Sashe 63
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'ah Ummeey ki bar shi zan ɗibo.." Murmushi Ummeey ta yi tana bin Lulun da kallo lokacin da ta wuce wajen randar ta buɗe ta ɗiba.
Sauke numfashi Lulu ta yi lokacin da ta zauna a kan gadon tace tana miƙawa Fatima Jug ɗin
"Ga shi ki sha ki ƙoshi.."
"Yawwah ko ke fa." Ta faɗa tana karɓa. Se kuma ta ɗora da
"Wai ba ki da lafiya ne?" Da sauri Lulu ta kalleta cike da mamakin abin da ta faɗa ɗin
"Me ki ka gani?" Ta yi ƙarfin halin faɗin hakan.
"Ganinki na yi kamar ba ke ba. Kin zama shiru shiru.. Ke kin dai koma kamar Didi." Sauke ajiyar zuciya ta yi tana ɗan lumshe idanunta. A fili kuma se ta harari Fatiman tace
"Oho miki dai."
Hira sosai suka sha kasancewar sun kwana biyu ba su ga juna ba. Fatima na sake jin daɗin yanda Lulun ta sauya kamar ba ita ba. Babu laifi ta ɗan jima a gidan. Se dai kamar yanda ta yi wa Ummanta alƙawari ba ta wuce hakan ba. Don haka lokacin da ta gama shiri se ta kalli Lulu tace
"Toh ni zan tafi.. Se haɗuwa ta gaba." Ba dan Lulu ta ji daɗi ba ta buɗe baki za ta yi magana Fatima tace
"Laaa Masoyiya na manta ban faɗa miki ba. Kin san da wa na haɗu ɗazu kuwa?" Girgiza kai Lulu ta yi kana ta amsa da
"A'ah.."
"Mutuniyarki Abida.." ta ƙare tana taɓe baki. Kallanta Lulu ta yi, cikin mamaki tace
"A'ah da ma ba ku na haɗuwa kullum a Islamiyya ba.?"
"Waaa..? Abidar? Tun yaushe aka koreta ke kam? Har babansu fa se da ya daɗe yana zuwa makarantar wai ashe duk a kan halin Abidar ne. Se daga baya kuma ya dena zuwa." Shiru Lulu ta yi na tsawon sakanni masu ɗan yawa. Ashe ma an kori Abidar daga Islamiyyar?
"Ai gwara haka.. Allah Ya shirya." Lulu ta faɗa.
"Ameen. Uhmm kin ga wucewata Masoyiya bye.." ta faɗa tana juyawa.
"Na gode sosai Masoyiya. Don Allah ki gaida min da Umma."
"Za ta ji." Ta ƙare maganar lokacin da ta gama ficewa daga ɗakin. A tsakar gida ta tarar da Ummeey da kuma Gwani da shigowarsa kenan. Cikin girmamawa tace
"Barka da wannan lokaci Ya mu'allim."
"Barka dai Fatima." Gwani ya amsa da hakan yana miƙewa tsaye daga zaunen da yake kan tabarmar da Ummeey ta ke kai.
"Toh Ummeey na tafi.." Fatima ta faɗa tana kallan Ummeey.
"Toh a gaida mutanen gidan."
"Za su ji In Sha Allah." Daga haka ta fice daga gidan.
... A karo na barkatai ta sake kallan agogon ɗakin da ya nuna ƙarfe 8 na dare daidai. An ya kuwa Little ɗin na sashen Mommah? Ko dai ya taho shi ɗaya be gane hanya ba ya yi wani wajen? Ta tambayi kanta tana miƙewa tsaye. Ita dai har ga Allah hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba idan ba ta ga Little ɗin ba. Miƙewa ta yi a nutse ta fice daga ɗakin. Daidai ta zo fita ta tuna da gargaɗin da ya mata ɗazun. Se ta dakata tana ji kamar ta fashe da kuka. Ta fi ƙarfin minti 10 tsaye a wajen ba tare da ta sake yunƙurin yin komai ba. Se kuma a hankali ta juya da niyyar komawa.
"A'ah Rankiyadaɗe." Ta jiyo muryar Baba Atine. Se ta juyo da sauri cike da jin daɗin ganinta. Don ko babu komai ta san ita ta fita da Little. May be ma yanzun ta dawo mata da shi ne. Se dai se ta ga Baba Atinen ita ɗaya ba wani Little.
"Ina Areef ɗin.. Ko ya yi bacci ne?" Baba Atine ta tambaya tana murmushi.
"Ai ba ya nan Baba."
"Ba ya nan kuma?" Ta yi tambayar cike da mamaki. Wanda hakan ba ƙaramin kaɗa 'ya'yan cikin Didi ya yi ba.
"Aeho.. Aff.. Ai na manta ɗazun sun fita da Yallaɓai Areef." Duk da yanda ta ji abin wani banbarakwai amma hakan be hanata sauke numfashi ba. Ba tare da ta san a fili ba ne ta furta
"Yallaɓai Areef kuma?"
"Ƙwarai kuwa sun fita tare.. Kar ki damu." Cikin wata nutsuwar da ta sake samu ta lumshe idanunta kafin tace
"Toh Baba na gode." Se da ta miƙa mata saƙon da Mommah ta aiko mata da shi sannan ta mata se da safe ta fice daga ɗakin. Cigaba da tsayuwa ta yi kamar wadda aka dasa. Fisabilillahi ya fita da yaro amma har yanzu be dawo ba? Ta raya hakan a ranta tana turo baki. Da dai ta ga tsayuwar ba za ta yi mata ba se ta nemi waje ta zauna tana cigaba da jiran nasu. Dan kuwa hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba idan ba ta ga Little ɗin ba..
.... A ɓangaren Ammi kuwa tun ranar da ta sauka a garin da ta je se ta tarar jikin Gwaggon na buƙatar ganin Likita. Don haka da kanta ta ɗauketa zuwa asibiti. Abinka da jikin tsufa nan take aka basu kwanciya. Cikin ikon Allah kamar yanda jikin Gwaggon ya saba a kwana 2 se ga shi jiki ya yi kyau kamar ba ita ce mara lafiya ba.
Gwaggon na kishingiɗe a kan gadon, ya yin da Ammi ke zaune a kan kujera. Wadda ke jinyar ta kusa da gadonsu ma tana kan kujera tana kallan Gwaggo wadda ta su ta zo ɗaya. Suna ta hirarsu kamar sun saba. Se dai lokaci zuwa lokaci ta kan juya ta kalli wadda take jinyar saboda tsaro. Mata ce wadda a kallan farko idan ka mata za ka ɗauka ta baiwa 50 baya. Se dai kuma ko 45 ba ta rufa ba. A kishingiɗe take, kallan farko ka mata se ka ɗauka lafiyayyiya ce. Se dai a zahiri gaba ɗaya jikinta ba ya aiki idan ka cire hannunta na dama wanda shi kaɗai ne ke iya motsi a jikinta. Se kam idanunta da take ƙiftasu lokaci zuwa lokaci. Idan ka kalleta za ka san tabbas tana tare da hirarsu Gwaggon. Dan kuwa ka na kallan ƙwayar idanunta za ka san da tana da baki za ta buɗe ne ta taya su hirar. Se dai da yake babu bakin, se ya kasance kawai jinsu take yi babu damar amsawa. Ita dai Ammi na gefe se dai ta yi murmushi kawai idan kuma an sakota ciki ta ɗan tofa albarkacin bakinta.
"Kuma wai wannan ɗin ma ɗiyarki ce ta cikinki Gwaggo?" Matar ta tambaya tana murmushi. Kallan Ammi Gwaggo ta yi se ta yi murmushi sannan ta maida dubanta kan matar tace
"'Yata ce.. Ita kuma a Kano take aure.." Ta ƙare tana murmushi.
"Allah sarki kuma tun farkon aurenta a Kanon take zaune?"
"Eh tun ranar da aka ɗaura mata aure."
Waro idanunta wannan mara lafiyar ta yi. Se dai da yake babu baki, ba kuma za ta iya motsa jikinta ba ya sanya duk ba su lura da hakan ba. Tsananin tashin hankalin da na gani cikin idanunta shi ne ya sanya ni sake kafe idanu ina kallanta. Daidai lokacin da ta ɗaga lafiyayyen hannunta ta soma yafito Ammi wadda sam ba ta lura da ita ba. Hatta Gwaggo da ita me jinyar tata babu wanda ya lura da ita. Ta runtse idanunta tana jin zuciyarta na karyewa. Se ta sake yin amfani da hannun nata ta daki wata roba da ke kan gadon. Se kuwa ta faɗi a ƙasa, wanda hakan ya janyo hankalinsu Gwaggo gaba ɗaya suka kalleta. Da sauri me jinyar tata ta miƙe ta ƙarasa inda take tana faɗin
"Lafiya..?" Inaa.. ita sam ba ta ta take ba. Ta rasa yanda za ta yi a fahimci abin da take nufi. Se dai yanzu da yake duk hankalinsu na kanta ne ya sanyata sake yin amfani da hannunta ta yi wa Ammi alama da ta zo. Babu ɓata lokaci Ammi ta miƙe ta ƙaraso har inda take. Still dai ba ta dena miƙa mata hannun ba. Hakan ne ya sanya Ammi saka hannunta ta riƙo na mara lafiyar tana maida dubanta kan fuskarta. So take ta yi magana se dai ta kasa. Ta yi iya bakin ƙoƙarinta ko yau ɗin Allah ze buɗe mata baki ta samu ta yi magana, ta samu ko da saƙo ne ta bayar kafin ta bar duniyar nan. Se dai duk iya ƙoƙarinta ta kasa ko da motsa bakin ne. Idanunta da suka yi jajir kamar gauta har sun soma zubar da hawaye. Da za ta iya magana da idanunta da ta yi hakan a yanzu. Se dai hakan ba me yiwuwa ba ne. Amma kuma ko da idanunta ka kalla se ka tausaya mata. Saboda yanda take cigaba da bin Ammin da kallo kamar me mata magana da idanu. Cikin tausayawa Ammi ke kallanta cike da mamakin abin da ke faruwa. Me ya faru? Wace ce wannan ɗin? Me take so tace mata?..
🤔🤐g
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO58*
___Cigaba ta yi da iya ƙoƙarinta ko za ta iya yin maganar, se dai duk yanda ta yi hakan ya citira. Dalili kenan da ya sanya wasu hawaye masu ɗumi suka zubo a kan kuncinta har kuma lokacin idanunta na kan Ammi, haka hannunta na cikin na Ammi. Daga Ammi, Gwaggo har me jinyar tata me suna Talatuwa mamaki da tausayinta ya gama cikasu. Se dai abin da ya ɗaga hankulan gaba ɗayansu shi ne yanda jikin Maimuna ya rikice cikin lokaci ƙanƙani. Dan kuwa idanunta ne suka soma ƙaƙƙafewa kamar wadda ke shirin barin duniyar. Cikin matuƙar tashin hankali Talatuwa ta fashe da kuka tana faɗin
"Na shiga 3.. Me yake faruwa da ke Maimuna." Ta faɗa tana kai hannunta jikin Maimunan ba tare da ta yi yunƙurin zuwa kiran likita ba. Ganin da Ammi ta yi ita kanta Talatun ba ta a hayyacin da za ta iya zuwa kiran likita ya sanya Ammin fita daga ɗakin da sauri. Se dai tun a ƙofar ɗakin ma suka haɗu da likitan kasancewar lokacin da ze duba marasa lafiya ya yi. Se ta faɗa masa abin da ya faru. Nan da nan kuwa ya ƙarasa cikin ɗakin.
Sauke numfashi Lulu ta yi lokacin da ta zauna a kan gadon tace tana miƙawa Fatima Jug ɗin
"Ga shi ki sha ki ƙoshi.."
"Yawwah ko ke fa." Ta faɗa tana karɓa. Se kuma ta ɗora da
"Wai ba ki da lafiya ne?" Da sauri Lulu ta kalleta cike da mamakin abin da ta faɗa ɗin
"Me ki ka gani?" Ta yi ƙarfin halin faɗin hakan.
"Ganinki na yi kamar ba ke ba. Kin zama shiru shiru.. Ke kin dai koma kamar Didi." Sauke ajiyar zuciya ta yi tana ɗan lumshe idanunta. A fili kuma se ta harari Fatiman tace
"Oho miki dai."
Hira sosai suka sha kasancewar sun kwana biyu ba su ga juna ba. Fatima na sake jin daɗin yanda Lulun ta sauya kamar ba ita ba. Babu laifi ta ɗan jima a gidan. Se dai kamar yanda ta yi wa Ummanta alƙawari ba ta wuce hakan ba. Don haka lokacin da ta gama shiri se ta kalli Lulu tace
"Toh ni zan tafi.. Se haɗuwa ta gaba." Ba dan Lulu ta ji daɗi ba ta buɗe baki za ta yi magana Fatima tace
"Laaa Masoyiya na manta ban faɗa miki ba. Kin san da wa na haɗu ɗazu kuwa?" Girgiza kai Lulu ta yi kana ta amsa da
"A'ah.."
"Mutuniyarki Abida.." ta ƙare tana taɓe baki. Kallanta Lulu ta yi, cikin mamaki tace
"A'ah da ma ba ku na haɗuwa kullum a Islamiyya ba.?"
"Waaa..? Abidar? Tun yaushe aka koreta ke kam? Har babansu fa se da ya daɗe yana zuwa makarantar wai ashe duk a kan halin Abidar ne. Se daga baya kuma ya dena zuwa." Shiru Lulu ta yi na tsawon sakanni masu ɗan yawa. Ashe ma an kori Abidar daga Islamiyyar?
"Ai gwara haka.. Allah Ya shirya." Lulu ta faɗa.
"Ameen. Uhmm kin ga wucewata Masoyiya bye.." ta faɗa tana juyawa.
"Na gode sosai Masoyiya. Don Allah ki gaida min da Umma."
"Za ta ji." Ta ƙare maganar lokacin da ta gama ficewa daga ɗakin. A tsakar gida ta tarar da Ummeey da kuma Gwani da shigowarsa kenan. Cikin girmamawa tace
"Barka da wannan lokaci Ya mu'allim."
"Barka dai Fatima." Gwani ya amsa da hakan yana miƙewa tsaye daga zaunen da yake kan tabarmar da Ummeey ta ke kai.
"Toh Ummeey na tafi.." Fatima ta faɗa tana kallan Ummeey.
"Toh a gaida mutanen gidan."
"Za su ji In Sha Allah." Daga haka ta fice daga gidan.
... A karo na barkatai ta sake kallan agogon ɗakin da ya nuna ƙarfe 8 na dare daidai. An ya kuwa Little ɗin na sashen Mommah? Ko dai ya taho shi ɗaya be gane hanya ba ya yi wani wajen? Ta tambayi kanta tana miƙewa tsaye. Ita dai har ga Allah hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba idan ba ta ga Little ɗin ba. Miƙewa ta yi a nutse ta fice daga ɗakin. Daidai ta zo fita ta tuna da gargaɗin da ya mata ɗazun. Se ta dakata tana ji kamar ta fashe da kuka. Ta fi ƙarfin minti 10 tsaye a wajen ba tare da ta sake yunƙurin yin komai ba. Se kuma a hankali ta juya da niyyar komawa.
"A'ah Rankiyadaɗe." Ta jiyo muryar Baba Atine. Se ta juyo da sauri cike da jin daɗin ganinta. Don ko babu komai ta san ita ta fita da Little. May be ma yanzun ta dawo mata da shi ne. Se dai se ta ga Baba Atinen ita ɗaya ba wani Little.
"Ina Areef ɗin.. Ko ya yi bacci ne?" Baba Atine ta tambaya tana murmushi.
"Ai ba ya nan Baba."
"Ba ya nan kuma?" Ta yi tambayar cike da mamaki. Wanda hakan ba ƙaramin kaɗa 'ya'yan cikin Didi ya yi ba.
"Aeho.. Aff.. Ai na manta ɗazun sun fita da Yallaɓai Areef." Duk da yanda ta ji abin wani banbarakwai amma hakan be hanata sauke numfashi ba. Ba tare da ta san a fili ba ne ta furta
"Yallaɓai Areef kuma?"
"Ƙwarai kuwa sun fita tare.. Kar ki damu." Cikin wata nutsuwar da ta sake samu ta lumshe idanunta kafin tace
"Toh Baba na gode." Se da ta miƙa mata saƙon da Mommah ta aiko mata da shi sannan ta mata se da safe ta fice daga ɗakin. Cigaba da tsayuwa ta yi kamar wadda aka dasa. Fisabilillahi ya fita da yaro amma har yanzu be dawo ba? Ta raya hakan a ranta tana turo baki. Da dai ta ga tsayuwar ba za ta yi mata ba se ta nemi waje ta zauna tana cigaba da jiran nasu. Dan kuwa hankalinta ba ze taɓa kwanciya ba idan ba ta ga Little ɗin ba..
.... A ɓangaren Ammi kuwa tun ranar da ta sauka a garin da ta je se ta tarar jikin Gwaggon na buƙatar ganin Likita. Don haka da kanta ta ɗauketa zuwa asibiti. Abinka da jikin tsufa nan take aka basu kwanciya. Cikin ikon Allah kamar yanda jikin Gwaggon ya saba a kwana 2 se ga shi jiki ya yi kyau kamar ba ita ce mara lafiya ba.
Gwaggon na kishingiɗe a kan gadon, ya yin da Ammi ke zaune a kan kujera. Wadda ke jinyar ta kusa da gadonsu ma tana kan kujera tana kallan Gwaggo wadda ta su ta zo ɗaya. Suna ta hirarsu kamar sun saba. Se dai lokaci zuwa lokaci ta kan juya ta kalli wadda take jinyar saboda tsaro. Mata ce wadda a kallan farko idan ka mata za ka ɗauka ta baiwa 50 baya. Se dai kuma ko 45 ba ta rufa ba. A kishingiɗe take, kallan farko ka mata se ka ɗauka lafiyayyiya ce. Se dai a zahiri gaba ɗaya jikinta ba ya aiki idan ka cire hannunta na dama wanda shi kaɗai ne ke iya motsi a jikinta. Se kam idanunta da take ƙiftasu lokaci zuwa lokaci. Idan ka kalleta za ka san tabbas tana tare da hirarsu Gwaggon. Dan kuwa ka na kallan ƙwayar idanunta za ka san da tana da baki za ta buɗe ne ta taya su hirar. Se dai da yake babu bakin, se ya kasance kawai jinsu take yi babu damar amsawa. Ita dai Ammi na gefe se dai ta yi murmushi kawai idan kuma an sakota ciki ta ɗan tofa albarkacin bakinta.
"Kuma wai wannan ɗin ma ɗiyarki ce ta cikinki Gwaggo?" Matar ta tambaya tana murmushi. Kallan Ammi Gwaggo ta yi se ta yi murmushi sannan ta maida dubanta kan matar tace
"'Yata ce.. Ita kuma a Kano take aure.." Ta ƙare tana murmushi.
"Allah sarki kuma tun farkon aurenta a Kanon take zaune?"
"Eh tun ranar da aka ɗaura mata aure."
Waro idanunta wannan mara lafiyar ta yi. Se dai da yake babu baki, ba kuma za ta iya motsa jikinta ba ya sanya duk ba su lura da hakan ba. Tsananin tashin hankalin da na gani cikin idanunta shi ne ya sanya ni sake kafe idanu ina kallanta. Daidai lokacin da ta ɗaga lafiyayyen hannunta ta soma yafito Ammi wadda sam ba ta lura da ita ba. Hatta Gwaggo da ita me jinyar tata babu wanda ya lura da ita. Ta runtse idanunta tana jin zuciyarta na karyewa. Se ta sake yin amfani da hannun nata ta daki wata roba da ke kan gadon. Se kuwa ta faɗi a ƙasa, wanda hakan ya janyo hankalinsu Gwaggo gaba ɗaya suka kalleta. Da sauri me jinyar tata ta miƙe ta ƙarasa inda take tana faɗin
"Lafiya..?" Inaa.. ita sam ba ta ta take ba. Ta rasa yanda za ta yi a fahimci abin da take nufi. Se dai yanzu da yake duk hankalinsu na kanta ne ya sanyata sake yin amfani da hannunta ta yi wa Ammi alama da ta zo. Babu ɓata lokaci Ammi ta miƙe ta ƙaraso har inda take. Still dai ba ta dena miƙa mata hannun ba. Hakan ne ya sanya Ammi saka hannunta ta riƙo na mara lafiyar tana maida dubanta kan fuskarta. So take ta yi magana se dai ta kasa. Ta yi iya bakin ƙoƙarinta ko yau ɗin Allah ze buɗe mata baki ta samu ta yi magana, ta samu ko da saƙo ne ta bayar kafin ta bar duniyar nan. Se dai duk iya ƙoƙarinta ta kasa ko da motsa bakin ne. Idanunta da suka yi jajir kamar gauta har sun soma zubar da hawaye. Da za ta iya magana da idanunta da ta yi hakan a yanzu. Se dai hakan ba me yiwuwa ba ne. Amma kuma ko da idanunta ka kalla se ka tausaya mata. Saboda yanda take cigaba da bin Ammin da kallo kamar me mata magana da idanu. Cikin tausayawa Ammi ke kallanta cike da mamakin abin da ke faruwa. Me ya faru? Wace ce wannan ɗin? Me take so tace mata?..
🤔🤐g
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO58*
___Cigaba ta yi da iya ƙoƙarinta ko za ta iya yin maganar, se dai duk yanda ta yi hakan ya citira. Dalili kenan da ya sanya wasu hawaye masu ɗumi suka zubo a kan kuncinta har kuma lokacin idanunta na kan Ammi, haka hannunta na cikin na Ammi. Daga Ammi, Gwaggo har me jinyar tata me suna Talatuwa mamaki da tausayinta ya gama cikasu. Se dai abin da ya ɗaga hankulan gaba ɗayansu shi ne yanda jikin Maimuna ya rikice cikin lokaci ƙanƙani. Dan kuwa idanunta ne suka soma ƙaƙƙafewa kamar wadda ke shirin barin duniyar. Cikin matuƙar tashin hankali Talatuwa ta fashe da kuka tana faɗin
"Na shiga 3.. Me yake faruwa da ke Maimuna." Ta faɗa tana kai hannunta jikin Maimunan ba tare da ta yi yunƙurin zuwa kiran likita ba. Ganin da Ammi ta yi ita kanta Talatun ba ta a hayyacin da za ta iya zuwa kiran likita ya sanya Ammin fita daga ɗakin da sauri. Se dai tun a ƙofar ɗakin ma suka haɗu da likitan kasancewar lokacin da ze duba marasa lafiya ya yi. Se ta faɗa masa abin da ya faru. Nan da nan kuwa ya ƙarasa cikin ɗakin.