Sashe 35
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
... A hankali ya maida idanunsa kan fuskarta dake kan ƙirjinsa, yanda take ɗan yamutsa baby face ɗinta se ta matuƙar yin kyau. Sauke numfashi ya yi yana jin sanyi a ransa, dan dama tun ɗazun yake ƙoƙarin zameta daga jikinsa amma ta ƙi ba shi haɗin kai, yanzu kuma daga yanda take yamutsa fuska ya fahimci tashi za ta yi daga baccin. A hankali ta ida buɗe idanun nata, se kuma ta yi saurin rufe su sannan ta sake buɗewa. Still dai a kan fuskar Gwani ta sauke idanun nata, sake buɗe idanun ta yi dan tabbatar da abin da idanun nata ke gani. Se dai me? Jinta da ta yi kane_kane a jikin nasa ya sanya ta ji ƙirjinta ya buga lokaci ɗaya kanta na sarawa. Da wani irin sauri da kuzarin da ba ta san tana da shi ba a yanzun ta wani hantsila cikin sakannin da basu wuce 3 ba se ga ta a ƙasa. Duk da faɗuwar da ta yi da kuma yanda wani jiri ya ɗebeta hakan be sanyata haƙura ba se da ta koma gefe ta takure tana jin wani irin kuka na taho mata. Kallanta ya yi a nutse, se kuma ya sauka daga kan gadon jikinsa a sanyaye ya wuce toilet dan ɗaura alwala, zuciyarsa cike fall da tunani barkatai.
Babu jimawa ya fito ya ƙaraso inda take a hankali ya furta
"Ya jikin naki?" Shiru ta yi tana ji kamar ta yi masa shiru, se dai kawai ta buɗe baki ba tare da ta kalle shi ba tace
"Da sauƙi.."
"Allah ya ƙara sauƙi.. Ki tashi ki yi sallah, ki yi wanka za mu je asibiti." Jinjina kai kawai ta yi har lokacin ba ta kalle shi ba, kanta na kan cinyarta duk da yanda take jin gaba ɗaya jikinta na ƙamshin Gwanin nan da suka san shi da shi. Se sauke numfashi take yi tana ɗan mammazewa dan kar ta cigaba da shaƙar ƙamshin nasa, dan har lokacin numfashinta ya ƙi saituwa, ji take kamar har yanzun tana cikin jikinsa ne. Ficewa ya yi daga ɗakin kai tsaye ya wuce masallaci. Tafi minti 2 zaune a wajen bayan fitarsa ba tare da ta motsa ko nan da can ba ne. Se da ta gaji dan kanta duk da har lokacin zazzaɓin jikinta na nan, haka ciwon kan ma na nan, se dai sam ba ta son abin da ze janyo ya sake taɓata, hakan ne ya sanya ta yin iya bakin ƙoƙarinta wajen miƙewa ta wuce toilet ɗin.
... Kallansu Ummeey ta yi lokacin da suka shigo cikin ɗakin tace tana kallan Lulu cike da tausayawa, ganin tun zuwanta gidan har lokacin jikinta ya ƙi daɗi.
"Sannu kin ji en nan.. Allah ya ƙara sauƙi."
"Ameen" Gwani ya amsa da hakan yana miƙewa.
"Ummeey bari mu wuce, kar rana ta yi."
"Ya kamata kam, gwara ku je da wuwwurin, kwa samu ku dawo kafin rana ta ƙwalle." Ummeey ta amsa masa da hakan. Se a lokacin Lulu ta fara ƙoƙarin tashi idanunta a rufe saboda jirin da har yanzun ba ta dena jinsa ba. Ta ɗan yi luu za ta faɗi, lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi kai hannu dan tarota se kuma cikin ikon Allah ta tsaya a kan ƙafafunta.
"Sannu.." Ummeey ta sake faɗa cike da tausayawa. Gaba ta yi yana biye da ita har suka fice daga gidan. Duk iya ƙoƙarinta da jarumtarta ta aro take takawa sanda suka fito ɗin. Shi kam tausaya mata yake yi, ganin lokaci ɗaya ta zabge, ta rame. Se yanzu ya fahimci ita ɗin wace irin yarinya ce, ta cika saka abu a ranta. Yanzu tunda wannan abun ya faru take ta kukan da ya ƙi ƙarewa har ya ja mata ciwon kai, daga nan kuma se zazzaɓi. Ko da yake dole ne ta damu, shi kansa da ba a kansa abin ya faru ba hankalinsa ya ƙi kwanciya, bare kuma ita.
.."Kina ina?" Abeey ya faɗa sanda ya shiga cikin ɗakin. Ummeey ta amsa da
"Gani nan Malam.." ta faɗa tana ƙarasowa inda yake.
"Ai zama be ganki ba, maza ki shirya ki tafi asibitin da yaran nan suka je, kin ji sun riƙe yarinyar se ta kwana."
"Subhanallahi.." Ummeey ta faɗa tana ɗora bayan hannunta a kan haɓarta. Se kuma ta ɗora da
"Toh Allah ya bawa baiwarsa lafiya. Ya kira can gidan nasu ne?" Ta tambaya tana kallan Abeeyn.
"Yana ƙoƙarin kiransu dai yanzu."
"Yawwah toh.. bari na shirya." Ummeey ta faɗa tana komawa cikin ɗakinta dan shiryawa.
.. A nutse ya gaishe da Ammin cike da girmamawa.
"Ya Ummeyn taka? Ya haƙuri da Afaaf?" Ammi ta tambaya saboda sanin halin ɗiyar tata. Se ya yi murmushi kawai ba tare da ya amsa ba. Hakan ne ya sanya Ammi faɗin
"Ka cigaba da haƙuri da ita kaa ji?" Se a lokacin ya buɗe baki yace
"Babu wani abu da take fa.. yanzun ma ba ta jin daɗi ne muna asibiti shi ya sa nace bari na sanar.."
"Subhanallahi.. ya salaam. Wanne asibitin ne?" Ammi ta faɗa a ɗan ruɗe. Be ajje wayar ba se da ya sanar da ita asibitin sannan suka yi sallama ya ajje wayar. Cigaba da zama ya yi natsawon mintuna cikin asibitin, duk yanda ya so haɗuwa da Abbati a yau ɗin hakan ba ze yiwu ba dole se dai ya haƙura. Babu daɗewa Ummeey ta iso asibitin, lokacin Lulun ta yi bacci a kan gadon asibitin. Waje ta nema ta zauna bayan ta je ta duba jikin Lulun. Ta kalli Gwani a nutse tace
"Affan.."
"Na'am Ummeey." Ya amsa da hakan yana kallanta.
"Anya yarinyar nan ba ciki gareta ba kuwa Affan?" Ummeey ta faɗa a sanyaye dan ta gaji da barin tunanin da take yi cikin ranta. Ta san shi ɗin ba sanin laulayin ciki ya yi ba, ita ma kuma Afaaf ɗin ta san ba sani ta yi ba. Dan haka ita dai tana ganin gwara a jarraba tunanin nata. Be san lokacin da dariya ta ƙwace masa ba, kamar ba Gwani ba, se dai ita kanta dariyar cikin natsuwa yake yinta.
"Ka ga mun ja'iri.. Hala kakarka ce ni da za ka zauna ka na min dariya dan na yi magana." Ɗan lumshe idanunsa ya yi kafin yace
"Ummeey ba fa haka ba ne.."
"Likita ne kai Affan? A jarraba gwadata, ka san wasu yaran haka suke fama idan suna da ciki. Sun dinga yin rashin lafiya kenan.. Gwara idan aka gane se a san matakin da za a ɗauka." Ummeey ta ƙare maganar da za ka fahimci da iya gaskiyarta take yinta kuma babu wasa. Ɗan shiru ya yi yana tunanin abin da ze cewa Ummeeyn ta bar wannan maganar, tunda dai shi ya riga ya san babu wani ciki, wata matsalar daban ta janyo mata ciwon. Se dai hatta Ummeeyn ba ya son faɗa mata abin da ya faru ɗin nan, duk da ya san Ummeeyn me fahimta ce a ko da yaushe, amma a irin wannan abun be san da wanne ido za ta kalla ba, shi ya sa ko da wasa ma be yi mata maganar ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO42*
Not edited ☹️
___"Ummeey.." Gwani ya faɗa yana kallanta. itama kallan nasa ta yi daidai lokacin da ya ɗora da faɗin
"Shi kenan toh.. In Sha Allah."
"Yawwah.. toh Allah ya ba da lafiya." Ummeey ta faɗa tana murmushi.
.. Babu daɗewa Ammi da Little suka iso asibitin. Kai tsaye ɗakin da aka kwantar da Lulun suka nufa. Da sallama Ammin ta shiga cikin ɗakin kanta a kan gadon da Lulun ke kwance. Ummeey dake zaune kan kujera ta amsa tana kallan me sallamar. Ganin Little da ta yi ya sanyata sakin murmushi tana faɗin
"Oyoyo Areef.." Se kuwa ya tafi wajenta shi ma yana murmushi daidai lokacin da ta miƙe tana faɗin
"Sannun ku da zuwa.." ta yi maganar tana kallan Ammi. Da murmushi kan fuskar Ammi ta amsa da
"Yawwah.." tana neman waje ta zauna. Cikin mutunta juna suka gaisa kamar sun saba, dan Ummeey na ganin Ammin ta gane wace ce musamman kuma da ta ganta tare da Little. Yayin da Ammi take tunanin wannan ɗin sirikar Lulu ce. Kallan gadon da Lulun ke kai ta yi, tana iya gano fuskarta lokacin da take bacci. Yanda ta ga ta rame shi ne ya sake tabbatar mata da har lokacin ba ta kwantar da hankalinta a kan auren ba. Ta girgiza kai cike da tausayin ɗiyar tata. Daidai lokacin Gwani ya yi sallama cikin ɗakin, dukansu suka amsa masa. Little dake zaune kan gadon kusa da Lulu ya tashi da sauri ya ƙarasa wajensa. Riƙe hannunsa ya yi da murmushi kan fuskarsa yace
"Areef.."
"Na'am ina kwana?" Ya faɗa yana sake riƙe hannun Gwani. Amsa gaisuwar tasa ya yi lokaci ɗaya yana ƙarasawa cikin ɗakin. Cikin girmamawa ya gaishe da Ammi dake zaune kan kujera. Ta kalle shi dan dama ba ta taɓa ganinsa ba. Haka kawai ta ji a jikinta lallai wannan ɗin shi ne mijin Lulu. Ita dai ba ta san dalili ba lokaci ɗaya ta ji ya kwanta mata. Se ta amsa gaisuwar tasa tana ɗorawa da
"Ya me jikin?"
"Alhamdulillah.." Gwani ya amsa da hakan.
"Allah ya ƙara sauƙi.."
"Ameen" ya yi maganar yana miƙewa dan fita daga ɗakin.
... Tsaki ta ja a fili ta furta
"Wai ba za ki ɗaga kiran ba ne?" Ta yi maganar kamar akwai wani a kusa da ita wanda ze amsa mata maganar da ta yi. Se dai kafin wayar ta tsinke aka ɗaga. Daga can ɓangaren Aunt Makiyy tace
"Yi haƙuri 'yar uwata.. Allah ya huci zuciyarki." Ta yi maganar tana er dariya. Tsaki Mom ta ja a fusace tace
"Wallahi na gama fusata kuwa, dan rashin kirki in yi ta kiran ki ki ƙi ɗagawa.."
"Ai dai na bayar da haƙuri.." Aunt Makiyy ta faɗa. Se a lokacin sannan Mom tace
"Toh na ji.. Yanzu dai ya ake ciki? Na ji ki shiru har yanzu, ko kina nufin har yanzu ba a zo lokacin da kike so a zo ba?"
"Kai Yaya don Allah ki yi haƙuri mana, ki bari mu bi komai a sannu.."
Babu jimawa ya fito ya ƙaraso inda take a hankali ya furta
"Ya jikin naki?" Shiru ta yi tana ji kamar ta yi masa shiru, se dai kawai ta buɗe baki ba tare da ta kalle shi ba tace
"Da sauƙi.."
"Allah ya ƙara sauƙi.. Ki tashi ki yi sallah, ki yi wanka za mu je asibiti." Jinjina kai kawai ta yi har lokacin ba ta kalle shi ba, kanta na kan cinyarta duk da yanda take jin gaba ɗaya jikinta na ƙamshin Gwanin nan da suka san shi da shi. Se sauke numfashi take yi tana ɗan mammazewa dan kar ta cigaba da shaƙar ƙamshin nasa, dan har lokacin numfashinta ya ƙi saituwa, ji take kamar har yanzun tana cikin jikinsa ne. Ficewa ya yi daga ɗakin kai tsaye ya wuce masallaci. Tafi minti 2 zaune a wajen bayan fitarsa ba tare da ta motsa ko nan da can ba ne. Se da ta gaji dan kanta duk da har lokacin zazzaɓin jikinta na nan, haka ciwon kan ma na nan, se dai sam ba ta son abin da ze janyo ya sake taɓata, hakan ne ya sanya ta yin iya bakin ƙoƙarinta wajen miƙewa ta wuce toilet ɗin.
... Kallansu Ummeey ta yi lokacin da suka shigo cikin ɗakin tace tana kallan Lulu cike da tausayawa, ganin tun zuwanta gidan har lokacin jikinta ya ƙi daɗi.
"Sannu kin ji en nan.. Allah ya ƙara sauƙi."
"Ameen" Gwani ya amsa da hakan yana miƙewa.
"Ummeey bari mu wuce, kar rana ta yi."
"Ya kamata kam, gwara ku je da wuwwurin, kwa samu ku dawo kafin rana ta ƙwalle." Ummeey ta amsa masa da hakan. Se a lokacin Lulu ta fara ƙoƙarin tashi idanunta a rufe saboda jirin da har yanzun ba ta dena jinsa ba. Ta ɗan yi luu za ta faɗi, lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi kai hannu dan tarota se kuma cikin ikon Allah ta tsaya a kan ƙafafunta.
"Sannu.." Ummeey ta sake faɗa cike da tausayawa. Gaba ta yi yana biye da ita har suka fice daga gidan. Duk iya ƙoƙarinta da jarumtarta ta aro take takawa sanda suka fito ɗin. Shi kam tausaya mata yake yi, ganin lokaci ɗaya ta zabge, ta rame. Se yanzu ya fahimci ita ɗin wace irin yarinya ce, ta cika saka abu a ranta. Yanzu tunda wannan abun ya faru take ta kukan da ya ƙi ƙarewa har ya ja mata ciwon kai, daga nan kuma se zazzaɓi. Ko da yake dole ne ta damu, shi kansa da ba a kansa abin ya faru ba hankalinsa ya ƙi kwanciya, bare kuma ita.
.."Kina ina?" Abeey ya faɗa sanda ya shiga cikin ɗakin. Ummeey ta amsa da
"Gani nan Malam.." ta faɗa tana ƙarasowa inda yake.
"Ai zama be ganki ba, maza ki shirya ki tafi asibitin da yaran nan suka je, kin ji sun riƙe yarinyar se ta kwana."
"Subhanallahi.." Ummeey ta faɗa tana ɗora bayan hannunta a kan haɓarta. Se kuma ta ɗora da
"Toh Allah ya bawa baiwarsa lafiya. Ya kira can gidan nasu ne?" Ta tambaya tana kallan Abeeyn.
"Yana ƙoƙarin kiransu dai yanzu."
"Yawwah toh.. bari na shirya." Ummeey ta faɗa tana komawa cikin ɗakinta dan shiryawa.
.. A nutse ya gaishe da Ammin cike da girmamawa.
"Ya Ummeyn taka? Ya haƙuri da Afaaf?" Ammi ta tambaya saboda sanin halin ɗiyar tata. Se ya yi murmushi kawai ba tare da ya amsa ba. Hakan ne ya sanya Ammi faɗin
"Ka cigaba da haƙuri da ita kaa ji?" Se a lokacin ya buɗe baki yace
"Babu wani abu da take fa.. yanzun ma ba ta jin daɗi ne muna asibiti shi ya sa nace bari na sanar.."
"Subhanallahi.. ya salaam. Wanne asibitin ne?" Ammi ta faɗa a ɗan ruɗe. Be ajje wayar ba se da ya sanar da ita asibitin sannan suka yi sallama ya ajje wayar. Cigaba da zama ya yi natsawon mintuna cikin asibitin, duk yanda ya so haɗuwa da Abbati a yau ɗin hakan ba ze yiwu ba dole se dai ya haƙura. Babu daɗewa Ummeey ta iso asibitin, lokacin Lulun ta yi bacci a kan gadon asibitin. Waje ta nema ta zauna bayan ta je ta duba jikin Lulun. Ta kalli Gwani a nutse tace
"Affan.."
"Na'am Ummeey." Ya amsa da hakan yana kallanta.
"Anya yarinyar nan ba ciki gareta ba kuwa Affan?" Ummeey ta faɗa a sanyaye dan ta gaji da barin tunanin da take yi cikin ranta. Ta san shi ɗin ba sanin laulayin ciki ya yi ba, ita ma kuma Afaaf ɗin ta san ba sani ta yi ba. Dan haka ita dai tana ganin gwara a jarraba tunanin nata. Be san lokacin da dariya ta ƙwace masa ba, kamar ba Gwani ba, se dai ita kanta dariyar cikin natsuwa yake yinta.
"Ka ga mun ja'iri.. Hala kakarka ce ni da za ka zauna ka na min dariya dan na yi magana." Ɗan lumshe idanunsa ya yi kafin yace
"Ummeey ba fa haka ba ne.."
"Likita ne kai Affan? A jarraba gwadata, ka san wasu yaran haka suke fama idan suna da ciki. Sun dinga yin rashin lafiya kenan.. Gwara idan aka gane se a san matakin da za a ɗauka." Ummeey ta ƙare maganar da za ka fahimci da iya gaskiyarta take yinta kuma babu wasa. Ɗan shiru ya yi yana tunanin abin da ze cewa Ummeeyn ta bar wannan maganar, tunda dai shi ya riga ya san babu wani ciki, wata matsalar daban ta janyo mata ciwon. Se dai hatta Ummeeyn ba ya son faɗa mata abin da ya faru ɗin nan, duk da ya san Ummeeyn me fahimta ce a ko da yaushe, amma a irin wannan abun be san da wanne ido za ta kalla ba, shi ya sa ko da wasa ma be yi mata maganar ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO42*
Not edited ☹️
___"Ummeey.." Gwani ya faɗa yana kallanta. itama kallan nasa ta yi daidai lokacin da ya ɗora da faɗin
"Shi kenan toh.. In Sha Allah."
"Yawwah.. toh Allah ya ba da lafiya." Ummeey ta faɗa tana murmushi.
.. Babu daɗewa Ammi da Little suka iso asibitin. Kai tsaye ɗakin da aka kwantar da Lulun suka nufa. Da sallama Ammin ta shiga cikin ɗakin kanta a kan gadon da Lulun ke kwance. Ummeey dake zaune kan kujera ta amsa tana kallan me sallamar. Ganin Little da ta yi ya sanyata sakin murmushi tana faɗin
"Oyoyo Areef.." Se kuwa ya tafi wajenta shi ma yana murmushi daidai lokacin da ta miƙe tana faɗin
"Sannun ku da zuwa.." ta yi maganar tana kallan Ammi. Da murmushi kan fuskar Ammi ta amsa da
"Yawwah.." tana neman waje ta zauna. Cikin mutunta juna suka gaisa kamar sun saba, dan Ummeey na ganin Ammin ta gane wace ce musamman kuma da ta ganta tare da Little. Yayin da Ammi take tunanin wannan ɗin sirikar Lulu ce. Kallan gadon da Lulun ke kai ta yi, tana iya gano fuskarta lokacin da take bacci. Yanda ta ga ta rame shi ne ya sake tabbatar mata da har lokacin ba ta kwantar da hankalinta a kan auren ba. Ta girgiza kai cike da tausayin ɗiyar tata. Daidai lokacin Gwani ya yi sallama cikin ɗakin, dukansu suka amsa masa. Little dake zaune kan gadon kusa da Lulu ya tashi da sauri ya ƙarasa wajensa. Riƙe hannunsa ya yi da murmushi kan fuskarsa yace
"Areef.."
"Na'am ina kwana?" Ya faɗa yana sake riƙe hannun Gwani. Amsa gaisuwar tasa ya yi lokaci ɗaya yana ƙarasawa cikin ɗakin. Cikin girmamawa ya gaishe da Ammi dake zaune kan kujera. Ta kalle shi dan dama ba ta taɓa ganinsa ba. Haka kawai ta ji a jikinta lallai wannan ɗin shi ne mijin Lulu. Ita dai ba ta san dalili ba lokaci ɗaya ta ji ya kwanta mata. Se ta amsa gaisuwar tasa tana ɗorawa da
"Ya me jikin?"
"Alhamdulillah.." Gwani ya amsa da hakan.
"Allah ya ƙara sauƙi.."
"Ameen" ya yi maganar yana miƙewa dan fita daga ɗakin.
... Tsaki ta ja a fili ta furta
"Wai ba za ki ɗaga kiran ba ne?" Ta yi maganar kamar akwai wani a kusa da ita wanda ze amsa mata maganar da ta yi. Se dai kafin wayar ta tsinke aka ɗaga. Daga can ɓangaren Aunt Makiyy tace
"Yi haƙuri 'yar uwata.. Allah ya huci zuciyarki." Ta yi maganar tana er dariya. Tsaki Mom ta ja a fusace tace
"Wallahi na gama fusata kuwa, dan rashin kirki in yi ta kiran ki ki ƙi ɗagawa.."
"Ai dai na bayar da haƙuri.." Aunt Makiyy ta faɗa. Se a lokacin sannan Mom tace
"Toh na ji.. Yanzu dai ya ake ciki? Na ji ki shiru har yanzu, ko kina nufin har yanzu ba a zo lokacin da kike so a zo ba?"
"Kai Yaya don Allah ki yi haƙuri mana, ki bari mu bi komai a sannu.."