← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 122

Sashe 26

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"A'ah.. Lulu ai se komai ya yi sannan zan zo na ɗauke ki.. Tafiya ma zan yi dake ballantana ki ce za ki fuskanci ƙyama daga wajen wasu.. Ki na ji na?" Ba tare da tsayawa ta wani fuskanci maganar Mamin ba tace

"Ehh.." Gyara zama Mami ta yi sannan ta soma faɗin

"Ban san yanda aka yi ba, aka samu wani hotonki wani ya rungume ki, cikin wani restaurant. Na san ba halinki ba ne amma dai tabbas hoton nan na gaske ne ba haɗi ba. Amma na yi miki uzuri dan dai kin ɗan yi sharholiya sau ɗaya. Se dai hakan ma mu taimakarmu ya yi. Dan kuwa da wannan hoton na yi amfani, da so na yi ma direct a san yanda za a yi ya je wajen shi wanda aka aura miki ɗin. Se dai kuma hakan ze iya kwaɓe mana. Hakan ne ya sa na saka aka nemo Abokinsa, aka same shi har inda yake aka kai masa zancen cewar matar da Abokinsa ya aura ba mutuniyar kirki ba ce, an rufe Abokin nasa ne ba tare da an sanar da shi ba aka aura masa ita. Idan kuma be yadda ba har sheda suna da ita, suka faɗa masa cewar su ɗin suna ɗaya daga cikin waɗanda ke ƙaunar mahaifin mijin naki shi ya sa ba za su so a cuce shi ba, hakan ne ya sa suka binciko wannan abun. Da farko dai ya so ya ba su matsala, dan ko saurararsu ma ƙin yi ya yi a kan hakan. Amma daga baya da ya ji har da sheda suna da ita, bayan duk uban bayanan da suka masa, se ya tsaya har ma ya tura hoton dan shi ma ya girgiza da ganin hoton. Daga nan ma ko ƙara saurararsu be yi ba ya tafi hankali a tashe. Sun kuma tabbatar min da sun san duk yanda ake ciki se ya nunawa Abokin nasa hoton. Na san tunani ze yi ba ze so cin amanar abokinsa ba, be san hakan mu ya taimakawa ba. In taƙaice miki zance dai wannan hoton ya je wajen Abokin wanda aka aura mikin, na kuma san idan har zuwa yanzu be je gare shi ba, toh yana dab da zuwa gare shi." Se ta ɗan dakata a nan sannan ta cigaba da cewa

"Amma fa kar ki ɗauki hakan a matsayin wani abu, kawai duk na saka an yi hakan ne dan mu samu ya sake ki salin alin ba tare da tsayawa wani dogon bincike ba. Shi ya sa muka yi amfani da abubuwa masu ƙarfi, da kuma zazzafar hujja.. Kar ki sake ki gode min kuma, ni ɗin kamar mahaifiyarki ce kin sani, har kuma abada ba zan taɓa bari na ga kin rayu cikin ƙunci ba. Ko da zan rasa wani abun ne kuwa, zan yi iya bakin ƙoƙarina wajen ganin na ciro ki daga wannan hali.."

Tunda Mami ta soma magana Lulu ke kallanta, zuciyarta na bugawa. Me Mamin ke faɗa ne? A kan me take magana? Me take ƙoƙarin aikata mata a matsayin gyara rayuwarta? Zama ta yi kamar wata saƙaguwa wadda aka dasa a wajen, idanunta dake cike taff da ƙwalla suka tsaya ƙiƙam, ita kanta ƙwallar ba ta san lokacin da ta koma ba. Wani irin bugu zuciyarta ke yi wanda tunda uwarta ta haifeta ba ta taɓa jin irinsa ba, ko kuma ba a faɗa mata ba, ta san wannan bugun ya wuce ƙa'ida. Cikin sakannin da basu wuce 3 ba jikinta ya ɗauki wata irin rawa kamar wadda ake kaɗata. Tashin hankali, tsoro gami da ruɗewa suka mata dirar mikiya. Ji take kamar kunnenta be jiye mata daidai ba a kan abin da Mamin ke faɗa ba. So take ta buɗe baki ta yi magana, ta tambayi Mamin ta sake yi mata bayani a kan abin da take faɗa, ta kuma ji cikakken bayani game da maganar hoton da ta yi. Se dai tsananin ruɗewa ya hanata aikata hakan. Wani jiri jiri ta ji yana kwasarta, har se da ta soma ganin giftawar wasu abubuwa cikin idanunta, wanda hakan ya tilasta mata runtse idanunta da sauri tana dafe saitin zuciyarta da take ji kamar tana ƙoƙarin yin tsalle ne ta fito daga zuciyarta..

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO37*

___"Ke lafiya kuwa?" Mami ta faɗa tana riƙo hannun Lulu ganin yanda ta birkice lokaci ƙanƙani. Hannu Lulun ta saka ta ture na Mamin lokaci ɗaya tana miƙewa ta soma ja da baya, daidai lokacin da kyawawan idanunta suka soma ƙyalli kamar waɗanda aka zuba wani abu a cikinsu. Se dai ƙwalla ce kawai ta gama cika cikin idanun taff wanda ƙiris take jira ta zuba. Da mamakin dai Mami ta miƙe tana kallanta tace

"Me yake faruwa Lulu?" Kasa riƙe kanta Lulu ta yi se fashewa da kuka da ta yi, ta zube a ƙasa tana yin kukan me cin rai. I zuwa yanzu Mami ta ida ruɗewa, ta ƙarasa da sauri tana sake tambayarta dalilin chanjawar tata a karo na barkatai. Da ƙyar kuma cikin kuka ta iya buɗe baki ta soma faɗin

"Mami me kika min? A kan wane hoto kike magana Mami? Mami ko mene ne ya je wajen Gwani ai ze je wajen Abba. Mami ko da da wasa ne Abba ze iya yanka ni. Mami me ya sa kika min haka..?" Kallanta Mami take yi cike da mamakin abin da ke fitowa daga cikin bakinta. Ba ta taɓa tunanin wannan shi ne abin da ze biyo baya ba, bayan ta sanar da Lulun abin da ta aikata ba, ba ta taɓa tsammanin abin da Lulun za ta mata ba kenan. Se dai dan sake tabbatarwa ya sanyata faɗin

"Ki na cikin hayyacinki kuwa daughter? Ina miki magana ne fa a kan raba aurenki da mutumin da ba kya so. Wanda muke ta fafutukar neman hanyar da za ku rabu da shi. Se yau na samo mafita kike ƙoƙarin sace min gwuiwa? Ko dai asiri ya miki ne? Hoto kuma, hoton da aka miki ne cikin wani restaurant rungume da wani, kuma dan ya je wajen shi mijin da aka aura miki ai ba ze bari ya sake fita wani wajen ba, daga nan ze tsaya, ko kin manta malamin addini ne? Abba kuma shi ya sa tun farko na faɗa miki ba wajensu za ki koma ba ni zan tafi dake wajena.." Girgiza kai Lulu ta shiga yi tana sake jin yanda kanta na wani irin sara mata.

"Mami ba ni ba ce.. Mami ba ni ba ce.." ta faɗa tana cigaba da girgiza kan cikin matuƙar ruɗewa. Kafin Mamin tace komai ta ɗora da faɗin

"Me ya sa za ki min haka Mami? Mami rayuwata ce za ta lalace fa har abada.. Na shiga 3.." ta ƙarashe tana riƙe kanta da take ji kamar ze faɗo mata. Dagalo Mami ta tsaya tana kallan ikon Allah. Anya kuwa Lulun ce ko dai an musanya mata ita? Anya kuwa tana cikin hayyacinta ko kuwa me yake faruwa? Yarinyar dake neman hanyar da za ta rabu da wannan auren, yanzu kuma an samo shi ne har ta tsaya tana iya bambance hanya me kyau da mara kyau? Cikin ɓacin rai Mami tace

"Ina ruwanki ne Lulu? Dama ba abin da muke so ba kenan? Babu wata hanya da ta za ɓulle mana, na yi iya tunanina wajen tuno mafitar da za ta saka ya sake ki amma na kasa. Cikin sauƙi kuma se ga wannan hanyar, wadda ita ce mafi sauƙi da ze sawwaƙe miki cikin kwanciyar hankali.. Ai dama abin da nake so ya yi zargi kenan, matar da ya aura ba mutuniyar kirki ba ce ta banza ce.. Idan ya sake ki ba shi kenan ba? Tunda dai kin san ke ba haka kike ba me ye na damuwa.. Saboda haka ki..."

"Ki ƙyale ni Mami.." Lulu ta faɗa tana miƙewa tsaye, duk da yanda ilahirin jikinta ke rawa saboda tsorata da ta yi da maganganun Mamin. Ba kuma ta jira Mamin da mamaki ya kusa kashewa ba ta ɗora da faɗin

"Zuciyata na dab da tarwatsewa Mami ki ƙyale ni.. Na kasa fahimtar abin da kike nufi.. Ban san da maganar hoton da kike yi ba, kuma kina maganar ɓata min suna da sunan mafita. Mami dama ba kya sona?" Ta tambaya muryarta a karye, jajayen idanunta a kan fuskar Mami. Wajen minti 1 amma Mami ta kasa furta komai se kallan Lulun da take yi, a ranta tana saƙa ko dai zuwan yarinyar gidan nan ya taɓa ƙwaƙwalwarta, ko kuma dai aljanu sun shafeta? Yau ita Lulu ke faɗawa magana haka a kan abin da ta yi dan jin daɗinta? Lallai tabbas akwai wata a ƙasa.

"Me kika sha ne Lulu? Ko dai kin samu taɓin hankali ne zamanki cikin gidan nan?" Shi ne abin da Mami ta faɗa tana kallanta sosai. Wasu zafafan hawaye ne suka zubo a kan kuncin Lulu, ta kasa cewa komai se komawa da ta yi ta kifa kanta a kan gadon ta cigaba da kukanta tunda ta ji Mamin ta ƙi tsayawa ta mata bayani yanda za ta fahimta face sake dilmiyar da ita da take yi, a kan lallai da gasken ta yi amfani da wani hoto ne can daban na wata dan cikar burinsu, wanda ita a ganinta wannan ɗin kamar tarwatsa mata rayuwarta ne Mamin ke ƙoƙarin yi. Ƙarasawa Mami ta yi ta ɗora hannunta a kan kafaɗar Lulu, da sauri Lulu ta saka hannunta ta ture hannun Mamin tana sake jin wani irin karyewar zuciya. Runtse idanunta Mami ta yi tana jin yanda tsoro ke kamata. Lallai lamarin ya caɓe mata. Ba ta taɓa tunanin Lulun na da wannan hankalin ba, ba ta taɓa tunanin Lulun kan ɗauki hakan a matsayin ɓata mata suna ba. Ta riga ta san halin Lulu, ta san wace ce ita, ta ɗauka duk abin da ta zo da shi za ta karɓa ne hannu bibbiyu. Se ga shi ta nuna mata ba haka ba ne.

"Lulu.." Mami ta faɗa tana sake ƙoƙarin kai hannunta kan kafaɗar Lulun.

"Ki ƙyale ni na ce.." ta faɗa cikin kukan dai. Sauke numfashi Mami ta yi tana ɗaukar jakarta da ta ajje sannan cikin sanyin da jikinta ya yi tace
Chapter 26 · 0% Book details