Sashe 59
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"A'ah ko kaɗan ba ka yi ɓatan kai ba.. Ni ce Ladi.. shigo." Ta sake yin gaba tana cigaba da jijjiga jikinta. Hannunsa ya dafe kan Bluetooth ɗin dake kunnensa a hankali yace
"Ku shigo kawai.." Daga haka ya sauke hannunsa. Kafin ƙiftawa da Bismillah se ga en sandan nan sun shigo sanye cikin uniform ɗinsu kowannensu babu annuri a kan fuskarsa.
"Ku kama duk wanda kuka gani.. Yau za a rufe gidan nan.." Ya sake bayar da umarni ta cikin waya. Cikin sakannin da basu wuce 3 ba en sandan suka fara aikinsu. Juyowar da Ladi za ta yi saboda jin da ta yi har lokacin mutumin be taho ba ya yi daidai da lokacin da mutanen cikin gidan suka soma ihu saboda kamasu da aka fara yi. Tuni kowa ya fara neman hanyar tserewa. Ya yin da en sandan suka ƙi basu kowacce dama. Suka dinga cafkesu suna zuwa su jefa su cikin motar nan. Tuni waɗanda ke cikin ɗaki maza da mata suka soma fitowa wasu da gajerun wanduna wasu da ɗaurin ƙirji. Kowa kuma hanyar gujewa en sandan yake nema. Sake buɗe idanunta Ladi ta yi dan sake tabbatar da abin da ke faruwa, dan ta ɗauka mafarki ne. Dan kuwa ba yau ne rana ta farko da ta soma irin mafarkin nan ba. Se dai da yake ta san hakan ba me yiwuwa ba ne ya sanya ba ta damuwa.
"Kamata.." Shi ne abin da mutumin nan ya faɗa yana kallan Ladi. Babu ɓata lokaci er sandar ta riƙota. Se a lokacin sannan ta fara tunanin to ko dai ba mafarki take yi ba. Jin an fara janta ne ya sanyata buɗe baki da sauri tace
"Ke meye haka ne? Wai ma me kuke min haka ne a cikin gida?" Ta tambaya tana jin wani bugun zuciya.
"Wuce kawai.." Ya sake bata umarni. Se ta sake cigaba da jan Ladi. Daidai lokacin da ta yi kukan kura ta fasa ƙara idanunta a kan yanda ake wulaƙanta mata mutanenta. Ake wulaƙanta mata gida, ake ƙoƙarin tozartata. Cike da mamaki da tsoro take cigaba da kallan abin da ke faruwa dan ba ta taɓa tsammanin nan kusa akwai wanda ze zo ya tarwatsa gidan nan ba bayan abubuwan da ta yi duk dan ta rufe bakin mutane.
"Ku dena wannan abun.. Kar ku kama min mutane.. Me muka yi muku? Ku su waye? Ashe dama kai yaudarata ka yi?" Ta ƙare tana kallan Mutumin nan. Ba tare da ya kalleta ba ya soma takawa dan barin wajen. Wanda hakan ya bawa er sandar damar jan Ladi da ƙarfin da take da shi.
"Wai ba za ki ƙyale ni ba.. Ki sake ni mana.. Ku kuma ku bar abin da kuke yi na faɗa muku ku dena.. ku dena nace.. Yau na shiga 3." Ta ƙare tana sake daƙirewa. Jin komai take kamar ba gaske ba. Kuka kawai Ladi ta fashe da shi lokacin da suka fito daga cikin gidan. Daidai lokacin da wani daga cikin en sandan ya saka key ya datse gidan da shi ta soma ƙoƙarin zubewa a wajen. Er sandar da yake ƙaƙƙarfa ce ta sake riƙota. Se kawai ta cigaba da fiffizgewa kamar wadda ta tayar da aljanu tana ta sumbatu..
"Kar ku min haka.. Ku ƙyale min gida.. Na shiga 3.. Wai gaske ne abin da ke faruwa? Na sake shiga 3 me na yi wa malam ze min haka.." Makamantan abin da take faɗa kenan har lokacin ta kasa yadda gaskiya ne abin da ya faru. Amma idan kuma gaskiyar ne toh tabbas Malam ne ya rage yi mata aiki saboda bijire masa da ta yi a karo na ƙarshe da ta je wajensa kan cewar se ya kwanta da ita kamar yanda aka saba sannan ze mata aiki. Ita kuma tace za ta je ta dawo ya yi mata aikin. Ta ɗauka ze mata aikin ne kawai dan ita ta ƙuɗurtawa ranta ƙin dawowar a wannan karon. Se ga shi ya mata ɗanyan aiki. A haka Ladi na ihu na komai aka shigar da ita cikin mota. Daga haka suka ja ta suka bar wajen.
.... Sun yi nisa suna hirar ita da Little abinta cikin matuƙar kewarsa. Kamar wadda aka tsikara ta tashi ta dubi agogon dake manne a bangon ɗakin. Da sauri ta zaro manyan kyawawan idanunta masu kyau tace
"Kaii!!" Ta faɗa ganin da ta yi har ta gota lokacin da take kai masa Coffee ɗin.
"Didi mene ne?" Little ya faɗa a shagwaɓe yana kallanta. Se ta yi saurin ƙaƙalo murmushi ta saka a kan fuskarta daidai lokacin da take faɗin
"Ba komai fa.. Tashi mu je ka raka ni kitchen.." ta yi maganar tana zamowa daga kan gado. Shi ma sakkowa ya yi da sauri dan karta fita ta bar shi. Ta kama hannunsa suka fita tare daga ɗakin, suna tafiya Little na cigaba da bata labarin abin da ya faru sa basa nan. Ita dai duk hankalinta ya tafi kan kar ta wuce lokacin da ya saka mata ya zo ya dinga mata hayaniya. Kai tsaye kitchen suka nufa. Ta samarwa Little waje ya zauna yayin da ta shiga abin da ya kawota. Tana yi suna cigaba da hirarsu gwanin burgewa. Kai idan ka ganta se ka ɗauka da wani ƙaton mutum me hankali take hira, nan kuwa da Ash_sheik Areef Little take hira, wana ta yi kewarsa mara misali.
"Jira ni a nan.. bari na je na dawo." Ta faɗa lokacin da suka fito hannunta ɗauke da plate ɗin dake ɗauke da cups ɗin Coffee guda 3.
"Didi.." ya faɗa yana riƙo hannunta. Se ta sakar masa murmushi kana tace
"Yanzu fa zan dawo.. Ka zauna Uhmm?" Ta ƙare tana jan kumatunsa. Ba dan ya so ba ya ɗaga kai. Hannunta ɗauke da Coffee ɗin ta soma takawa zuwa ɗakin Bad Man.
A gajiye ya dawo gidan, duk da be tsaya an gama komai a gabansa ba. Ya bar Gwani ne a can ɗin ya taho. Dan haka kai tsaye kayan jikinsa ya fara ragewa dan ya samu ya watsa ruwa a jikinsa. Ya soma ɓalle maɓallin rigarsa aka yi knocking ƙofar ɗakin. Se ya dakata yana ɗaga idanunsa ya kalli ƙofar kamar me nazari. Se kuma ya maida dubansa kan hannunsa ya duba lokaci. Tabbas ya san ita ce. Se dai kuma ya tuna da rashin mutuncin da ta tsira yanzu. Wanda ba karamin ɓata masa rai yake ba. A ganinsa wannan ɗin ai salon raini ne ba komai ba. Ɗauke kai ya yi kamar be ji an yi knocking ɗin ba ya cigaba da abin da yake yi cikin basarwa. Daga ɓangarenta kuwa kwaɓe fuska ta yi jin har lokacin shiru. Se dai ta sake yin shahada ta kuma ƙwanƙwasa ƙofar cike da fatan ta ji takunsa ta juya ta bar wajen dan kuwa har Allah Allah take ta koma su cigaba da hirarsu da Little. Se dai sam, ko kusa ko alama ba ta ji takunsa ba har lokacin, ba ma ta ji motsin komai ba se kawai ganinsa ta yi a ƙofar ɗakin idanunsa a kanta. Da sauri ta ja da baya dan ba ta yi tsammanin ganinsa a wajen ba. Ta yi maza ta sauke kanta ƙasa. Se ta soma ƙoƙarin ajje Coffee ɗin dan ta juya. Lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi buɗe baki yace a fusace
"Kar ki soma ajjewa.." Abin da ya dakatar da ita kenan daga abin da ta yi niyya. Da nufinta ta ɗaga kai ta kalle shi se dai sam ta kasa. Dan haka kawai se ta miƙe a kan ƙafafunta daidai lokacin da yake faɗin
"Wuce ki je ki ajje.." Yanzu kam ba ta san lokacin da ta kalle shi a mamakance ba. Ya ɗauka shi da kansa yace mata kar ta sake shiga ɗakin? Har da yi mata warning a kai. Se yanzu kuma ze ce ta shiga? Kai an ya ma shi ne kuwa? Ganin da ya yi kawai rarraba ido take yi kamar ba ta fahimci abin da yake nufi ba ya sanya shi sake faɗin
"Ke!! Na ce ki shigo koh?" Se ta girgiza kai da sauri ba tare da ta kalle shi ba. A karo na farko tace
"A'ah.. Ka ce kar na sake shigowa."
"Yanzu kuma na ce ki shigo." Ya yi maganar kamar ransa a ɓace.
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO55*
"Ku shigo kawai.." Daga haka ya sauke hannunsa. Kafin ƙiftawa da Bismillah se ga en sandan nan sun shigo sanye cikin uniform ɗinsu kowannensu babu annuri a kan fuskarsa.
"Ku kama duk wanda kuka gani.. Yau za a rufe gidan nan.." Ya sake bayar da umarni ta cikin waya. Cikin sakannin da basu wuce 3 ba en sandan suka fara aikinsu. Juyowar da Ladi za ta yi saboda jin da ta yi har lokacin mutumin be taho ba ya yi daidai da lokacin da mutanen cikin gidan suka soma ihu saboda kamasu da aka fara yi. Tuni kowa ya fara neman hanyar tserewa. Ya yin da en sandan suka ƙi basu kowacce dama. Suka dinga cafkesu suna zuwa su jefa su cikin motar nan. Tuni waɗanda ke cikin ɗaki maza da mata suka soma fitowa wasu da gajerun wanduna wasu da ɗaurin ƙirji. Kowa kuma hanyar gujewa en sandan yake nema. Sake buɗe idanunta Ladi ta yi dan sake tabbatar da abin da ke faruwa, dan ta ɗauka mafarki ne. Dan kuwa ba yau ne rana ta farko da ta soma irin mafarkin nan ba. Se dai da yake ta san hakan ba me yiwuwa ba ne ya sanya ba ta damuwa.
"Kamata.." Shi ne abin da mutumin nan ya faɗa yana kallan Ladi. Babu ɓata lokaci er sandar ta riƙota. Se a lokacin sannan ta fara tunanin to ko dai ba mafarki take yi ba. Jin an fara janta ne ya sanyata buɗe baki da sauri tace
"Ke meye haka ne? Wai ma me kuke min haka ne a cikin gida?" Ta tambaya tana jin wani bugun zuciya.
"Wuce kawai.." Ya sake bata umarni. Se ta sake cigaba da jan Ladi. Daidai lokacin da ta yi kukan kura ta fasa ƙara idanunta a kan yanda ake wulaƙanta mata mutanenta. Ake wulaƙanta mata gida, ake ƙoƙarin tozartata. Cike da mamaki da tsoro take cigaba da kallan abin da ke faruwa dan ba ta taɓa tsammanin nan kusa akwai wanda ze zo ya tarwatsa gidan nan ba bayan abubuwan da ta yi duk dan ta rufe bakin mutane.
"Ku dena wannan abun.. Kar ku kama min mutane.. Me muka yi muku? Ku su waye? Ashe dama kai yaudarata ka yi?" Ta ƙare tana kallan Mutumin nan. Ba tare da ya kalleta ba ya soma takawa dan barin wajen. Wanda hakan ya bawa er sandar damar jan Ladi da ƙarfin da take da shi.
"Wai ba za ki ƙyale ni ba.. Ki sake ni mana.. Ku kuma ku bar abin da kuke yi na faɗa muku ku dena.. ku dena nace.. Yau na shiga 3." Ta ƙare tana sake daƙirewa. Jin komai take kamar ba gaske ba. Kuka kawai Ladi ta fashe da shi lokacin da suka fito daga cikin gidan. Daidai lokacin da wani daga cikin en sandan ya saka key ya datse gidan da shi ta soma ƙoƙarin zubewa a wajen. Er sandar da yake ƙaƙƙarfa ce ta sake riƙota. Se kawai ta cigaba da fiffizgewa kamar wadda ta tayar da aljanu tana ta sumbatu..
"Kar ku min haka.. Ku ƙyale min gida.. Na shiga 3.. Wai gaske ne abin da ke faruwa? Na sake shiga 3 me na yi wa malam ze min haka.." Makamantan abin da take faɗa kenan har lokacin ta kasa yadda gaskiya ne abin da ya faru. Amma idan kuma gaskiyar ne toh tabbas Malam ne ya rage yi mata aiki saboda bijire masa da ta yi a karo na ƙarshe da ta je wajensa kan cewar se ya kwanta da ita kamar yanda aka saba sannan ze mata aiki. Ita kuma tace za ta je ta dawo ya yi mata aikin. Ta ɗauka ze mata aikin ne kawai dan ita ta ƙuɗurtawa ranta ƙin dawowar a wannan karon. Se ga shi ya mata ɗanyan aiki. A haka Ladi na ihu na komai aka shigar da ita cikin mota. Daga haka suka ja ta suka bar wajen.
.... Sun yi nisa suna hirar ita da Little abinta cikin matuƙar kewarsa. Kamar wadda aka tsikara ta tashi ta dubi agogon dake manne a bangon ɗakin. Da sauri ta zaro manyan kyawawan idanunta masu kyau tace
"Kaii!!" Ta faɗa ganin da ta yi har ta gota lokacin da take kai masa Coffee ɗin.
"Didi mene ne?" Little ya faɗa a shagwaɓe yana kallanta. Se ta yi saurin ƙaƙalo murmushi ta saka a kan fuskarta daidai lokacin da take faɗin
"Ba komai fa.. Tashi mu je ka raka ni kitchen.." ta yi maganar tana zamowa daga kan gado. Shi ma sakkowa ya yi da sauri dan karta fita ta bar shi. Ta kama hannunsa suka fita tare daga ɗakin, suna tafiya Little na cigaba da bata labarin abin da ya faru sa basa nan. Ita dai duk hankalinta ya tafi kan kar ta wuce lokacin da ya saka mata ya zo ya dinga mata hayaniya. Kai tsaye kitchen suka nufa. Ta samarwa Little waje ya zauna yayin da ta shiga abin da ya kawota. Tana yi suna cigaba da hirarsu gwanin burgewa. Kai idan ka ganta se ka ɗauka da wani ƙaton mutum me hankali take hira, nan kuwa da Ash_sheik Areef Little take hira, wana ta yi kewarsa mara misali.
"Jira ni a nan.. bari na je na dawo." Ta faɗa lokacin da suka fito hannunta ɗauke da plate ɗin dake ɗauke da cups ɗin Coffee guda 3.
"Didi.." ya faɗa yana riƙo hannunta. Se ta sakar masa murmushi kana tace
"Yanzu fa zan dawo.. Ka zauna Uhmm?" Ta ƙare tana jan kumatunsa. Ba dan ya so ba ya ɗaga kai. Hannunta ɗauke da Coffee ɗin ta soma takawa zuwa ɗakin Bad Man.
A gajiye ya dawo gidan, duk da be tsaya an gama komai a gabansa ba. Ya bar Gwani ne a can ɗin ya taho. Dan haka kai tsaye kayan jikinsa ya fara ragewa dan ya samu ya watsa ruwa a jikinsa. Ya soma ɓalle maɓallin rigarsa aka yi knocking ƙofar ɗakin. Se ya dakata yana ɗaga idanunsa ya kalli ƙofar kamar me nazari. Se kuma ya maida dubansa kan hannunsa ya duba lokaci. Tabbas ya san ita ce. Se dai kuma ya tuna da rashin mutuncin da ta tsira yanzu. Wanda ba karamin ɓata masa rai yake ba. A ganinsa wannan ɗin ai salon raini ne ba komai ba. Ɗauke kai ya yi kamar be ji an yi knocking ɗin ba ya cigaba da abin da yake yi cikin basarwa. Daga ɓangarenta kuwa kwaɓe fuska ta yi jin har lokacin shiru. Se dai ta sake yin shahada ta kuma ƙwanƙwasa ƙofar cike da fatan ta ji takunsa ta juya ta bar wajen dan kuwa har Allah Allah take ta koma su cigaba da hirarsu da Little. Se dai sam, ko kusa ko alama ba ta ji takunsa ba har lokacin, ba ma ta ji motsin komai ba se kawai ganinsa ta yi a ƙofar ɗakin idanunsa a kanta. Da sauri ta ja da baya dan ba ta yi tsammanin ganinsa a wajen ba. Ta yi maza ta sauke kanta ƙasa. Se ta soma ƙoƙarin ajje Coffee ɗin dan ta juya. Lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi buɗe baki yace a fusace
"Kar ki soma ajjewa.." Abin da ya dakatar da ita kenan daga abin da ta yi niyya. Da nufinta ta ɗaga kai ta kalle shi se dai sam ta kasa. Dan haka kawai se ta miƙe a kan ƙafafunta daidai lokacin da yake faɗin
"Wuce ki je ki ajje.." Yanzu kam ba ta san lokacin da ta kalle shi a mamakance ba. Ya ɗauka shi da kansa yace mata kar ta sake shiga ɗakin? Har da yi mata warning a kai. Se yanzu kuma ze ce ta shiga? Kai an ya ma shi ne kuwa? Ganin da ya yi kawai rarraba ido take yi kamar ba ta fahimci abin da yake nufi ba ya sanya shi sake faɗin
"Ke!! Na ce ki shigo koh?" Se ta girgiza kai da sauri ba tare da ta kalle shi ba. A karo na farko tace
"A'ah.. Ka ce kar na sake shigowa."
"Yanzu kuma na ce ki shigo." Ya yi maganar kamar ransa a ɓace.
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO55*