Sashe 111
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Allah Ya sa lafiya.. Duk da dai kin kai ki yi abin da kike so cikin gidan nan, se dai wannan ɗin abu ne me muhimmanci, dan haka zan so in ji dalilinki na faɗin hakan.. Wani abu ya faru ne?" Ya faɗa cike da fatan ba wani abu ne babba ba. Se da Mommah ta gyara zama tana tunanin ta inda za ta fara. Se da ta ɗauki wajen minti 1 ba tare da tace komai ba kafin ta soma faɗin
"Babu amfanin cigaba da zama da su.. sun ci amanarka Rankayadaɗe.." Daga nan ta shiga sanar da shi abubuwan da suka faru, da irin gwagwarmayar da suka sha wajen ganin sun ƙwato Areef ɗin daga halayyar da ya jefa kansa ciki. Da taimakon Ubangiji kuwa se ga shi ya dena ɗin. Hannu Daddy ya kai ya sauke hular kansa ya ajjeta a gefe.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel.." Abin da ya din ga maimaitawa kenan yana jin yanda ilahirin jikinsa ya yi mugun sanyi.
"Kar ka ɗaga hankalinka Yallaɓai.. Komai ya daidaita da izinin Ubangiji. Ban ma so bari ka sani ba saboda sanin halinka, dan dai ka nemi da ka sani ɗin ne ya sa na sanar da kai. Don Allah kar ka saka damuwa a ranka." Girgiza kai Daddy ya yi kafin ya sauke dogon numfashi. Ya yi murmushin yaƙe sannan yace
"Allah Ya kyauta.." Ya yi maganar yana ƙoƙarin miƙewa. Da sauri Mommah ta katse shi, ta hanyar faɗin
"A'ah don Allah.. Da na san haka ne ai da ban faɗa maka ba." Mommah ta faɗa yanayin fuskarta na sauyawa. Se ya koma ya zauna yana faɗin
"Ina tunanin abin da ya kamata na yi ne. Ashe yanzu duk yaddar da na ba su se da suka ci amanata? Me ye amfanin zuwansu kenan? Duk zaman nan da suka yi babu wanda ya taɓa buɗar baki yace ga abin da Areef ke yi. Se ga shi yanzu abin da nake ji.. Kaii!!" Ya ƙare yana dafe kansa.
"Ka yi haƙuri.. In Sha Allah komai ya wuce Uhmmm?" Ɗaga kansa ya yi kafin yace
"Allah Ya yadda.. Ya ƙara shirya mana su dukansu. Su kuma duk za su haɗu da ni ne." Ya ƙare maganar a ransa yana tunanin abin da ya kamata ya yi musu.
.. Lokacin da Gwani da Lulu suka isa gidan a kwance sosai suka tarar da Abeey, wanda har hakan ya so baiwa Gwani tsoro. Dan haka cikin ƙanƙanin lokaci ya ɗauki Abeeyn se asibiti. Babu ɓata lokaci aka ba shi taimakon gaggawa, aka kuma yi masa duk abin da ya dace. Kiran Daddy da ya gani cikin wayarsa shi ne abin da ya sanya shi komawa ya zauna. Ya ɗaga wayar yana karawa a kunnensa.
"Barka da wannan lokaci Daddy."
"Barka dai Son.. Ka na cikin gida ne?" Se da ya kalli Ummeey da Lulu ke kusa da ita kafin ya girgiza kai
"A'ah muna asibiti."
"Subhanallahi.. waye ba lafiya?" Daddy ya tambaya cike da mamaki.
"Abeey ne.." Ya bayar da amsar kansa na kallan ƙasan tiles ɗin asibitin.
"Ya ilahy! Da ma ba shi da lafiya ne?" Se da Gwani ya sauke ajiyar zuciya kafin yace
"Eh toh.. Daddy da ma dai yana fama da rashin lafiyar ne, ga kuma ciwon ƙoda.. Wani lokacin jikin kan motsa ba ma tare da kowa ya sani ba. Se dai a wannan karon abin ya kai shi ƙasa ne, se da ya kayar da shi."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!" Daddy ya faɗa muryarsa na bayyana damuwar da ya tsinci kansa ciki bayan jin abin da ya faru.
"Amma kuma shi ne ba ka sanar da ni ba tuntuni?"
"Daddy ban ɗauka.."
"Idan dai har ba kare kanka za ka yi ba, ba na buƙatar jin wani abu daga bakinka." Daddy ya katse Gwani da faɗin hakan. Se ya kama bakinsa ya tsuke har se da Daddyn ya kai ƙarshe kafin ya amsa da
"A yi haƙuri Daddy." Ajiyar zuciya Daddy ya sauke kana yace
"Shi kenan, zan shigo an jima za mu yi magana."
"Allah Ya kai mu, Ya kawoka lafiya."
"Ameen." Daddy ya amsa da hakan yana ajje wayar.
.. A ɗaya ɓangaren kuwa yana ganin fitowar Lulun ya miƙe ya shige ɗakin. A kan kujera ya hangi Didin zaune. Ya fesar da iska daga bakinsa kafin yace bayan ya sauke ajiyar zuciya
"Thank God." Ya faɗa yana ƙarasawa cikin ɗakin.
"Awwwn, that's my baby gurl.." Ya ƙare yana neman waje ya zauna inda ya zamana yana kallanta ne tana kallansa. Ba ta san da shigowarsa ba se maganarsa kawai da ta ji. Abin da ya bata tsoro kenan, ta ɗaga kai ta kalle shi da sauri, se kuma ta sauke ajiyar zuciya dan har ga Allah ta tsorata.
"Kaina bisa wuyana." Ya faɗa yana ɗan marairaice fuska kamar ƙaramin yaron da ya yi laifi ya tuba. A hankali ya miƙe ya ƙarasa ƙasan kujerar da take kai ya ɗan leƙa fuskarta, cikin basarwa yace
"Kin ji sauƙi ne Babe? Ko dai in duba ki..?" Se kuma yanzun ya ƙare maganar yana ɗan kwaɓe fuska. Haɗa idanun da suka yi ne ya sanyata saurin ɗora kanta a kan kafaɗarsa da ta fi kusa da ita tana rufe idanunta cikin kunyar da ta ƙi sakinta. Fara alamun kukan shagwaɓar da ya ji ta soma yi ne still kuma kanta na kan kafaɗarsa ya sanya shi saurin faɗin
"Yi haƙuri na dena.. Uhmmm?" Ya faɗa yana ƙunshe dariyarsa. Gefe guda kuma yana jin daɗin yanda ya ganta, da alama ta ji daɗin jikinta. Hannu ya saka ya ɗago kan nata. Ya miƙe ya koma kan kujerar kusa da ita ya zauna. A hankali ya jata da niyyar kwantar da ita a jikinsa, ta zille tana maƙe kanta a kan kafaɗarta gami da ja baya. Dariya ta so ba shi, dan ya gane abin da take nufi. Dan kuwa da gaske tsoro take ji kar daga haka a sake maimaita abin da ya faru. Hannu ya sake miƙa mata yana motsa kansa alamar ta taho. Se ta sake kauda kai tana ma ƙoƙarin tashi gaba ɗaya. Da sauri ya riƙo hannunta yana faɗin
"Afuwan Sweerie.. Na yi alƙawarin babu abin da zan miki.. Runguma ce fa kawai." Ya ƙare maganar a marairaice yana langaɓar da kai. Ita dai har ga Allah ta gaji, so take ta sake jinta a kwance, da ma ta zauna ne saboda zuwan Lulu.
"Ni dai.." Ta faɗa tana fakar idanunsa da niyyar miƙewa. Ya yi saurin sanya hannunsa ya jawota, gaba ɗaya se gata ta dawo jikinsa babu tsammani. Ta yi kane-kane a kan faffaɗan ƙirjinsa. Hakan ne kuma ya ba shi damar gyara mata kwanciyar yanda za ta ji daɗi, ya rungumeta gam gam yanda ma ba za ta yi ko da yunƙurin tashi ba ne. Haka tana ji tana gani ta haƙura. Se kawai ta yi shiru tana sauraran bugun zuciyarsu dake fita kusan a tare. Ganin yanda ta ke ta ɗan gyara kwanciyar ne ya sanya shi faɗin
"Wani abu na miki ciwo ne?" Ya tambaya cike da kulawa. Runtse idanunta ta yi kamar yana kallanta. Ta girgiza kai ba tare da tace komai ba. Lura da abin da ta yi ne ya sanya shi faɗin
"Kin tabbatar? Idan akwai don Allah ki sanar da ni." Ya ƙare yana kallan tsakiyar kanta da ke kwance a ƙirjinsa. Nan ma jinjina kai kawai ta yi, ya cije lips ɗinsa kafin yace
"Idan fa ba ki buɗe baki ba zan duba ne in tabbatar.. Ni ban fahimci abin da kike nufi ba, lafiyarki kuma na da matuƙar muhimmanci a wajena." Jin ya ƙarasa maganar yana sassauta riƙon da ya mata ne ya sanyata saurin faɗin ba tare da ta shirya ba, dan ta san ba ƙaramin aikinsa ba ne ya aikata abin da ya yi niyya.
"Eh, na warke fa.." Ta ƙare tana turo baki kamar za ta fashe. Wata miskilar dariya ce ta ƙwace masa. Be ce komai ba se shafa sumar kansa da ya yi har lokacin murmushi ya ƙi barin fuskarsa. Tana jinsa lokacin da ya ɗauki hannayenta ya zagaya da su bayansa. Se kawai ta sake su, ta dai cigaba da kwanciya a jikin nasa.
"Idan fa ba ki yi abin da nake so ba toh ni zan.." Ya ƙare yana ƙoƙarin birkitota. Babu shiri ta yi saurin rungume shi. Ya lumshe idanunsa yana komawa ya baje a kan kujerar har lokacin idanunsa a lumshe. Cikin lokaci ƙanƙani wani daddaɗan bacci ya yi awon gaba da kowannensu.
.. A ranar kuwa kamar yanda Daddy ya alƙawarta se ga shi cikin asibitin. Se da ya je ya duba Abeey kafin suka dawo suka zauna dan yin magana da Gwani. Sake tattaunawa suka yi a kan rashin lafiyar Abeeyn kafin daga bisani Daddy yace
"Yanda na yanke, ina ganin tun da har da ma za su je Saudiyya, na kuma amince da ƙwarewar likitocin asibitin da na taɓa zuwa shekarun baya, se ku je a duba lafiyar Malam sosai. In Sha Allah za a dace.." Cikin na'am da maganar Daddyn Gwani ya amsa da
"Babu amfanin cigaba da zama da su.. sun ci amanarka Rankayadaɗe.." Daga nan ta shiga sanar da shi abubuwan da suka faru, da irin gwagwarmayar da suka sha wajen ganin sun ƙwato Areef ɗin daga halayyar da ya jefa kansa ciki. Da taimakon Ubangiji kuwa se ga shi ya dena ɗin. Hannu Daddy ya kai ya sauke hular kansa ya ajjeta a gefe.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel.." Abin da ya din ga maimaitawa kenan yana jin yanda ilahirin jikinsa ya yi mugun sanyi.
"Kar ka ɗaga hankalinka Yallaɓai.. Komai ya daidaita da izinin Ubangiji. Ban ma so bari ka sani ba saboda sanin halinka, dan dai ka nemi da ka sani ɗin ne ya sa na sanar da kai. Don Allah kar ka saka damuwa a ranka." Girgiza kai Daddy ya yi kafin ya sauke dogon numfashi. Ya yi murmushin yaƙe sannan yace
"Allah Ya kyauta.." Ya yi maganar yana ƙoƙarin miƙewa. Da sauri Mommah ta katse shi, ta hanyar faɗin
"A'ah don Allah.. Da na san haka ne ai da ban faɗa maka ba." Mommah ta faɗa yanayin fuskarta na sauyawa. Se ya koma ya zauna yana faɗin
"Ina tunanin abin da ya kamata na yi ne. Ashe yanzu duk yaddar da na ba su se da suka ci amanata? Me ye amfanin zuwansu kenan? Duk zaman nan da suka yi babu wanda ya taɓa buɗar baki yace ga abin da Areef ke yi. Se ga shi yanzu abin da nake ji.. Kaii!!" Ya ƙare yana dafe kansa.
"Ka yi haƙuri.. In Sha Allah komai ya wuce Uhmmm?" Ɗaga kansa ya yi kafin yace
"Allah Ya yadda.. Ya ƙara shirya mana su dukansu. Su kuma duk za su haɗu da ni ne." Ya ƙare maganar a ransa yana tunanin abin da ya kamata ya yi musu.
.. Lokacin da Gwani da Lulu suka isa gidan a kwance sosai suka tarar da Abeey, wanda har hakan ya so baiwa Gwani tsoro. Dan haka cikin ƙanƙanin lokaci ya ɗauki Abeeyn se asibiti. Babu ɓata lokaci aka ba shi taimakon gaggawa, aka kuma yi masa duk abin da ya dace. Kiran Daddy da ya gani cikin wayarsa shi ne abin da ya sanya shi komawa ya zauna. Ya ɗaga wayar yana karawa a kunnensa.
"Barka da wannan lokaci Daddy."
"Barka dai Son.. Ka na cikin gida ne?" Se da ya kalli Ummeey da Lulu ke kusa da ita kafin ya girgiza kai
"A'ah muna asibiti."
"Subhanallahi.. waye ba lafiya?" Daddy ya tambaya cike da mamaki.
"Abeey ne.." Ya bayar da amsar kansa na kallan ƙasan tiles ɗin asibitin.
"Ya ilahy! Da ma ba shi da lafiya ne?" Se da Gwani ya sauke ajiyar zuciya kafin yace
"Eh toh.. Daddy da ma dai yana fama da rashin lafiyar ne, ga kuma ciwon ƙoda.. Wani lokacin jikin kan motsa ba ma tare da kowa ya sani ba. Se dai a wannan karon abin ya kai shi ƙasa ne, se da ya kayar da shi."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!" Daddy ya faɗa muryarsa na bayyana damuwar da ya tsinci kansa ciki bayan jin abin da ya faru.
"Amma kuma shi ne ba ka sanar da ni ba tuntuni?"
"Daddy ban ɗauka.."
"Idan dai har ba kare kanka za ka yi ba, ba na buƙatar jin wani abu daga bakinka." Daddy ya katse Gwani da faɗin hakan. Se ya kama bakinsa ya tsuke har se da Daddyn ya kai ƙarshe kafin ya amsa da
"A yi haƙuri Daddy." Ajiyar zuciya Daddy ya sauke kana yace
"Shi kenan, zan shigo an jima za mu yi magana."
"Allah Ya kai mu, Ya kawoka lafiya."
"Ameen." Daddy ya amsa da hakan yana ajje wayar.
.. A ɗaya ɓangaren kuwa yana ganin fitowar Lulun ya miƙe ya shige ɗakin. A kan kujera ya hangi Didin zaune. Ya fesar da iska daga bakinsa kafin yace bayan ya sauke ajiyar zuciya
"Thank God." Ya faɗa yana ƙarasawa cikin ɗakin.
"Awwwn, that's my baby gurl.." Ya ƙare yana neman waje ya zauna inda ya zamana yana kallanta ne tana kallansa. Ba ta san da shigowarsa ba se maganarsa kawai da ta ji. Abin da ya bata tsoro kenan, ta ɗaga kai ta kalle shi da sauri, se kuma ta sauke ajiyar zuciya dan har ga Allah ta tsorata.
"Kaina bisa wuyana." Ya faɗa yana ɗan marairaice fuska kamar ƙaramin yaron da ya yi laifi ya tuba. A hankali ya miƙe ya ƙarasa ƙasan kujerar da take kai ya ɗan leƙa fuskarta, cikin basarwa yace
"Kin ji sauƙi ne Babe? Ko dai in duba ki..?" Se kuma yanzun ya ƙare maganar yana ɗan kwaɓe fuska. Haɗa idanun da suka yi ne ya sanyata saurin ɗora kanta a kan kafaɗarsa da ta fi kusa da ita tana rufe idanunta cikin kunyar da ta ƙi sakinta. Fara alamun kukan shagwaɓar da ya ji ta soma yi ne still kuma kanta na kan kafaɗarsa ya sanya shi saurin faɗin
"Yi haƙuri na dena.. Uhmmm?" Ya faɗa yana ƙunshe dariyarsa. Gefe guda kuma yana jin daɗin yanda ya ganta, da alama ta ji daɗin jikinta. Hannu ya saka ya ɗago kan nata. Ya miƙe ya koma kan kujerar kusa da ita ya zauna. A hankali ya jata da niyyar kwantar da ita a jikinsa, ta zille tana maƙe kanta a kan kafaɗarta gami da ja baya. Dariya ta so ba shi, dan ya gane abin da take nufi. Dan kuwa da gaske tsoro take ji kar daga haka a sake maimaita abin da ya faru. Hannu ya sake miƙa mata yana motsa kansa alamar ta taho. Se ta sake kauda kai tana ma ƙoƙarin tashi gaba ɗaya. Da sauri ya riƙo hannunta yana faɗin
"Afuwan Sweerie.. Na yi alƙawarin babu abin da zan miki.. Runguma ce fa kawai." Ya ƙare maganar a marairaice yana langaɓar da kai. Ita dai har ga Allah ta gaji, so take ta sake jinta a kwance, da ma ta zauna ne saboda zuwan Lulu.
"Ni dai.." Ta faɗa tana fakar idanunsa da niyyar miƙewa. Ya yi saurin sanya hannunsa ya jawota, gaba ɗaya se gata ta dawo jikinsa babu tsammani. Ta yi kane-kane a kan faffaɗan ƙirjinsa. Hakan ne kuma ya ba shi damar gyara mata kwanciyar yanda za ta ji daɗi, ya rungumeta gam gam yanda ma ba za ta yi ko da yunƙurin tashi ba ne. Haka tana ji tana gani ta haƙura. Se kawai ta yi shiru tana sauraran bugun zuciyarsu dake fita kusan a tare. Ganin yanda ta ke ta ɗan gyara kwanciyar ne ya sanya shi faɗin
"Wani abu na miki ciwo ne?" Ya tambaya cike da kulawa. Runtse idanunta ta yi kamar yana kallanta. Ta girgiza kai ba tare da tace komai ba. Lura da abin da ta yi ne ya sanya shi faɗin
"Kin tabbatar? Idan akwai don Allah ki sanar da ni." Ya ƙare yana kallan tsakiyar kanta da ke kwance a ƙirjinsa. Nan ma jinjina kai kawai ta yi, ya cije lips ɗinsa kafin yace
"Idan fa ba ki buɗe baki ba zan duba ne in tabbatar.. Ni ban fahimci abin da kike nufi ba, lafiyarki kuma na da matuƙar muhimmanci a wajena." Jin ya ƙarasa maganar yana sassauta riƙon da ya mata ne ya sanyata saurin faɗin ba tare da ta shirya ba, dan ta san ba ƙaramin aikinsa ba ne ya aikata abin da ya yi niyya.
"Eh, na warke fa.." Ta ƙare tana turo baki kamar za ta fashe. Wata miskilar dariya ce ta ƙwace masa. Be ce komai ba se shafa sumar kansa da ya yi har lokacin murmushi ya ƙi barin fuskarsa. Tana jinsa lokacin da ya ɗauki hannayenta ya zagaya da su bayansa. Se kawai ta sake su, ta dai cigaba da kwanciya a jikin nasa.
"Idan fa ba ki yi abin da nake so ba toh ni zan.." Ya ƙare yana ƙoƙarin birkitota. Babu shiri ta yi saurin rungume shi. Ya lumshe idanunsa yana komawa ya baje a kan kujerar har lokacin idanunsa a lumshe. Cikin lokaci ƙanƙani wani daddaɗan bacci ya yi awon gaba da kowannensu.
.. A ranar kuwa kamar yanda Daddy ya alƙawarta se ga shi cikin asibitin. Se da ya je ya duba Abeey kafin suka dawo suka zauna dan yin magana da Gwani. Sake tattaunawa suka yi a kan rashin lafiyar Abeeyn kafin daga bisani Daddy yace
"Yanda na yanke, ina ganin tun da har da ma za su je Saudiyya, na kuma amince da ƙwarewar likitocin asibitin da na taɓa zuwa shekarun baya, se ku je a duba lafiyar Malam sosai. In Sha Allah za a dace.." Cikin na'am da maganar Daddyn Gwani ya amsa da