Sashe 16
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Will u just shut up ko na nuna miki waye ni? Fita.." Yanzun ma ya ƙare a fusace yana watsa mata wani banzan kallo. Jikinta na matuƙar rawa, hawaye sun cika idanunta fall ta juya tana jin yanda ƙafarta ke rawa, haka ta fice daga cikin ɗakin. Kallan abin da ta ajje ya yi a fusace ya ɗaga ƙafarsa ya yi ball da su zuwa jikin bango. Cikin lokaci ƙanƙani kowanne ya yi nasa wajen bayan sun tarwatse a wajen, coffee ɗin kansa ya zube a wajen. Be bi ta kan komai ba ya koma ya zauna a kan gadon, hannunsa ya ɗauka ya cusa cikin sumar kansa yana jin wani shahararren ɓacin rai na taso masa. Se ya fesar da wata zazzafar iska daga bakinsa yana lumshe idanunsa. Mom ta zo ta sanar da shi lokacin da wannan wasan ze ƙare, idan ba haka ba da kansa ze samarwa kansa mafita ya rabu da wannan wasan.
Se da ta ƙarasa cikin ɗakin sannan ta iya fashewa da kukan. Ta shiga raira shi tana tuna irin wannan cin mutuncin da ya mata. Me ta masa haka da ya tsaneta? A haka za su yi zaman auren? Tana nan kwance tana cigaba da kukan ko zuciyarta za ta yi sauƙi ta dena mata zafi Baba Atine ya shigo ɗakin. Da sauri ta ƙaraso tana faɗin
"Subhanallahi Afrah.. Me ya faru?" ta tambaya tana ɗaga kanta ta ɗora a kan cinyarta.
"Koro ni ya yi.." Ajiyar zuciya Atine ta sauke kafin tace
"Toh ya isa haka. Ki dena kuka ka da kanki ya yi ciwo kin ji?" Jinjina kai kawai ta yi ba dan tana da tabbacin kukan ze tsaya ba. Atine ba ta samu cewa komai ba, se da ta ji ta dena kukan sannan ta soma faɗin
"Komai za ki yi ba laifi ba ne Afrah. Ko da ze miki wani abu ki daure ki cije ki yi haƙuri, saboda so nake ke ɗin nan ki zama matar Areef ta har abada. Kin ga ko anan kin karya alƙadarin mahaifiyarsa. Shi ya sa nake so daga yau ke za ki dinga dafa coffee ɗin kina kai masa, ko da ze miki wani abun a farko ne, kuma a farko ne za ki ji zafinsa, idan ya kasance kin saba da abin da yake miki ba za ki dinga damuwa ba. Shi kuma mutum a duk lokacin da yake wani abu dan wani ya ji babu daɗi, toh daga lokacin da ya fahimci wanda yake ƙuntatawan ba ya damuwa dole ze haƙura. Toh haka nake so ta faru tsakaninki da Areef. In Sha Allah nan gaba ze so ki fiye da tsammani. Ki yi haƙuri, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri kar ki sare tun yanzu kin ji?" Shiru ta yi na tsawon sakanni masu yawa bayan gama saurarar maganar Atine. Wato kenan tana nufin ta cigaba da kai masa coffee ɗin bayan wannan abun da ya mata? Se da ta yi sheshsheƙa sannan tace
"Don Allah Baba ki bar shi.." Girgiza kai ta yi tace
"A'ah ki dena faɗar haka Afrah. Ke yarinya ce me hankali, kin kuma san fa'idar bin umarnin iyaye, saboda haka ki daure ki yi biyayya a gidan auren ki. Kowacce mace na da nata ƙalubalen, ke wannan shi me naki. Amma idan dai har kika yi haƙuri In Sha Allah ba za ki yi danasani ba.." Wasu hawaye masu ɗumi ne suka zubo mata a kan fuskarta, tana tunanin yanda rayuwarta za ta cigaba da kasancewa a cikin gidan. Se dai ita kanta ba za taso watsawa Abbanta ƙasa a ido ba, dan haka za ta jure duk wani ƙalubale da zata fuskanta cikin gidan, tunda dai Abba da kansa ya aura mata shi, wanda hakan ke nuna ya san wanda ya aura mata. Dan haka za ta yi ƙoƙari wajen ƙin ganin ta watsawa Abban ƙasa a ido.
"Allah ka ba ni iko.. Ka sassauta min.." ta faɗa a kan laɓɓanta daidai lokacin da wasu hawaye suka zubo a kan fuskarta.
... "Abbansu ina so na dinga sanin halin da 'ya'yana ke ciki. Amma babu dama tunda babu waya a hannunsu.." Kallanta Abna dake kan kujera ya yi sannan yace
"Haka ne, hakan na da kyau. Ko babu komai ke ɗin tamkar ƙawa kike a wajen 'ya'yanki. Na kuma san za su fara magana dake ne a dukkan wani abu da ya shige musu duhu. Shi ya sa a kodayaushe nake alfahari dake.." ya ƙare yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi har zuciyarta tana jin daɗin wannan yabon da Abban ya mata. Kafin tace komai yace
"Se dai har yanzun ban amince su riƙe waya ba. Saboda haka zan karɓar miki number mazajensu idan ya so se ku dinga magana ta nan. Duk lokacin kuma da suka ga ya dace su fara riƙe waya da kansu se su siya musu.."
"Toh shi kenan Abbansu na gode.." Murmushi Abba ya yi, yana shirin cewa wanj abu, se ga Little ya fito daga cikin ɗaki sanye cikin ƙananan kaya yana murza idanu, alamar daga bacci ya tashi. Kai tsaye jikin Ammi ya faɗa yana tura baki a shagwaɓe.
"Toh me kuma ya faru?" Ammj ta faɗa tana ɗauke hannunsa daga kan fuskarsa.
"Lulu da Didina.." ya faɗa kamar ze yi kuka. Kallan Abba Ammi ta yi se kuma ta maida dubanta kan Little ɗin tace
"Toh ya isa haka uhmm?" ta faɗa tana kwantar da shi a jikinta. Miƙewa ya yi da sauri yana fashewa da kukan lokaci ɗaya yana faɗin
"Ni dai Ammi su Lulu.." Ya faɗa yana sake buɗe baki. Sauke numfashi Ammi ta yi, dan ta fahimci yau ɗin da gaske yake, rigimar ganin en uwansa yake. Kafin ta kai ga cewa komai Abba yace yana miƙa hannunsa ya ɗauke shi
"Je ka maza Ammi ta shiryaka ka zo na kaika.." Dariya me suna dariya Little ya yi yana sauka daga jikin Abba, ya kalli Ammi yace
"Ammi Abba yace ki shirya ni.." ya faɗa yana cigaba da dariyarsa.
"Aou har ka gama kukan?" Ammi ta faɗa tana murmushi. Se ya cuno baki kawai yana murmushi.
"Ahh toh ba ya samu abin da yake so ba?" Abba ya faɗa yana murmushi.
Cigaba da zama Abba ya yi cikin d'akin, yayin da Ammi ta shige cikin d'akin dan shirya Little. Sallamar da aka yi cikin d'akin ita ya sanya shi juyawa yana amsa sallamar. K'arasowa Fatima ta yi cikin d'akin ta zube a k'asa, cike da ladabi tace
"Abba ina yini?"
"Lafiya k'alau, ku na lafiya?"
"Alhamdulillah.." Se ta d'an dakata a nan, sannan ta d'ora da
"Abba Ammi ba ta nan?"
"Tana ciki.." Ya yi maganar yana nuna d'akin da Ammi ta shiga. Mik'ewa Fatima ta yi ta shiga d'akin yanzun ma da sallama a bakinta. Ammi ta amsa sallamar tana mamakin ganinta. Dan ita dai kam ta d'an jima ba ta ganta ba. Gaisawa suka yi da Ammi cike da sabo kamar yanda suka saba. Fatima ta mik'a hannu wajen Little tace
"Little zo ina za ka je.?" Mak'e kafad'a ya yi yana fad'in
"A'ah.. Ammi in tafi.?" Ya tambaya yana kallan Ammi. Se ta girgiza kai tana fad'in
"A'ah jira ni mu fita tare.." Komawa gefen Ammin ya yi ya zauna yana d'an wuwwulga k'afa, har lokacin murmushi ya k'i barin fuskarsa.
"Ammi da ma wata magana na ji, shi ne na ce bari na zo dan tabbatarwa.. Ammi na d'an kwana biyu ba na garin, se yau na dawo. Shi ne nake ji wai an yi bikinsu Lulu" ta faɗa a sanyaye. Sauke numfashi Ammi ta yi, se da ta ɗan ja lokaci ka min tace
"Ki yi haƙuri Fatima.. Ba laifin kowa ba ne se na akasin da aka samu ba kya garin. Auren ne ya tashi bagatatan shi yasa ma ba ki ji labari ba. Amma ki yi haƙuri.." Ita Fatima ji take kamar wasan yara ko kuma wani labari. Yau ba da ban Ammi da kanta ta faɗa mata wannan maganar ba, da babu abin da ze sa ta yadda. Se dai ga shi kamar yanda ta ji labari, da gasken Masoyiyar tata ta yi aure ba ma ta san da hakan ba se yanzu.
"Allah ya sanya alkhairi Ammi.. Bari na je gida.."
"A'ah Fatima dawo ki zauna.. Dama yanzu Abbansu ze kai Little gidan Lulu, dan haka ki tashi ya kai ku, se ki ganta, ni ma kuma ki gano min yanda take.." Ammi ta ƙarasa da murmushi a kan fuskarta. Murmushin ita ma Fatima ta yi tana faɗin
"Ammi ai ban faɗawa Umma ba.."
"Babu damuwa ni da kai na zan sanar da ita.. Wuce mu je.." Ammi ta faɗa tana miƙewa tsaye hannunta riƙe da na Little. Fatima ba ta sake cewa komai ba se yin gaba da ta yi. Ammi na bayanta suka fito daga cikin ɗakin. Abba na tsaye yana amsa kira. Ammi ta saki hannun Little ta ƙarasa inda Abba yake. Se a lokacin sannan Little ya yadda Fatima ta kama hannunsa, ganinsa ga shi ga Abban da ze fita da shi. Se da Abba ya ida wayar sannan Ammi tace
"Abbansu ga Fatima nan za ta muku rakiya. Se ka ajje su tare da Little ɗin idan babu damuwa.." Kallan Fatima Abba ya yi sannan ya dubi Ammi yace
"Ba na son tarayyarsu da ƙawaye ta cigaba da tafiya har yanzun.." Girgiza kai Ammi ta yi kafin tace
"Babu komai Abbansu. Na yadda da Fatima, na san halinta, babu abin da ze faru In Sha Allah. Ba halinsu ɗaya da Lulu ba, dan kuwa ta fita hankali, shi yasa ma na bar tarayyarsu har zuwa wannan lokacin.." Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace
"Shi kenan. Allah ya ƙara tsarewa.."
"Ameen ya rabbi.. A gaida mim da ɗiyata.." Ammi ta faɗa har ranta tana jin farin ciki kamar ita ce za ta je ganin Lulun.
"Za ta ji In Sha Allah.." Abba ya faɗa shi ma yana murmushin.
"Saura Afrah.." Jinjina kai Abba ya yi yana faɗin
Se da ta ƙarasa cikin ɗakin sannan ta iya fashewa da kukan. Ta shiga raira shi tana tuna irin wannan cin mutuncin da ya mata. Me ta masa haka da ya tsaneta? A haka za su yi zaman auren? Tana nan kwance tana cigaba da kukan ko zuciyarta za ta yi sauƙi ta dena mata zafi Baba Atine ya shigo ɗakin. Da sauri ta ƙaraso tana faɗin
"Subhanallahi Afrah.. Me ya faru?" ta tambaya tana ɗaga kanta ta ɗora a kan cinyarta.
"Koro ni ya yi.." Ajiyar zuciya Atine ta sauke kafin tace
"Toh ya isa haka. Ki dena kuka ka da kanki ya yi ciwo kin ji?" Jinjina kai kawai ta yi ba dan tana da tabbacin kukan ze tsaya ba. Atine ba ta samu cewa komai ba, se da ta ji ta dena kukan sannan ta soma faɗin
"Komai za ki yi ba laifi ba ne Afrah. Ko da ze miki wani abu ki daure ki cije ki yi haƙuri, saboda so nake ke ɗin nan ki zama matar Areef ta har abada. Kin ga ko anan kin karya alƙadarin mahaifiyarsa. Shi ya sa nake so daga yau ke za ki dinga dafa coffee ɗin kina kai masa, ko da ze miki wani abun a farko ne, kuma a farko ne za ki ji zafinsa, idan ya kasance kin saba da abin da yake miki ba za ki dinga damuwa ba. Shi kuma mutum a duk lokacin da yake wani abu dan wani ya ji babu daɗi, toh daga lokacin da ya fahimci wanda yake ƙuntatawan ba ya damuwa dole ze haƙura. Toh haka nake so ta faru tsakaninki da Areef. In Sha Allah nan gaba ze so ki fiye da tsammani. Ki yi haƙuri, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri kar ki sare tun yanzu kin ji?" Shiru ta yi na tsawon sakanni masu yawa bayan gama saurarar maganar Atine. Wato kenan tana nufin ta cigaba da kai masa coffee ɗin bayan wannan abun da ya mata? Se da ta yi sheshsheƙa sannan tace
"Don Allah Baba ki bar shi.." Girgiza kai ta yi tace
"A'ah ki dena faɗar haka Afrah. Ke yarinya ce me hankali, kin kuma san fa'idar bin umarnin iyaye, saboda haka ki daure ki yi biyayya a gidan auren ki. Kowacce mace na da nata ƙalubalen, ke wannan shi me naki. Amma idan dai har kika yi haƙuri In Sha Allah ba za ki yi danasani ba.." Wasu hawaye masu ɗumi ne suka zubo mata a kan fuskarta, tana tunanin yanda rayuwarta za ta cigaba da kasancewa a cikin gidan. Se dai ita kanta ba za taso watsawa Abbanta ƙasa a ido ba, dan haka za ta jure duk wani ƙalubale da zata fuskanta cikin gidan, tunda dai Abba da kansa ya aura mata shi, wanda hakan ke nuna ya san wanda ya aura mata. Dan haka za ta yi ƙoƙari wajen ƙin ganin ta watsawa Abban ƙasa a ido.
"Allah ka ba ni iko.. Ka sassauta min.." ta faɗa a kan laɓɓanta daidai lokacin da wasu hawaye suka zubo a kan fuskarta.
... "Abbansu ina so na dinga sanin halin da 'ya'yana ke ciki. Amma babu dama tunda babu waya a hannunsu.." Kallanta Abna dake kan kujera ya yi sannan yace
"Haka ne, hakan na da kyau. Ko babu komai ke ɗin tamkar ƙawa kike a wajen 'ya'yanki. Na kuma san za su fara magana dake ne a dukkan wani abu da ya shige musu duhu. Shi ya sa a kodayaushe nake alfahari dake.." ya ƙare yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi har zuciyarta tana jin daɗin wannan yabon da Abban ya mata. Kafin tace komai yace
"Se dai har yanzun ban amince su riƙe waya ba. Saboda haka zan karɓar miki number mazajensu idan ya so se ku dinga magana ta nan. Duk lokacin kuma da suka ga ya dace su fara riƙe waya da kansu se su siya musu.."
"Toh shi kenan Abbansu na gode.." Murmushi Abba ya yi, yana shirin cewa wanj abu, se ga Little ya fito daga cikin ɗaki sanye cikin ƙananan kaya yana murza idanu, alamar daga bacci ya tashi. Kai tsaye jikin Ammi ya faɗa yana tura baki a shagwaɓe.
"Toh me kuma ya faru?" Ammj ta faɗa tana ɗauke hannunsa daga kan fuskarsa.
"Lulu da Didina.." ya faɗa kamar ze yi kuka. Kallan Abba Ammi ta yi se kuma ta maida dubanta kan Little ɗin tace
"Toh ya isa haka uhmm?" ta faɗa tana kwantar da shi a jikinta. Miƙewa ya yi da sauri yana fashewa da kukan lokaci ɗaya yana faɗin
"Ni dai Ammi su Lulu.." Ya faɗa yana sake buɗe baki. Sauke numfashi Ammi ta yi, dan ta fahimci yau ɗin da gaske yake, rigimar ganin en uwansa yake. Kafin ta kai ga cewa komai Abba yace yana miƙa hannunsa ya ɗauke shi
"Je ka maza Ammi ta shiryaka ka zo na kaika.." Dariya me suna dariya Little ya yi yana sauka daga jikin Abba, ya kalli Ammi yace
"Ammi Abba yace ki shirya ni.." ya faɗa yana cigaba da dariyarsa.
"Aou har ka gama kukan?" Ammi ta faɗa tana murmushi. Se ya cuno baki kawai yana murmushi.
"Ahh toh ba ya samu abin da yake so ba?" Abba ya faɗa yana murmushi.
Cigaba da zama Abba ya yi cikin d'akin, yayin da Ammi ta shige cikin d'akin dan shirya Little. Sallamar da aka yi cikin d'akin ita ya sanya shi juyawa yana amsa sallamar. K'arasowa Fatima ta yi cikin d'akin ta zube a k'asa, cike da ladabi tace
"Abba ina yini?"
"Lafiya k'alau, ku na lafiya?"
"Alhamdulillah.." Se ta d'an dakata a nan, sannan ta d'ora da
"Abba Ammi ba ta nan?"
"Tana ciki.." Ya yi maganar yana nuna d'akin da Ammi ta shiga. Mik'ewa Fatima ta yi ta shiga d'akin yanzun ma da sallama a bakinta. Ammi ta amsa sallamar tana mamakin ganinta. Dan ita dai kam ta d'an jima ba ta ganta ba. Gaisawa suka yi da Ammi cike da sabo kamar yanda suka saba. Fatima ta mik'a hannu wajen Little tace
"Little zo ina za ka je.?" Mak'e kafad'a ya yi yana fad'in
"A'ah.. Ammi in tafi.?" Ya tambaya yana kallan Ammi. Se ta girgiza kai tana fad'in
"A'ah jira ni mu fita tare.." Komawa gefen Ammin ya yi ya zauna yana d'an wuwwulga k'afa, har lokacin murmushi ya k'i barin fuskarsa.
"Ammi da ma wata magana na ji, shi ne na ce bari na zo dan tabbatarwa.. Ammi na d'an kwana biyu ba na garin, se yau na dawo. Shi ne nake ji wai an yi bikinsu Lulu" ta faɗa a sanyaye. Sauke numfashi Ammi ta yi, se da ta ɗan ja lokaci ka min tace
"Ki yi haƙuri Fatima.. Ba laifin kowa ba ne se na akasin da aka samu ba kya garin. Auren ne ya tashi bagatatan shi yasa ma ba ki ji labari ba. Amma ki yi haƙuri.." Ita Fatima ji take kamar wasan yara ko kuma wani labari. Yau ba da ban Ammi da kanta ta faɗa mata wannan maganar ba, da babu abin da ze sa ta yadda. Se dai ga shi kamar yanda ta ji labari, da gasken Masoyiyar tata ta yi aure ba ma ta san da hakan ba se yanzu.
"Allah ya sanya alkhairi Ammi.. Bari na je gida.."
"A'ah Fatima dawo ki zauna.. Dama yanzu Abbansu ze kai Little gidan Lulu, dan haka ki tashi ya kai ku, se ki ganta, ni ma kuma ki gano min yanda take.." Ammi ta ƙarasa da murmushi a kan fuskarta. Murmushin ita ma Fatima ta yi tana faɗin
"Ammi ai ban faɗawa Umma ba.."
"Babu damuwa ni da kai na zan sanar da ita.. Wuce mu je.." Ammi ta faɗa tana miƙewa tsaye hannunta riƙe da na Little. Fatima ba ta sake cewa komai ba se yin gaba da ta yi. Ammi na bayanta suka fito daga cikin ɗakin. Abba na tsaye yana amsa kira. Ammi ta saki hannun Little ta ƙarasa inda Abba yake. Se a lokacin sannan Little ya yadda Fatima ta kama hannunsa, ganinsa ga shi ga Abban da ze fita da shi. Se da Abba ya ida wayar sannan Ammi tace
"Abbansu ga Fatima nan za ta muku rakiya. Se ka ajje su tare da Little ɗin idan babu damuwa.." Kallan Fatima Abba ya yi sannan ya dubi Ammi yace
"Ba na son tarayyarsu da ƙawaye ta cigaba da tafiya har yanzun.." Girgiza kai Ammi ta yi kafin tace
"Babu komai Abbansu. Na yadda da Fatima, na san halinta, babu abin da ze faru In Sha Allah. Ba halinsu ɗaya da Lulu ba, dan kuwa ta fita hankali, shi yasa ma na bar tarayyarsu har zuwa wannan lokacin.." Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace
"Shi kenan. Allah ya ƙara tsarewa.."
"Ameen ya rabbi.. A gaida mim da ɗiyata.." Ammi ta faɗa har ranta tana jin farin ciki kamar ita ce za ta je ganin Lulun.
"Za ta ji In Sha Allah.." Abba ya faɗa shi ma yana murmushin.
"Saura Afrah.." Jinjina kai Abba ya yi yana faɗin