← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 122

Sashe 44

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

"Plss.. mu je dai." Gaba ya yi ya wuce zuwa sashen Mom ɗin hannunsa riƙe da wayarsa yana dannawa. Ɗan dakatawa ya yi kafin ya kai ga ƙarasawa sashen Mom ɗin yana sake kallan cikin wayar tasa.

"Oh god.." ya faɗa yana kai hannunsa ya ɗan dafe goshinsa. Sam ya manta da maganar Hero se yanzun yake tunawa. Ya ja ƙaramin tsaki yana ɗan furzar da iska daga bakinsa. Se ya ƙara saurin tafiyarsa zuwa sashen Mom ɗin cike da fatan ta gama faɗa masa abin da za ta faɗa masa ya wuce inda yake da tabbacin ze sami Hero wanda tunda abin nan ya faru be sake bi ta kansa ba.

Kafin ya shiga palourn ya dakata, ya ja kujera ya zauna yana ɗan karkaɗa ƙafarsa. Daidai lokacin Mom ta iso. Se a lokacin sannan ya sauke ƙafar tasa yana kallanta. Neman waje ta yi ta zauna tana fuskantar shi. Cikin kwantar da murya tace

"Wai ka fara son yarinyar can ne?" Ta tambaya tana kafe shi da idanunta. Dan so take yau ɗin ta gano komai a wuce wajen, shi ya sa take bugar cikinsa. Kallan Mom ɗin kawai ya tsaya yana yi kamar wanda ya ji ta yi saɓo. Se can ya yi wani murmushi wanda ke matuƙar ƙawata fuskarsa.

"Shi ne maganar da ma?" Ya tambaya a nutse.

"A'ah.. so nake na ji dalilin da ya sa ka ɗauketa cikin motarka.." Numfashi ya sauke daidai lokacin da yake lumshe idanunsa, ya buɗe su kana yace

"Bari dai na faɗa miki yanda aka yi.. Daddy ne ya saka ni.. Daga nan babu wani abu" ya ƙare yana kallanta.

"Toh madallah.. Amma ka san wani abu?" Ta ɗan dakata a nan tana tunanin an ya kuwa ta fara yi masa maganar ya bar ƙasar kamar yanda ita ma za ta bari har ta dawo yanzu?

"Shi kenan ma kawai je ka.. Ina za ka je?" Ta fasa yin maganar bayan ta gama tsarawa a ranta ba yanzu ya kamata ta yi masa ba. Shafa sumar kansa ya yi kamar yanda marasa gaskiya ke yi yace lokacin da ya miƙe

"Babu.."

"Toh shi kenan.. duk lokacin da kake free dai ka zo mu yi hira ka san ba na son shigowa sashen nan.." ta ƙare tana ɗan yamutsa fuska.

"Ohk.." ya faɗa yana matsowa kusa da ita ya yi hugging nata sannan ya fice.

"Allah ya maka albarka.." ta faɗa tana binsa da kallo murmushi fall fuskarta. Har yau har gobe ta kalli Areef ɗin se ta ji farin cikin kasancewarsa ɗanta..

Bayan wajen minti 1 da fitarsa Mom ta sauke ajiyar zuciya sannan ta cigaba da takawa zuwa palournta. Tana zaune a ƙasan carpet a mugun takure kamar wadda wani abun ze kama. Se babbaza idanu kawai take yi cikin rashin sanin abin yi. Wani kallo Mom ta watsa mata tana sake ji har cikin ranta wannan yarinyar ba za ta taɓa zama sirikarta ba. Dan kuwa tun kallon farko ta ji ba ta mata ba, ban da ma tsanarta babu abin da take ji cikin zuciyarta. Ballantana kuma a kai ga ba ita ce ta yi wa Areef ɗin zaɓi ba, zaɓin mahaifinsa ce. Ita kuma ba ta ga abin da ze sanya ta amshi zaɓin Daddyn a matsayin zaɓinta ba, ko da kuwa yarinyar ta mata ne ballantana kuma ba ta mata ba. Wani banzan kallo Mom ɗin ke binta da shi lokacin da ta ida shiga cikin ɗakin. Se a lokacin sannan Didi ta san da zuwanta cikin ɗakin. Ta yi saurin yin ƙasa da kanta saboda yanda ƙirjinta ya buga lokacin da suka haɗa idanu.

"Tashi maza ki ji ni shashasha.." Mom ta faɗa a tsawace. Babu musu Didi ta tashi se dai har lokacin ba ta sake gangancin kallan Mom ba.

"Ki buɗe kunnanki da kyau ki ji ni.. Daga yau se yau, kar da wata ƙatuwa ko kuma wani yace miki ki shiga motar ɗana ki shigeta. Wannan motar ba an yi ta ne dan irinki ba a'ah.. ki kama kanki, idan ba haka ba zan ɗauki mummunan mataki a kanki. Zan kuma ƙarasa nuna miki wace ce ni, dan na ga har yanzu kin kasa fahimtar wace ce ni.. kin ji ni??" Jinjina kai Didi ta yi a hankali.

"Ki buɗe baki ki min magana shashasha.." Mom ta sake faɗa har wani huci take fiddawa.

"Eh na ji.." Didi ta faɗa a sanyaye.

"Toh ga hanya nan ɓace min da gani." Ta yi maganar tana nuna mata hanyar fita. Babu musu, da ma abin da take buƙata kenan, Didi ta ɗaga ƙafafunta ta fice daga ɗakin.

"Wawiyar yarinya.." Mom ta faɗi hakan bayan ta bi ta da wata harara..

... A ranar da aka sallami Lulu ranar Abba ya wakilta wasu suka je suka kai mata haɗaɗɗun kayanta na gani na faɗa wanda suka kasance sakk irin na Didi ne babu bambancin komai. Ba wani daɗewa suka yi a gidan ba, bayan sun gama shirya komai da taimakon Ummeey suka wuce gidan Alhaji Matawalle inda a can ɗin waje daban aka basu suka ajje kayan da niyyar duk lokacin da su Didin za su koma gidansu na su su kaɗai se a tafi mata da su. Saboda nan ɗin ko ina akwai furniture, akwai komai na buƙata. Se bayan da masu jeran suka tafi sannan Ummeey ta wuce asibiti suka taho tare da su Gwani da Lulun gida.

.. A ɗakin Ummeey suka sauka duk da kasancewar dare ne hakan be hana Ummeeyn saurin hura wuta ta ɗorawa Lulu ruwa dan ta samu ta yi wanka ba.

"Ki tashi ki je ki yi wanka za ki sake jin daɗin jikinki.." Ummeey ta faɗa da murmushi a kan fuskarta tana kallan Lulu.

"Toh.." Lulu ta faɗa tana miƙewa. Kai tsaye banɗakin tsakar gidan ta wuce bayan an kai mata kayanta. Ta yi wankan kuwa sosai ta shiryo sannan ta fito. A ɗakin Ummeeyn dai ta sake zama kamar yanda Ummeeyn ta mata umarni. Ba ta daɗe da zama ba Gwani ya shigo cikin ɗakin. Ta amsa sallamar da ya yi ƙasa_ƙasa sannan ta cigaba da zama kawai. Neman waje ya yi ya zauna yana danna wayarsa da alama wani abun yake dubawa me matuƙar amfani. Babu daɗewa Ummeey ta shigo cikin ɗakin ta nemi waje ta zauna.

"Afaaf ya kamata kuwa ki tashi ki je ɗaki ki ga kayan da aka kawo miki daga gidan.. Ɗazun nan aka zo aka miki jere cikin ɗakinki.." Ummeey ta ƙare tana murmushi cike da fatan Lulun ta saki jiki da ita kar ta ɗauketa a matsayin suruka. Kallanta Lulu ta yi duk da ta fahimci abin da Ummeeyn ke nufi amma kuma se hankalinta ya tafi wajen tunanin makomarta. Ta tabbata dai ba za bar gidan ba kenan, tun da ga shi har da yi mata jere cikin ɗakin Gwanin. Se kawai ta yi murmushin yaƙe tana faɗin

"Toh.." Daga haka ta miƙe.

"Toh se da safe kenan?" Ummeey ta tambaya.

"Ehh Ummeey.." ta yi ƙarfin halin faɗin sunan Ummeeyn. Wanda hakan ba ƙaramin farantawa Ummeeyn ya yi ba. Har se da ta yi murmushi sannan ta amsa da

"Toh Allah ya tashe mu lafiya.." da "Ameen" ta amsa tana ficewa daga ɗakin. Ummeey ta bita da kallo ganin daga Gwanin har ita Lulun babu wanda yace da ɗan uwansa uffan. Kar dai har yanzun a haka rayuwar tasu take babu wani cigaba? Ta tambayi kanta.

"Affan.."

"Na'am Ummeey." Ya amsa yana ɗaga kansa daga kan wayar ya kalleta.

"Ba ka jin bacci ne?"

"A'ah, akwai wani aiki ne da zan ƙarasa.."

"Toh Allah ya taimaka.." Ummeey ta faɗa tana sauke numfashi. Cikin zuciyarta tana addu'a a kan Gwanin da kuma Lulun.
Chapter 44 · 0% Book details