Sashe 10
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
... A ɗaya ɓangaren kuwa shimfiɗa bargon ya yi, ya jefar da pillow, kana ya ɗan kishingiɗa a kai. Idanunsa ya ɗan lumshe kaɗan, duk da ya san shima ya yaudari kansa in dai bacci ne ba zuwar masa ze yi ba. Haka dai ya cigaba da zaman, hannunsa ɗore a kansa. Ya daɗe zaune a wajen, babu abin da kwanyarsa ke yi se tunani. Be ankara ba se ji ya yi ana kiran Assalatu. Buɗe idanunsa da suka ɗan lumshe ya yi. A hankali ya miƙe zaune, se kawai ya miƙe kai tsaye ya nufi toilet. Ko kallan inda gadon yake be yi ba. Kai tsaye wanka ya yi, ya ɗauro alwala sannan ya fito. Shiryawa ya yi kamar yanda shigarsa take ta koyaushe. Cikin ƙanƙanin lokaci ya fito a Gwaninsa sakk, ya yi matuƙar kyau kamar wanda ya shafe tsawon awanni yana shiryawa. Se a lokacin ya ɗan dakata, ya kalli kan gadon. Tana kanannaɗe cikin zanin gadon, kwata kwata ba a iya ganinta saboda yanda ta cukwuikuye zanin gadon. A hankali ya ɗan danna wayarsa, ya kalli ƙarfe nawa. Se ya maidata aljihu kawai ya fice daga ɗakin. Be daɗe da fita ba ɓarawon baccin da ya saceta ya soma sakinta. Se ta shiga buɗe idanunta a hankali. Firgigit! Ta zabura gami da miƙewa zaune tana kallan inda take. Ya aka yi ta yi bacci a cikin gidan nan? Me yasa ba ta cigaba da jiran safiya ta yi har Mami ta zo ba? Ture zanin gadon ta yi a fusace, kamar shi ne ya mata laifi. Ta ja dogon tsaki tana jin ɓacin rai na taso mata. Hijabin da ta lalubo shi ta sake gyara zamansa, ta sake kallan ɗakin tana cigaba da yamutse fuska. Ƙofar da ta fi mata kama da banɗaki nan ta nufa. Tana zuwa ta tura ƙofar banɗakin da hannu ɗaya, ita a lallai dole ƙyanƙyami take ji. Bin toilet ɗin ta yi da kallo, yanda yake a wanke tass kamar ka lashe. Babu abin da ke tashi se ƙamshin sabulun da ya yi wanka da shi yanzun. Sam sam babu alamar datti ko na wani abun makamancinsa a cikin banɗakin, dan kuwa mamallakinsa me tsafta ne, kuma mara son ƙazanta. Duk kuwa da yanda toilet ɗin yake ƙal ƙal hakan be hanata sake taɓe fuska ba. Ta shiga ciki duk a ɗarare kamar wadda ke kan tutu. Wanka ta yi da sabulu kawai, shi ma ba dan ta so ba, se dan kawai ba ta so ne Mami ta zo ta sameta yaɓe_yaɓe. Kuma har su koma gida ma babu wanka, shi yasa ta gwammace ta yi anan ɗin. Ko da ta fito babu abin da ta shafa a jikinta, se maida kayanta da ta yi, ta sake saka hijab ɗinta, kana ta tayar da Sallah. Se wajen ƙarfe 7 ya dawo gidan. Kai tsaye ɗakin ya nufa dan tabbatar da tashinta. Se ya yi tozali da ita a bakin ƙofa kamar yanda ya sameta jiya. Be bi ta kanta ba kawai ya rufe ƙofar, ya koma ɗakin Ummeey kamar yanda ya saba. Se da suka gaisa sannan Ummeey tace
"Ina ɗiyar tawa? Ban ganta ba.. Ina fata dai ta tashi lafiya.." Murmushin yaƙe kawai ya yi kafin ya amsa da
"Alhamdulillah.."
"Madallah.. So nake yau na ɗora abun kari da wuri, saboda yarinyar nan. Ka san wasu sun saba da karyawa da wuri, ka da na je itama wajen ɗiyar tawa haka ne, a zo kuma a yi abin kunya.." Cike da tausayin Ummeeyn, da kuma tuna hali irin na Lulu ya girgiza kai. Da Ummeey ta san wace ce Lulun da ta rabu da ita. Ta watsar da ita a gefe tun kafin ta nuna mata wace ce ita. Da ta manta da zancenta ma kwata kwata duk da suna zaune cikin gida ɗaya.
"Bari na duba miki ita Ummeey.."
"Aikam dai duba min.. Idan kuma bacci take yi ka ƙyaleta.. Na san idan ta tashi za ta fito.." Da "toh" ya amsa yana wucewa ɗakin nasa.
... "Wallahi na yi iya bakin ƙoƙarina amma sun hana ni shiga cikin gidan nan. Wai tsaya! Ko a fuska ma na yi kama da ɗan iska ne?" Hero ya faɗa yana kallan Ladi. Dariya Abida dake gefe ta sheƙe da ita jin maganar Hero ɗin. Ita kuwa Ladi ba wannan ne a gabanta ba, dan haka tace
"Duk wata dabara ka gwada?" Ta tambaya fuska a dame.
"Wallahi na gwada.. Ke kaina gaba ɗaya fa ya kulle, ban san me mutanen ke nufi da mu ba.."
"Duk kai ne ka ja wallahi Hero.."
"Daga yau wallahi duk lokacin da kika sake cewa ni na ja, toh na cire hannuna a kan komai, se ki ƙarasa da kanki.." Hero ya faɗa a fusace.
"Ka yi haƙuri. Raina ne a ɓace.." Ladi ta faɗa. Se ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ɗora da
"Abin da ya rage kawai mu tura Abida gidansu yarinyar, na san za ta samo mana labari a kan abin da ke faruwa. Wallahi Hero ba zaka gane bane, kullum kwanan duniya ji nake ana ƙaramin ƙaunar jikin yarinyar nan.." Ladi ta faɗa tana lumshe ƙananan idanunta.
"Shi kenan, mu gwada hakan.." Hero ya faɗa, dan gaba ɗaya kansa ya kulle, ya ma rasa abin da ya kamata ya yi.
... "Toh mu dai Yaya za mu yi gaba.. Allah ya sa an yi komai a sa'a.." Mami ta faɗa sanda ta ga Abban na ƙoƙarin fita daga gidan. Juyawa ya yi ya kalleta yace
"Har za ki tafi..?"
"Ehh, amma dai zan biya ta gidan Afaaf ne, dan tun jiya na barta tana ta kuka, ina so ne na je na rarrasheta, ka san yarinyar nan fa dama Yaya se da rarrashi.." Mami ta ƙare tana murmushi, ita a lallai dole so take Abba ya yarda da abin da ta faɗa. Jinjina kai Abba ya yi sannan yace
"Ehh hakan ma na da kyau. Se dai yana da kyau duk yarinyar da ta yi aure ta san fa auren ta yi. Dan haka ya kamata itama Afaaf ta san yanzu ta girma ta yi aure, gwara ta fara sabawa tun yanzu. Dan haka ina ganin ba se kin je ba. A barta idan ta kwana biyu se a je a duba lafiyarta, amma banda yanzu.." Tunda Abban ya fara magana se ta tsaya sororo tana kallansa kamar wanda ya yi saɓo. Cikin basar da zancen nasa tace
"Amma Yaya Afaaf fa yarinya ce ƙarama.."
"Ita kuma Afrah fa? Dukkansu yara ne, amma idan basu san sun girma ba yanzu se yaushe? Kin ga shiga maza ki ɗauko kayan ki ki zo mu fita se na sauke ki a gida. Sannan kar kuma na ji labarin kin je a kwanakin nan.. Ke fa kamar uwa kike a wajen Afaaf. Ko ba ma wannan ba, ni dai nace a barsu dukansu su fara sabawa kafin a soma ziyartarsu.." Shiru Mami ta yi saboda yadda maganar Abban ta ɓata mata rai. Ya riga ya san halin Mamin dama, dan haka be jira amsarta ba yace
"Ki yi da hanzari, ina jiranki.." Daga haka ya fice daga ɗakin. Binsa ta yi da kallo tana huci kamar wadda ta yi ko take shirin yin dambe. Kawai se ta koma ta zauna a kan kujerar bayanta har lokacin ta gaza furta komai saboda yadda ranta ya ɓaci a kan yayan nata. Da sallama ta shigo cikin ɗakin cike da fatan ganin Lulu ko Didi cikin ɗakin. Se dai babu ma wanda ya amsa mata sallamar, se Mami kawai da ta hango zaune kan kujera, babu ma alamar ta san da shigowar wata halitta cikin ɗakin. Se ta shiga ƙarasawa inda Mamin take, da farko ma ta ɗauka Amminsu Lulu ce, se kuma da ta kusa ƙarasawa ta lura da ba ita bace.
"Ina wuni?" Abida ta faɗa tana kallan Mami. Takaicin maganar Abba ya sanya Mami juyawa ta watsawa Abida wani kallo kafin tace
"Lafiya malama?" Dan ba ta san ma da shigowar Abidar ba, se maganarta kawai ta ji.
"Don Allah wajen Afaaf na zo.." Kamar ba za ta tanka ba se kuma tace
"An yi aurensu.." daga haka ta ɗauki wayarta dake kusa da ita ta yi cikin ɗakin da suke dan ɗakko kayanta da ta gama haɗawa. Cike da mamaki Abida tace
"Aure kuma?" Ganin Mami na ƙoƙarin barinta a wajen ba tare da jin tabbacin abin da ta faɗa ba, ya sanya ta saurin yin gaba, ta sha gaban Mami tace jiki na rawa
"Aure kuma don Allah..?" Dakatawa Mami ta yi tana bin Abidar da kallo irin na tuhuma. Se da ta gyara tsayuwarta sannan tace
"Wace ce ke?" Ta tambaya cikin tsare gida. Cikin mazewa da yanayin yanda ta shiga shock ta gyara tsayuwarta tana ƙaƙalo murmushi tace
"Uhmm.. ƙawar Afaaf ce fa sosai.." Taɓe baki Mami ta yi kana tace
"Toh ta yi aure.." Daga haka ta yi gaba ta bar Abida a tsaye da ta saki barandar laɓɓa, dan saboda tsabar mamaki ta kasa ko da motsawa ne ballantana ta fita daga ɗakin..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO29*
___Ta kai wajen minti ɗaya a tsayen cikin rashin sanin abin yi. Da dai ta ga babu abin da za ta sake yi cikin gidan, babu kuma wanda ya fito, se ta ja tsummar ƙafafunta ta fice daga ɗakin. Tun kafin ta ƙarasa su Hero suka hangota. Gaba ɗaya idanunsu na kanta, musamman Ladi da ta ƙagu kawai ta ji abin da ke faruwa. Daidai sanda ta iso inda suke ta sauke ajiyar zuciya. Cikin ƙaguwa da son jin wani abu daga bakin Abidan Ladi tace
"Me ya faru? Ki yi sauri ki faɗa mana.."
"An yi aurenta wai.." ta faɗa a sare.
"An yi aurenta kuma? Kamar yaya?" Ladi ta faɗa tana kallanta cike da mamaki.
"Wallahi haka aka ce min." Tsayawa Hero ya yi yana kallan Abidar kamar me son gano gaskiyar abin da take faɗa.
"Ina ɗiyar tawa? Ban ganta ba.. Ina fata dai ta tashi lafiya.." Murmushin yaƙe kawai ya yi kafin ya amsa da
"Alhamdulillah.."
"Madallah.. So nake yau na ɗora abun kari da wuri, saboda yarinyar nan. Ka san wasu sun saba da karyawa da wuri, ka da na je itama wajen ɗiyar tawa haka ne, a zo kuma a yi abin kunya.." Cike da tausayin Ummeeyn, da kuma tuna hali irin na Lulu ya girgiza kai. Da Ummeey ta san wace ce Lulun da ta rabu da ita. Ta watsar da ita a gefe tun kafin ta nuna mata wace ce ita. Da ta manta da zancenta ma kwata kwata duk da suna zaune cikin gida ɗaya.
"Bari na duba miki ita Ummeey.."
"Aikam dai duba min.. Idan kuma bacci take yi ka ƙyaleta.. Na san idan ta tashi za ta fito.." Da "toh" ya amsa yana wucewa ɗakin nasa.
... "Wallahi na yi iya bakin ƙoƙarina amma sun hana ni shiga cikin gidan nan. Wai tsaya! Ko a fuska ma na yi kama da ɗan iska ne?" Hero ya faɗa yana kallan Ladi. Dariya Abida dake gefe ta sheƙe da ita jin maganar Hero ɗin. Ita kuwa Ladi ba wannan ne a gabanta ba, dan haka tace
"Duk wata dabara ka gwada?" Ta tambaya fuska a dame.
"Wallahi na gwada.. Ke kaina gaba ɗaya fa ya kulle, ban san me mutanen ke nufi da mu ba.."
"Duk kai ne ka ja wallahi Hero.."
"Daga yau wallahi duk lokacin da kika sake cewa ni na ja, toh na cire hannuna a kan komai, se ki ƙarasa da kanki.." Hero ya faɗa a fusace.
"Ka yi haƙuri. Raina ne a ɓace.." Ladi ta faɗa. Se ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ɗora da
"Abin da ya rage kawai mu tura Abida gidansu yarinyar, na san za ta samo mana labari a kan abin da ke faruwa. Wallahi Hero ba zaka gane bane, kullum kwanan duniya ji nake ana ƙaramin ƙaunar jikin yarinyar nan.." Ladi ta faɗa tana lumshe ƙananan idanunta.
"Shi kenan, mu gwada hakan.." Hero ya faɗa, dan gaba ɗaya kansa ya kulle, ya ma rasa abin da ya kamata ya yi.
... "Toh mu dai Yaya za mu yi gaba.. Allah ya sa an yi komai a sa'a.." Mami ta faɗa sanda ta ga Abban na ƙoƙarin fita daga gidan. Juyawa ya yi ya kalleta yace
"Har za ki tafi..?"
"Ehh, amma dai zan biya ta gidan Afaaf ne, dan tun jiya na barta tana ta kuka, ina so ne na je na rarrasheta, ka san yarinyar nan fa dama Yaya se da rarrashi.." Mami ta ƙare tana murmushi, ita a lallai dole so take Abba ya yarda da abin da ta faɗa. Jinjina kai Abba ya yi sannan yace
"Ehh hakan ma na da kyau. Se dai yana da kyau duk yarinyar da ta yi aure ta san fa auren ta yi. Dan haka ya kamata itama Afaaf ta san yanzu ta girma ta yi aure, gwara ta fara sabawa tun yanzu. Dan haka ina ganin ba se kin je ba. A barta idan ta kwana biyu se a je a duba lafiyarta, amma banda yanzu.." Tunda Abban ya fara magana se ta tsaya sororo tana kallansa kamar wanda ya yi saɓo. Cikin basar da zancen nasa tace
"Amma Yaya Afaaf fa yarinya ce ƙarama.."
"Ita kuma Afrah fa? Dukkansu yara ne, amma idan basu san sun girma ba yanzu se yaushe? Kin ga shiga maza ki ɗauko kayan ki ki zo mu fita se na sauke ki a gida. Sannan kar kuma na ji labarin kin je a kwanakin nan.. Ke fa kamar uwa kike a wajen Afaaf. Ko ba ma wannan ba, ni dai nace a barsu dukansu su fara sabawa kafin a soma ziyartarsu.." Shiru Mami ta yi saboda yadda maganar Abban ta ɓata mata rai. Ya riga ya san halin Mamin dama, dan haka be jira amsarta ba yace
"Ki yi da hanzari, ina jiranki.." Daga haka ya fice daga ɗakin. Binsa ta yi da kallo tana huci kamar wadda ta yi ko take shirin yin dambe. Kawai se ta koma ta zauna a kan kujerar bayanta har lokacin ta gaza furta komai saboda yadda ranta ya ɓaci a kan yayan nata. Da sallama ta shigo cikin ɗakin cike da fatan ganin Lulu ko Didi cikin ɗakin. Se dai babu ma wanda ya amsa mata sallamar, se Mami kawai da ta hango zaune kan kujera, babu ma alamar ta san da shigowar wata halitta cikin ɗakin. Se ta shiga ƙarasawa inda Mamin take, da farko ma ta ɗauka Amminsu Lulu ce, se kuma da ta kusa ƙarasawa ta lura da ba ita bace.
"Ina wuni?" Abida ta faɗa tana kallan Mami. Takaicin maganar Abba ya sanya Mami juyawa ta watsawa Abida wani kallo kafin tace
"Lafiya malama?" Dan ba ta san ma da shigowar Abidar ba, se maganarta kawai ta ji.
"Don Allah wajen Afaaf na zo.." Kamar ba za ta tanka ba se kuma tace
"An yi aurensu.." daga haka ta ɗauki wayarta dake kusa da ita ta yi cikin ɗakin da suke dan ɗakko kayanta da ta gama haɗawa. Cike da mamaki Abida tace
"Aure kuma?" Ganin Mami na ƙoƙarin barinta a wajen ba tare da jin tabbacin abin da ta faɗa ba, ya sanya ta saurin yin gaba, ta sha gaban Mami tace jiki na rawa
"Aure kuma don Allah..?" Dakatawa Mami ta yi tana bin Abidar da kallo irin na tuhuma. Se da ta gyara tsayuwarta sannan tace
"Wace ce ke?" Ta tambaya cikin tsare gida. Cikin mazewa da yanayin yanda ta shiga shock ta gyara tsayuwarta tana ƙaƙalo murmushi tace
"Uhmm.. ƙawar Afaaf ce fa sosai.." Taɓe baki Mami ta yi kana tace
"Toh ta yi aure.." Daga haka ta yi gaba ta bar Abida a tsaye da ta saki barandar laɓɓa, dan saboda tsabar mamaki ta kasa ko da motsawa ne ballantana ta fita daga ɗakin..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO29*
___Ta kai wajen minti ɗaya a tsayen cikin rashin sanin abin yi. Da dai ta ga babu abin da za ta sake yi cikin gidan, babu kuma wanda ya fito, se ta ja tsummar ƙafafunta ta fice daga ɗakin. Tun kafin ta ƙarasa su Hero suka hangota. Gaba ɗaya idanunsu na kanta, musamman Ladi da ta ƙagu kawai ta ji abin da ke faruwa. Daidai sanda ta iso inda suke ta sauke ajiyar zuciya. Cikin ƙaguwa da son jin wani abu daga bakin Abidan Ladi tace
"Me ya faru? Ki yi sauri ki faɗa mana.."
"An yi aurenta wai.." ta faɗa a sare.
"An yi aurenta kuma? Kamar yaya?" Ladi ta faɗa tana kallanta cike da mamaki.
"Wallahi haka aka ce min." Tsayawa Hero ya yi yana kallan Abidar kamar me son gano gaskiyar abin da take faɗa.