗumi suka shiga zubowa a kan kuncinta. A kan laɓɓanta ta shiga maimaita
"Hasbunahallahu wa ni'imal wakeel.."
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO68*
___ Runtse idanunsa ya yi yana sake kifa kansa jikin gadon zuciyarsa na zafi. Mommah sam ta kasa furta komai, ban da tsoro da kuma faɗuwar gaba da take ji ta kasa cewa komai saboda tsananin tashin hankali. A hankali ya buɗe idanunsa ya sake kallan Mommah, cikin shaƙaƙƙiyar muryarsa ya furta
"Mommah.. Ki dena kukan please.." Se a lokacin sannan ta iya ɗaga kanta ta kalle shi. Ita kaɗai ta san abin da take ji cikin zuciyarta a halin yanzu.
"Da ma rayuwar da ka ɗaukarwa kanka kenan?" Ta yi maganar a sanyaye tana goge hawayen fuskarta. Se ya girgiza kai yana sake buɗe idanunsa da ke lumshewa da kansu.
"Mommah na kasa jurewa ne wallahi. Na kasa jure yanda na zauna tsawon shekaru ina matsayin ɗan macuciya, azzaluma kuma mara imani.. Na kasa jure yanda na shafe tsayin shekaru tare da ke ina miki kallan kishiyar uwata.. Duk yanda na so mantawa da hakan na kasa, duk yanda na so in kawo walwala ta maye gurbin ɓacin ran hakan ya citira. Damuwa na neman yi min yawa Mommah.." Ya ƙare muryarsa a raunane kamar ba ta shi ba.
"Shin ba ka san Alqur'ani shi ne kaɗai maganin damuwa ba? Irin wannan damuwar da kake magana a kai ba ka san ka ɗauki Qur'ani ka karanta ba Areef? Wace irin rayuwa ce wannan ka ɗaukarwa kanka? Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un..." Ta ƙarasa faɗa tana riƙo kanta da ke sara mata. Kawai ta kasa yadda ba mafarki take yi ba. Wai Areef, ɗanta ke shaye shaye. Wannan wace irin baƙar rana ce?
"Ki yi haƙuri Mommah.. Kar ya zamana ranar farin ciki kuma ta koma ta baƙin ciki.." Ya yi maganar kamar ba shi ba. Se ka ce chanja shi a ka yi gaba ɗaya.
"Ba ka so hakan ta faru amma kake shan wani abu Areef?" Mommah ta yi ƙarfin halin faɗin hakan. Se ya girgiza kai kawai yana sake lumshe ido saboda yanda wani bacci me daɗi ya soma fuzgar shi wanda hakan da ya tilastawa idanunsa sake ƙanƙancewa.
Ga kuma tausayin Mommahn da ya kama shi. Yanda duk ta ruɗe lokaci guda, yanayinta gaba ɗaya ya chanja, muryarta ta sauya, haka zalika komai nata ma ya chanja. Abubuwa da dama sun haɗar mata a yau ɗin. Ga wannan labarin da ya zo mata a bazata, ga kuma kama Areef ɗin da ta yi yana shan wani abun. Sun kai wajen minti 3 babu wanda ya sake cewa uffan, kowa da abin da ke saƙawa cikin ransa. Can Mommah ta miƙe jikinta a matuƙar sanyaye. Ta kwashi kwalaben tana jin wani irin ɗaci har a cikin bakinta, ta wuce da su toilet. Babu jimawa ta fito, da alama kuma ta kasa daurewa se da hawaye suka tarar mata. Ta yi saurin kawar da su tana kallansa a kaikaice tace
"Ka shiga ka watsa ruwa yanzun nan ka fito ina jiranka." Mommah ta faɗa tana ƙoƙarin juyawa. Lura da wani siririn hawaye da ya yi a kan fuskarta shi ne ya sanya shi sake buɗe baki a sanyaye yace
"Ki yi haƙuri Mommah.." Kawai se ta fice da sauri ba tare da tace komai ba. A iya yau ɗin abubuwa sun faru da dama. Ita ba fushi take da Bad Man ba, dan ta san rashin kulawar uwa ya yi matuƙar taka muhimmiyar rawa a cikin rayuwarsa. Dan haka ba za ta yi wannan kuskuren a yanzu haka ba. Tun farko Mom ce ta jawo, dagewa da ta yi se an tura shi ƙasar waje ya taimaka ƙwarai, tun da ga shi nan be fara shan komai ba se da ya bar ƙasar. Shi ya sa ashe tun lokacin da za a tura shi wata ƙasar ta ji hankalinta be kwanta ba, ta ji ina ma za ta iya faɗawa Mom ɗin gaskiya, da ta ce mata kar ta bar Areef ɗin ya bar gabanta. Ta gefe guda kuma har yanzu ta kasa gane duk ina tulin masu tsaro da Daddy ya tura masa? Ba su san yana sha ba ne ko kuwa ya ya? Su da aka tura kula da shi, da duk wani abu da yake yi, ya aka yi har ya fara shan wani abu ba su sani ba? An ya kuwa hakan za ta faru? Amma kuma idan sun sani ɗin ya aka yi ba su sanarwa da Daddy ba? Ire_iren wannan tunanin ke ta mata yawo a kwanya. "Ya zama dole na bincika abin da ya faru." Ta tsara hakan cikin zuciyarta. Hannu Mommah ta saka ta kamo na Didi ba tare da tace komai ba ta jata zuwa kan kujera ta zaunar. Babu musu Didi ta zauna, ya yin da Little ya ɗora hannunsa a kan cinyarta.
"Kalle ni nan Afrah.." Mommah ta faɗa tana kallanta. Babu musu ta kalli Mommahn cike da mamakin abin da za ta faɗa mata. Se dai tambayar da Mommahn ta mata ita ce ta sanyata ƙamewa a wajen ta rasa abin da za tace
"Faɗa min halayen Areef da kika sani kin ji?" Ita ce tambayar da Mommahn ta mata. Ta ɗauki kusan minti 1 ba tare da tace komai ba. Se kame_kame kawai da take, daga zarar ta kamo can se ta kamo nan. Amma takamaimai ta rasa abin da za ta faɗa.
"Kin ga kwantar da hankalinki Afrah.. Kin san dai yanzu ni mahaifiyar Areef ce.. Ke kuma na ɗauke ki ne tamkar 'yata.. toh idan dai har kin ɗauke ni a matsayin uwa ki buɗe baki ki faɗa min gaskiya.." Haba, komai rashin kirkinta ai ta yi wa Mommahn kara, tun da komai lalacewar Bad Man ai dai ɗanta ne. Ba kuma za ta so ta buɗe abin da yake a rufe ba. Dan haka a sanyaye tace
"Yana da kirki.." Tun kafin ta kai ƙarshe Mommah ta shiga girgiza kai. Ta ɗan yi murmushi duk da har lokacin ba ta gama komawa daidai ba tun shigarta ɗakin Bad Man.
"Ki faɗa min gaskiya Daughter.. Amma tabbas ba haka ne a ranki ba.." Kawai se ta yi ƙasa da kanta ta rasa abin da za ta ce. Dan ba ƙarya Mommahn ta kasheta da jijiyoyin jikinta. Ajiyar zuciya Mommah ta sauke jin da ta yi Didin ta kasa cewa komai. Ta ɗan lumshe idanunta kafin ta buɗe. Cikin ƙarfin hali, da kokawa da zuciyarta da ke bugawa tace
"Kin san Areef na shan wani abu ne?" Babu shiri Didi ta ɗaga kai ta kalli Mommah cike da mamaki. Ya aka yi ta sani? Waye ya faɗa mata? Ta tambayi kanta.
"Uhmm?? Kar ki ɓoye min komai.." Mommah ta sake faɗa. Runtse idanunta ta yi tana jin yanda jikinta ke rawa kamar wata mara gaskiya. Se kawai ta jinjina kai kafin cikin ƙarfin hali ta soma faɗin
"Ehh Mommah.. Na yi ƙoƙarin barin abun a zuciyata ne ba tare da na faɗawa kowa ba, in yi maganin abun kuma ni kaɗai da yaddar Allah. Ba zan iya tunkarar Mom in faɗa mata abin da ke faruwa ba, ba kuma zan iya faɗa miki ba saboda kamar na tona masa asiri ne bayan babu wanda ya sani. Shi ya sa na cigaba da ƙoƙarin ganin ya dena, amma hakan ya citira. " Shiru Mommah ta yi tana kallanta, lokaci ɗaya tana jin wata ƙaunarta har cikin ranta. Lallai Didin ita ce matar da ya kamata a zauna da ita. Didin ita ce matar nan da ake kira da matar rufin asiri. Yanzu da wata ce aka mata auren haɗi ta fahimci mijin na shaye shaye, ai da tuni mutanen duniya sun ji. Amma ita ta zaɓi ta yi shiru, ba tare da ta sanarwa da kowa ba. Lallai ta cancanci yabo na musamman.
"Allah Ya yi miki albarka Daughter.." Mommah ta faɗa bayan ta rungumeta cike da farin cikin samun sirika kamar Didi. Sanye cikin ƙananan kaya ya fito kamar kodayaushe. Tafiyarsa ta sake zama nutsattstsiya me burgewa. A haka ya ƙaraso inda su Mommahn suke. Sam ya kasa haɗa ido da Mommahn, dan haka ba tare da ya kalleta ba yace
"Mommah na fito.."
"Je ka, ga mu nan zuwa.." Mommah ta ba shi amsa tana miƙewa ita ma ba ta kalle shi ba. Be sake cewa uffan ba ya fice daga ɗakin.
"Areef..." Se ta kasa furta komai dan tsananin tashin hankalin da ta tsinci kanta a ciki.
"Ki yi haƙuri Mommah.. Ba na shan me bugarwa.. ina sha ne kawai dan na saba da rayuwa da ita tun a U.S."
"U.S" Mom ta maimaita tana kafe shi da idanunta. Maganar da ya faɗa yanzun ita ce ta sake ɗaga mata hankali, yana sha ne dan ya saba rayuwa da ita. Kenan duk tsawon rayuwarsa yana sha ko kuwa me yake nufi? Kawai se ta kifa kanta a kan hannunta wasu hawaye masu ɗumi suka shiga zubowa a kan kuncinta. A kan laɓɓanta ta shiga maimaita
"Hasbunahallahu wa ni'imal wakeel.."
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO68*
___ Runtse idanunsa ya yi yana sake kifa kansa jikin gadon zuciyarsa na zafi. Mommah sam ta kasa furta komai, ban da tsoro da kuma faɗuwar gaba da take ji ta kasa cewa komai saboda tsananin tashin hankali. A hankali ya buɗe idanunsa ya sake kallan Mommah, cikin shaƙaƙƙiyar muryarsa ya furta
"Mommah.. Ki dena kukan please.." Se a lokacin sannan ta iya ɗaga kanta ta kalle shi. Ita kaɗai ta san abin da take ji cikin zuciyarta a halin yanzu.
"Da ma rayuwar da ka ɗaukarwa kanka kenan?" Ta yi maganar a sanyaye tana goge hawayen fuskarta. Se ya girgiza kai yana sake buɗe idanunsa da ke lumshewa da kansu.
"Mommah na kasa jurewa ne wallahi. Na kasa jure yanda na zauna tsawon shekaru ina matsayin ɗan macuciya, azzaluma kuma mara imani.. Na kasa jure yanda na shafe tsayin shekaru tare da ke ina miki kallan kishiyar uwata.. Duk yanda na so mantawa da hakan na kasa, duk yanda na so in kawo walwala ta maye gurbin ɓacin ran hakan ya citira. Damuwa na neman yi min yawa Mommah.." Ya ƙare muryarsa a raunane kamar ba ta shi ba.
"Shin ba ka san Alqur'ani shi ne kaɗai maganin damuwa ba? Irin wannan damuwar da kake magana a kai ba ka san ka ɗauki Qur'ani ka karanta ba Areef? Wace irin rayuwa ce wannan ka ɗaukarwa kanka? Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un..." Ta ƙarasa faɗa tana riƙo kanta da ke sara mata. Kawai ta kasa yadda ba mafarki take yi ba. Wai Areef, ɗanta ke shaye shaye. Wannan wace irin baƙar rana ce?
"Ki yi haƙuri Mommah.. Kar ya zamana ranar farin ciki kuma ta koma ta baƙin ciki.." Ya yi maganar kamar ba shi ba. Se ka ce chanja shi a ka yi gaba ɗaya.
"Ba ka so hakan ta faru amma kake shan wani abu Areef?" Mommah ta yi ƙarfin halin faɗin hakan. Se ya girgiza kai kawai yana sake lumshe ido saboda yanda wani bacci me daɗi ya soma fuzgar shi wanda hakan da ya tilastawa idanunsa sake ƙanƙancewa.
Ga kuma tausayin Mommahn da ya kama shi. Yanda duk ta ruɗe lokaci guda, yanayinta gaba ɗaya ya chanja, muryarta ta sauya, haka zalika komai nata ma ya chanja. Abubuwa da dama sun haɗar mata a yau ɗin. Ga wannan labarin da ya zo mata a bazata, ga kuma kama Areef ɗin da ta yi yana shan wani abun. Sun kai wajen minti 3 babu wanda ya sake cewa uffan, kowa da abin da ke saƙawa cikin ransa. Can Mommah ta miƙe jikinta a matuƙar sanyaye. Ta kwashi kwalaben tana jin wani irin ɗaci har a cikin bakinta, ta wuce da su toilet. Babu jimawa ta fito, da alama kuma ta kasa daurewa se da hawaye suka tarar mata. Ta yi saurin kawar da su tana kallansa a kaikaice tace
"Ka shiga ka watsa ruwa yanzun nan ka fito ina jiranka." Mommah ta faɗa tana ƙoƙarin juyawa. Lura da wani siririn hawaye da ya yi a kan fuskarta shi ne ya sanya shi sake buɗe baki a sanyaye yace
"Ki yi haƙuri Mommah.." Kawai se ta fice da sauri ba tare da tace komai ba. A iya yau ɗin abubuwa sun faru da dama. Ita ba fushi take da Bad Man ba, dan ta san rashin kulawar uwa ya yi matuƙar taka muhimmiyar rawa a cikin rayuwarsa. Dan haka ba za ta yi wannan kuskuren a yanzu haka ba. Tun farko Mom ce ta jawo, dagewa da ta yi se an tura shi ƙasar waje ya taimaka ƙwarai, tun da ga shi nan be fara shan komai ba se da ya bar ƙasar. Shi ya sa ashe tun lokacin da za a tura shi wata ƙasar ta ji hankalinta be kwanta ba, ta ji ina ma za ta iya faɗawa Mom ɗin gaskiya, da ta ce mata kar ta bar Areef ɗin ya bar gabanta. Ta gefe guda kuma har yanzu ta kasa gane duk ina tulin masu tsaro da Daddy ya tura masa? Ba su san yana sha ba ne ko kuwa ya ya? Su da aka tura kula da shi, da duk wani abu da yake yi, ya aka yi har ya fara shan wani abu ba su sani ba? An ya kuwa hakan za ta faru? Amma kuma idan sun sani ɗin ya aka yi ba su sanarwa da Daddy ba? Ire_iren wannan tunanin ke ta mata yawo a kwanya. "Ya zama dole na bincika abin da ya faru." Ta tsara hakan cikin zuciyarta. Hannu Mommah ta saka ta kamo na Didi ba tare da tace komai ba ta jata zuwa kan kujera ta zaunar. Babu musu Didi ta zauna, ya yin da Little ya ɗora hannunsa a kan cinyarta.
"Kalle ni nan Afrah.." Mommah ta faɗa tana kallanta. Babu musu ta kalli Mommahn cike da mamakin abin da za ta faɗa mata. Se dai tambayar da Mommahn ta mata ita ce ta sanyata ƙamewa a wajen ta rasa abin da za tace
"Faɗa min halayen Areef da kika sani kin ji?" Ita ce tambayar da Mommahn ta mata. Ta ɗauki kusan minti 1 ba tare da tace komai ba. Se kame_kame kawai da take, daga zarar ta kamo can se ta kamo nan. Amma takamaimai ta rasa abin da za ta faɗa.
"Kin ga kwantar da hankalinki Afrah.. Kin san dai yanzu ni mahaifiyar Areef ce.. Ke kuma na ɗauke ki ne tamkar 'yata.. toh idan dai har kin ɗauke ni a matsayin uwa ki buɗe baki ki faɗa min gaskiya.." Haba, komai rashin kirkinta ai ta yi wa Mommahn kara, tun da komai lalacewar Bad Man ai dai ɗanta ne. Ba kuma za ta so ta buɗe abin da yake a rufe ba. Dan haka a sanyaye tace
"Yana da kirki.." Tun kafin ta kai ƙarshe Mommah ta shiga girgiza kai. Ta ɗan yi murmushi duk da har lokacin ba ta gama komawa daidai ba tun shigarta ɗakin Bad Man.
"Ki faɗa min gaskiya Daughter.. Amma tabbas ba haka ne a ranki ba.." Kawai se ta yi ƙasa da kanta ta rasa abin da za ta ce. Dan ba ƙarya Mommahn ta kasheta da jijiyoyin jikinta. Ajiyar zuciya Mommah ta sauke jin da ta yi Didin ta kasa cewa komai. Ta ɗan lumshe idanunta kafin ta buɗe. Cikin ƙarfin hali, da kokawa da zuciyarta da ke bugawa tace
"Kin san Areef na shan wani abu ne?" Babu shiri Didi ta ɗaga kai ta kalli Mommah cike da mamaki. Ya aka yi ta sani? Waye ya faɗa mata? Ta tambayi kanta.
"Uhmm?? Kar ki ɓoye min komai.." Mommah ta sake faɗa. Runtse idanunta ta yi tana jin yanda jikinta ke rawa kamar wata mara gaskiya. Se kawai ta jinjina kai kafin cikin ƙarfin hali ta soma faɗin
"Ehh Mommah.. Na yi ƙoƙarin barin abun a zuciyata ne ba tare da na faɗawa kowa ba, in yi maganin abun kuma ni kaɗai da yaddar Allah. Ba zan iya tunkarar Mom in faɗa mata abin da ke faruwa ba, ba kuma zan iya faɗa miki ba saboda kamar na tona masa asiri ne bayan babu wanda ya sani. Shi ya sa na cigaba da ƙoƙarin ganin ya dena, amma hakan ya citira. " Shiru Mommah ta yi tana kallanta, lokaci ɗaya tana jin wata ƙaunarta har cikin ranta. Lallai Didin ita ce matar da ya kamata a zauna da ita. Didin ita ce matar nan da ake kira da matar rufin asiri. Yanzu da wata ce aka mata auren haɗi ta fahimci mijin na shaye shaye, ai da tuni mutanen duniya sun ji. Amma ita ta zaɓi ta yi shiru, ba tare da ta sanarwa da kowa ba. Lallai ta cancanci yabo na musamman.
"Allah Ya yi miki albarka Daughter.." Mommah ta faɗa bayan ta rungumeta cike da farin cikin samun sirika kamar Didi. Sanye cikin ƙananan kaya ya fito kamar kodayaushe. Tafiyarsa ta sake zama nutsattstsiya me burgewa. A haka ya ƙaraso inda su Mommahn suke. Sam ya kasa haɗa ido da Mommahn, dan haka ba tare da ya kalleta ba yace
"Mommah na fito.."
"Je ka, ga mu nan zuwa.." Mommah ta ba shi amsa tana miƙewa ita ma ba ta kalle shi ba. Be sake cewa uffan ba ya fice daga ɗakin.