← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 122

Sashe 71

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya, har aka ɗauki watanni Mom ba ta san da zaman cikin Mommah ba. Ita kam Mommah a nutse cikin kwanciyar hankali take rainon cikinta babu hayaniya. Ba ta nemi wata er aiki ba, ita ta cigaba da ayyukanta, se wani lokacin Yaya Amina kan zuwa ta tayata aiki, dan a lokacin ba ta da manyan 'ya'ya. Gefe guda dai kam Mom na nan tana cigaba da yaɓawa Mommah magana duk a kan haihuwa, wai ita nan duk dan Mommahn ta shiga damuwa, ta kuma muzanta, dan har lokacin ba ta san da cikin ba. Ita kam babu abin da ya dameta, ta maidata tamkar wata mahaukaciya. Duk da haka kuma ba ta haƙura ba, yin abinta take yi. Da farko ma idan Daddy ya ji ta faɗa mata magana yana tsawatar mata duk da ba komai take yi a gabansa ba, dan ya san halinsa. Daga ƙarshe ma da ya ga abun nata ba na ƙare ba ne, lokacin kuma da ita ma Mommahn aka tabbatar tana da nata cikin se ya rabu da ita ta cigaba da haushinta. Musamman da wadda ake yi dan ita abin be taɓa damunta ba daidai da minti ɗaya kuwa.

... "Wai ba ka yi farin ciki da jin namiji zan haifa ba?" Mom ta faɗa tana kallan Daddy. Murmushi ya yi ya nemi waje ya zauna yace

"Na yi mana.. Amma fa kin san ba lallai hakan ne gaskiya ba koh?"

"A'ah wallahi, ni namiji nake so.. kuma shi zan haifa. In Sha Allah se an yi wa Alhaji Matawalle takwara." Kallanta ya yi sosai ganin yanda ta fitittike daga er wannan maganar. Shi ya ɗauka da mace da namiji duk ɗaya ne idan dai Allah Ya baka. Me ye abun damuwa dan ya yi maganar da shi ma ba shi da tabbacinta?

"Toh shi kenan.. Allah Ya ɗayyiba.. Ya kawo shi lafiya." In ji Daddy. Se a lokacin ta yi murmushi tana shafa cikinta tace

"Ameen.. ko kai fa." Daga haka ta miƙe ta fice daga ɗakin, dan ba ta ma so ta cigaba da zama a ɗakin ballantana ya sake yi mata maganar da za ta ɗaga mata hankali.

Kwanaki suka cigaba da tafiya, satika na samuwa, suka kuma bayar da watanni. Har lokacin babu abin da ya chanja cikin gidan. I zuwa lokacin cikin Mommah har ya fito, duk da kasancewarta doguwa hakan be hana cikin nata bayyana sosai ba. Dan kuwa cikin lokaci ƙanƙani ya zarce girman cikin Mom, se ka ɗauka ma ta bata wasu watanni ne, nan kuwa watanninsu ɗaya. Tun daga lokacin Mommah ta ajje fita a gefe. Ya zamana komai za ta yi daga sashenta zuwa sashenta take komai. Shi kansa Daddy hakan ya masa, dan da ma ba kasafai ya cika son haɗuwarsu ba. Se ya zamana rabon da Mommah su haɗu da Mom se da suka ɗauki lokaci me tsayi. Hakan ba ƙaramin damun Mom ya yi ba, dan kuwa har se da ta aika Maimunatu ta gano mata abin da ke faruwa, dan haka kawai hankalinta be kwanta da jin Mommahn shiru ba. Amma haka ta gama gurminta ba ta samu ta ga Mommah ba. Ita kanta abun na bata mamaki, duk kuma sinƙi_sinƙi na ƙwarewarta a gulma haka ta ƙare ta gama ba ta gano komai ba.

.. Mommah na zaune kan kujera sanye cikin wata doguwar riga da ta saketa. Sosai cikinta ya fito se ka ɗauka tana dab da haihuwa ne. Daga fuska kuwa duk da yanda ta ɗan yi ƙiba hakan be hanata yin kyau ba, ta yi wani irin fresh, fatarta ta sake yin haske, kyau da sheƙi. Wayarta da ke gefenta ta yi ƙara, ta saka hannu ta ɗauka tana karawa a kunne. Gaisawa suka yi da Yaya Amina kafin daga bisani tace

"Ya nauyin jiki?" Se da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta kalli cikinta tace

"Alhamdulillah Yaya.. Kin ganni ma a palour yau na samu na zauna."

"Toh Allah Ya ƙara lafiya.. Ki dai samu ki cigaba da motsa jiki."

"In Sha Allah.."

"Kin dai ƙi zuwa a ganar mana abin da za ki haifa koh?" Murmushi Mommah ta yi sannan tace

"Ni Yaya Amina na fi so kawai na haifa, se na fi jin daɗin hakan."

"Ai shi kenan.. Allah dai Ya inganta mana.. Ameen." Murmushi kawai Mommahn ta sake yi daidai lokacin da ta ji motsin shigowa cikin sashen. Ba kuma tare da neman izini ba ta ji ana neman yowa ɗakin.

"Yaya ina zuwa." Ta faɗa tana ajje wayar. Se ta ɗauki mayafi ta lulluɓa a jikinta, daidai lokacin da Mom ta ida shigowa cikin ɗakin. Da mamaki Mommah ke kallanta. Se ta ƙaraso cikin ɗakin tana cigaba da kallan Mommahn da tun shigowarta idanunta ke nuna mata wani abu da ya fi kama da ciki zaune a jikin Mommahn. Kawai se ta ƙarasa kar gaban Mommahn da ke ƙoƙarin miƙewa a hankali saboda nauyin ciki.
Kafin Mommahn ta kai ga miƙewa Mom ta saka hannu ta yaye mayafin da ke jikin Mommahn muryarta har wani rawa take yi tace

"Ke me nake gani a jikinki?" Mom ta faɗa hannunta na rawa. A fusace Mommah ta saka hannunta ta riƙo na Mom daidai lokacin da ta ida miƙewa, ta watsa mata idanunta masu shegen kwarjini tace zuciyarta na tafarfasa

"Ashe da ma ba ki da hankali? Haukan naki be ƙare a iya baki ba har se da hannunki ya taɓa ni, ki ke neman nuna min shi a aikace?"

"Ni ɗin ce nake miki hauka? Lallai ma yarinyar nan.." Mom ta faɗa duk da mamakin Mommahn ya kusa kasheta, gefe guda kuma tsoro da firgici na neman kayar da ita. Me ye ya shiga kanta? Wanne kalar hauka ne a kanta? Wane kalar sakaci ne wannan ta yi? Har wata nawa Mommahn ta ɗauka ɗauke da ciki ba tare da ta sani ba tana nan tana hauka? "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un." Ta faɗa tana jin yanda wani irin jiri ke ɗibarta. Hannu ta saka ta riƙo cikinta da take ji tamkar ɗan cikinta ma ya fuskanci tashin hankalin da ke neman durfafar rayuwarsu.

"Ciki ne da ke? Ciki ki ke ɗauke da shi ban sani ba Sa'adatu?" Mom ta faɗa hawaye sun cika idanunta har gani ma se da ta koma ganin dishi_dishi. Sam ta kasa ɓoye zallar tashin hankalin da ta ji a lokacin. Ta kasa ɓoye tsantsar baƙin cikin da ta tsinci kanta a ciki a yanzun. Mamaki, gami da mugun takaicin halin Mom ɗin ya sa Mom ta kasa tankawa, se tsayawa kawai da ta yi tana kallanta. Jin da Mom ta yi idan ta cigaba da tsayuwa a wajen tabbas za ta iya bajewa ya sanyata juyawa dan ficewa daga ɗakin, duk da yanda jiri ke kwasarta. Komawa Mommah ta yi ta zauna a kan kujerar bayan ficewar Mom daga cikin ɗakin. Ta saka hannu ta dafe kanta da ke sara mata. Wannan wace irin rayuwa ce? Shin Mom ɗin wace irin mata ce ita? Me za ta ƙaru da shi dan wata ta haihu bayan ita ma ba a hanata ba an bata? Shin wace kalar zuciya ce da Mom ɗin haka?.

Ɓangaren Mom kuwa zubewa ta yi a kan gado tana fashewa da kuka. Yau ta gama shiga 3 ta lalace. Wannan wace kalar mummunar rana ce ta zo ta risketa. Ashe da ma Mommahn na ɗauke da ciki amma ba ta taɓa sani ba wai da sunan suna cikin gida ɗaya? Kenan ita ma haihuwa za ta yi kamar yanda za ta haihu? Kenan wace riba za ta ci idan su biyun suka haihu? Kenan duk uban gorin da take mata hakan ya tashi a banza? Ashe ba juya ba ce? Ashe ma ta daɗe tana ɗauke da cikin amma ta mata shiru ta barta tana ta haukanta?

"Yanzu idan ta haifi mace ita kuma Sa'adah ta haifi namiji ya za ta yi? Me ze faru?" Tunanin da ya ɗarsu cikin zuciyarta kenan, wanda ya tilastawa bugun zuciyarta ƙaruwa. Kawai se ta ji hawaye sun tarar mata cikin idanu, a fili ta furta

"Allah kar ka nuna min wannan baƙar ranar." Ta faɗa tana share hawayen. Se kuma ta shiga girgiza kai a filin dai ta cigaba da faɗin

"A'ah.. hakan ma ba ze faru ba. Bayan an tabbatar min da namiji zan haifa, ta yaya kuma zan haifi mace? Hakan ma ba ze taɓa faruwa."

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO63*

___"Lafiya kuwa Hajiya?" Maimuna ta faɗa tana kallan Mom jin sumbatun da take ta yi ita ɗaya. Kawai se ta fashe da kukan da yake fitowa tun daga ƙasan ranta me ɗaci. Da ƙyar ta iya buɗe baki tace

"Maimuna na shiga 3.. Ashe yarinyar nan ciki ne da ita ban taɓa sani ba. Tana nan da tsohon ciki ina nan na sake baki." Sosai Maimuna ke mamakin abin da Mom ɗin take faɗa. Ciki kuma? Amma ba su sani ba? Ta tambayi kanta. Se dai kuma yanzu ba lokacin wannan ba ne idan ta yi la'akari da yanda Mom ɗin take a rikice, hakan ne ya sanyata kwantar da murya tace

"Ki yi haƙuri ki dena damuwa a kan wannan abun. Kin manta likita ya tabbatar miki da cewar namiji za ki haifa? Toh me ye abun damuwa kuma?"
Chapter 71 · 0% Book details