← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 122

Sashe 19

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Me ya faru?" Duk da ba ta san da wanzuwarsa ba, amma jin an janye mata hannu ya sanyata fizgewa da ƙarfi tana mayarwa kan cikinta. Se ta maida kanta kan katifar ta kifa shi tana cigaba da kukanta gami da rirriƙe ciki kamar me wanke kaya. Iska ya fesar yana ɗan lumshe idanunsa. Dan har cikin kansa yake jin wannan kukan. Hakan ne ya sanya shi kai hannunsa saman kanta ya juyo da fuskarta, kafin a hankali ya ɗora kan nata a kan ƙafarsa. Se ya ɗauki idanunsa ya ɗora a kan fuskar tata, yana shirin cewa wani abu ta fara ƙoƙarin miƙewa duk da har lokacin ba ta fahimci a inda take ba. Ɗan haɗe face ɗinsa ya yi kafin ya sake maimaita tambayar da ya mata ɗazun. Se dai har yanzun ma babu amsa, se cigaba da kukan nata dai ta yi. Kansa ya matsar dab da fuskarta, ya shiga hura mata iska a kan idanunta. Se ta yi saurin lumshe su lokaci ɗaya kukan na tsayawa cakk. Kafin ta cigaba kuma se jin muryarsa ta yi yana faɗin

"Keee!! Ki nutsu.. Me yake damunki?" ya yi maganar a saitin kunnenta kamar me raɗa, se dai har lokacin fuskarsa na nan a yanda take. Jin muryarsa da ta yi ne ya sanyata soma fahimtar a inda take, a ina kuma ta ji muryarsa. Hakan ne ya sanyata yunƙurawa dan miƙewa, daidai lokacin da cikinta ya yi wata muguwar murɗawa, ba ta san sanda ta koma kan ƙafar tasa ba cikin kuka tace muryarta na sarƙewa

"Cikina.. Cikina ze cire.." Ta yi maganar tana rirriƙe shi da ƙarfi lokaci ɗaya tana fashewa da wani marayan kuka..

Pls kar a tambaye ni dalilin da ya sa jiya aka ji ni shiru, ni kaɗae na san abin da nake ji.😭 Na yi rabin typing na ajje shi a email, ina ta saurin na je na ɗauko shi na haɗa na muku posting. Na duba na neme shi na rasa, ban san yanda aka yi hakan ta faru ba. Se da na taushi kaina na sake maimaitawa.

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO33*

___ Se kuma murɗawar ta tsaya, hakan ne ya sanyata sakinsa a hargitse ta miƙe da sauri ƙirjinta na bugawa. Kawai se ta fashe da kuka tana zubewa a wajen tunawa da ta yi yanda ta riƙe shi, shi kuma har da riƙota.

"Ɗan iska kawai.." ta faɗa a kan laɓɓanta tana cigaba da kukan durƙushe a ƙasa. Binta ya yi da kallo a ransa yana tunanin ko dai tana da wasu nau'i ne na iskokai? Se dai kafin ma ya ida tunanin da yake cikin nata ya sake murɗawa, da ta sake sakin wata ƙara tana bajewa a wajen tana kuka kamar ranta ze fita. Yanzu kam fargabar da ya ji har tafi ta ɗazu. Se kawai ya miƙe ya sakko daga kan gadon ya sake komawa inda take. Ya tattare girar sama da ta ƙasa sannan ya saka hannu ya ɗagota gaba ɗayanta. Gudun ka da ma ta masa gardama ya sanya shi shigar da ita cikin jikinsa. Jin abin da ya mata ne ya sanyata soma fiffizgewa, tana ƙara sautin kukanta, amma be bi ta kanta ba, se ma saka hannu da ya yi ya ɗage hijab ɗinta da yake har wajen gwuiwarta, ya maida shi saman cikinta. Duk da yanda take cigaba da fizgewa tana wani marayan kuka saboda yanda muryarta ta soma dashewa hakan be dame shi ba. Se saka hannunsa da ya yi ya ɗage rigar daga kan cikinta zuwa sama. A hankali kuma ya kai tattausan hannunsa kan farin cikinta. Kamar wata wutar lantarki me ja haka dukansu suka ji lokacin da hannunsa ya sauka a kan fatar cikinta. Ita Lulu suma ne kawai ba ta yi ba saboda tsoron da ta ji ya shigeta, yayin da Gwani se da bugun zuciyarsa ya ƙaru, ya koma fita da sauri da sauri, idanunsa a ɗan lumshe kamar me jin bacci. Wani yunƙurawa ta yi dan miƙewa daga jikinsa amma ina ya mata tsatstsauran riƙo. Se kawai ta shiga kai masa cizo ko za ta samu ya saketa. Shi kam ko kulata be yi ba, se matsa cikinta da ya yi da hannunsa. Ya ɗan taɓa gefe shi ma sannan ya yi saurin janye hannunsa yana janyo rigar da ya ɗage ya maidata yanda take. Sakinta ya yi ya miƙe a nutse yana ɗan sake buɗe idanunsa sosai, ya ƙarasa drawer ɗin mirror. Fashewa ta yi da kuka sanda ya saketa, se ta ja hijab ɗinta ta lulluɓe ilahirin jikinta dake wata irin karkarwa kamar ana kaɗa ganga. Ta cure waje ɗaya kanta kife a kan cinyarta tana kuka me cin rai. Duk da yanda cikinta ke juyawa hakan be dameta ba yanzu, wani tsoron gwanin ne ya kamata. Ba ta ankara ba se jin muryarsa ta yi dab da ita yace

"Karɓi ki sha.." ya yi maganar fuskar nan babu annuri ko kaɗan. Sauke kanta ta yi ƙasa tana sake matsawa baya. Ganin yana ƙoƙarin miƙewa ne ya sanyata buɗe bakinta da ƙyar cikin raunanniyar murya kamar ba Lulu ba ta soma faɗin

"Kar ka matso kusa da ni don Allah.. ka rabu da ni.. ka rabu da ni don Allah.." Da mamaki ya ɗan kalleta, se ya ji kamar ba Lulun ba. Ashe dai rashin lafiya na chanja mara kunyar mutum? Se da ya lumshe idanunsa sannan ya sake takawa ya ƙara rage tazarar dake tsakaninsu.

"Ki karɓa ki sha ko kuma na ba ki da kaina.."

"Ni ka ƙyale ni.. Allah ka ƙyale ni.." yanzun ma ta faɗa tana sake fashewa da sabon kuka. Ajiyar zuciya ya sauke, ganin za ta ɓata masa lokaci, ga shi so yake ya fita ya sama mata abin da za ta ci, ya sanya shi yin shahada ya sake riƙeta cikin jikinsa duk da yanda take fizgewa ya ba ta ruwan. Haka tana kukan tana komai se da ya tabbatar ta shanye tass duk da dama kaɗan ne sannan ya saketa. Ya miƙe ya bar wajen ma gaba ɗaya. Kawai bajewa ta yi a wajen cikin rashin sanin abin yi tana juya kanta wani dogon kuka na taho mata. Ta ɗauki tsawon sakanni, kafin kukan ya fito fili, ta kuwa shiga rera shi tana ji kamar ta mutu dan baƙin ciki. Farar fuskar nan ta haɗe ta yi jajur.

... A karo na biyu kiran ya sake shigowa cikin wayar, ya juya daga inda yake zaune yana saka haɗɗaɗen takalminsa. Iska ya fesar daga bakinsa a ransa yana tunanin wanda ya masa kira har 2 a jere haka. Daga inda yake zaune ya miƙa hannunsa zuwa inda wayar take, ya ɗaukota yana kallan wata hargitsatstsiyar number dake yawo a saman wayar tasa. Dogon tsaki ya ja yana jefar da wayar a gefensa ransa a ɓace saboda ganin da ya yi sabuwar number ce ma ke kiransa. Shi kuma da ma ba ya ɗaukar number da be sani ba. Se da ya gama shiryawarsa sannan ya miƙe lokacin da ya gama fitowa a Bad Man ɗinsa, ya yi matuƙar kyau, cikin shigar ƙananan kayan da a kodayaushe suke ɗaukar jikinsa. Sam be taɓa kawowa cewar Hero ke kiransa a wannan lokacin ba, dan kuwa ya daɗe da goge numbersa daga wayarsa kamar yanda ya goge shi daga cikin rayuwarsa. Daidai lokacin da yake ƙoƙarin saka wayar cikin aljihu ta ɗauki ruri, ya yi tunanin ko number ɗazu ke kira, dan haka a matuƙar fusace ya juyo da wayar, se ganin sunan Kaseem na yawo a kan wayar tasa ya yi. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana ɗaga wayar ya kara a kunnensa.

"Bro ka shirya ne?"

"Zuwa ina fa?" Ya tambaya yana ɗan ƙanƙance idanunsa.

"Ka na nufin ka ce har ka manta? Amma dai ai ka san za mu fita koh?" Kaseem ya tambaya yana mamakin yanda Bad Man ɗin ba ya ɗaukar komai serious. Kafin yace komai ya ɗora da faɗin

"Plss ina jiranka.. Ka yi ƙoƙari ka fito ko don farin cikin Daddy.."

"Ok.." ya faɗa a taƙaice yana datse kiran. Ya sake lumshe idanunsa kafin ya buɗe su. Sam be so bin Kaseem ɗin wani waje ba, shiryawar nan da ya yi ze ɗan fita ne ya samowa kansa wasu abubuwan charge. Se dai da ma yana tunanin yanda ze shigo da su, ko kuma yanda ze fita ba tare da samun wani tsaiko ba bayan Daddy na nan. Kai tsaye compound ɗin ya wuce hannunsa ɗaya na cikin aljihun wandonsa ya ƙarasa inda motar Kaseem take. Tun kafin ya ƙaraso dama ya riga ya buɗe masa ƙofar, dan haka yana zuwa kawai shiga ya yi ya nemi waje ya zauna.

"Mu tafi?" Kaseem ya tambaya yana kallan Bad Man.

"Yeap.." ya amsa yana fito da wayarsa. Babu ɓata lokaci Kaseem ya soma driving. Kaseem ɗin gwani ne wajen hira, se dai a wannan karon se ya kasance tafiyar tasu ta zama wata lami, musamman da ya kasance har yanzu Kaseem ɗin be koma ainahin Kaseem ɗinsa ba, tun lokacin da ya rasa Didi. Mutane da dama sun sha tambayarsa dalilin chanjawar tasa amma se dai yace babu komai. Areef da shi kansa wani na arziƙi ne me kula da wasu, da ze yi noticing chanjawar Kaseem ɗin. Amma da yake be iya damuwa da damuwar wasu ba ya sanya tun kallo ɗaya da ya yi wa Kaseem ɗin be sake ba, ballantana a kai ga tambayar abin da ke damunsa. Haka suka cigaba da tafiya babu me cewa da wani uffan. Se da Kaseem ya gaji sannan ya ɗan shiga jan shi da hira sama sama. Da yake akwai sabo a tsakaninsu ya sanya ya ɗan saki jiki suka taɓa hira babu laifi.

Da wannan damar ya yi amfani ya siyi kayan mayensa da na shaƙa, ya san yanda ya yi ya shigar dasu gida ba tare da kowa ya gani ba.

... Idar da sallahrta kenan, ta miƙe tana ninke dadduma Baba Atine ta shigo da sallama. Amsawa ta yi da murmushi a kan fuskarta. Baba Atine ta ƙaraso tana faɗin

"Sannu ɗiyata.. Kin idar da sallahr?" Ta tambaya ita ma tana murmushi.

"Ehh na idar.."
Chapter 19 · 0% Book details