Sashe 98
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
... Washegari haka sirr ya wuni be sanyata cikin idanunsa ba. A hankali ya saukar da ƙafarsa ƙasa daga kan gadon da yake. Ya lumshe idanunsa lokaci ɗaya yana cusa hannayensa duka biyun cikin sumar kansa. Gaba ɗaya al'amarinsa neman taɓarɓarewa yake yi. Mace na neman saka masa hauka. Ji yake kamar ya fita ko ma ina ne ya nemo wani abun ya zo ya bankawa kansa ko ze ji sauƙi. Se dai wani ɓangaren na zuciyarsa ya ƙi yin na'am da hakan. Daga zarar ya raya hakan se Mommah ta faɗo masa. Zazzafar iska ya fitar daga bakinsa yana miƙewa. Ya ɗauki rigarsa da ke gefensa ya zura, ya saka haɗaɗɗen tsadadden takalminsa ya fice daga ɗakin. Abin da be taɓa tsammata ba, se ga shi a bakin sashen Mommahn ya hangeta. Daga nesa ya sake buɗe idanunsa yana fatan ba idanunsa ke gizo ba, ko kuma er uwatta ce ya gani. Se da ya ɗan sake matsawa ɗin kuwa sannan ya tabbatar da tabbas ita ɗin ce. Ya lumshe idanunsa ya buɗe, kana da sauri ya ƙarasa inda take. Ya sha gabanta lokacin da take ƙoƙarin shigewa sashen. Dakatawa ta yi tana jin jikinta ya yi sanyi. Ita kam wannan mutumin ta shiga uku da shi. Ba ta iya ɗaga ido ta kalle shi ba, se yin shiru kawai da ta yi tana jira ta ji yau kuma da me ya zo. Da so samu ne su yi wata maganar ba wannan ba, se dai ba ya so Mommah ta gan shi ballantana tace ba ya jin magana. Hakan ne ya sanya shi tamke fuskarsa kamar yanda ya saba a da idan ze mata magana. Dan gani yake hakan ne kaɗai ze sa ta ji maganar da ze mata.
"Ki kawo min Coffee.. Kar ki kawo min maganar Mommah dan ba karɓa zan yi ba. Ina nan ina jiranki a ɗakina, kar kuma ki sake ki sanarwa da Mommah." Ba ta san me ya gani ba ita dai ta ga ya yi saurin bi ta baya ya bar wajen. Se da ta ji maganar Mommah na faɗin
"Daughter.. lafiya?" Sannan ta yi saurin girgiza kai tana faɗin
"A'ah Mommah babu komai." Ta ƙare tana ƙaƙalo murmushi a kan fuskarta. Daga haka suka wuce cikin ɗakin tare da Mommahn.
... Ya fi minti 30 yana zagaye cikin ɗakin, yana jiran shigowar Didi. Dan ya saka a ransa ko me za ta yi yau cikin ɗakin za ta kwana ko ya samu ya fanshe kallanta da be samu ya yi ba jiya da yau. A karo na barkatai ya sake kallan agogo ya duba lokaci, har lokacin babu ita babu dalilinta. Har bayan Sallahr maghrib shiru babu Didi babu alamunta. Kenan me ta cigaba da zama ta yi a sashen Mommah? Ko dai Mommah ta san ya sakata aikin nan ne? Ko kuma ita ta sanar da Mommahn? Ya kaasa haƙuri har ga Allah zuciyarsa azalzalzalarsa take yi, hakan ne ya sa ya miƙe kawai ya fice daga ɗakin zuwa sashen Mommah. A madaidaicin palourn da za ka fara tararwa kafin ka kai ga ainahin palourn Mommah ya sameta tana shirin shiga palournta. Se ya dakata yana ji kamar ya koma, se dai kawai ya basar yace
"Barka da wannan lokaci Mommah.."
"Barka dai Son.." Mommah ta amsa da hakan.
"Amma kamar na ce maka ka dakata da shigowa ɗakin nan idan ba na nan koh?" Ɗaga idanunsa ya yi ya kalli Mommahn a narke ko da hakan ze sa ta ji tausayinsa. Yace a sanyaye
"Ki yi haƙuri Mommah.. ba tare da saninki ba na sakata kai min Coffee ne.. So na ji shiru shi ne na biyo baya.. Ban da haka babu komai wallahi."
"Wai me kake nufi da yarinyar nan ne? Na ɗauka ka ce ba ka sonta koh? Toh mun ji kuma mun amince, me ye kuma ya yi saura? Me ye na duk wannan shishshige matan?" Mommah ta faɗa fuskarta a haɗe, dan so take da gasken ta koya masa hankali. Runtse idanunsa ya yi kafin ya buɗe, ya ɗauki wajen second 30 kafin yace
"Mommah.. Don Allah ki dena tuna abin da ya wuce.. Wallahi ina sonta yanzu.. Don Allah ki bar ni ko da ganinta ne na yi." Ya ƙare a marairaice kai ba kace Bad Man ne ba. Shi sam ya ma manta akwai kunya a irin wannan maganar da ya faɗawa Mommahn. Shi dai kawai so yake Mommah ta yadda ya tuba, yana kuma son matarsa yanzun. Ɗauke kanta Mommah ta yi lokacin da murmushi ya suɓuce mata. Se kuma ta juyo bayan ta maida fuskarta kamar ɗazun tace bayan ta yi murmushi kamar na yaƙe
"Ka dena yaudarar kanka Areef.. Ka riga ka yi sake, dan haka ka shirya rubuta mata takardar saki dan kuwa daga nan se gidansu. Yarinya da gatanta ba aura maka ita aka yi dan ba a sonta ba." Be san lokacin da ya ɗaga idanunsa ya kalli Mommahn da sauri ba. Kallanta kawai yake yi yana ji kamar ta yi wani saɓo ne. Da gaske take tana nufin abin da ta faɗa? Wai an ya kuwa yanzu Mommah na ƙaunarsa? Ya tambayi kansa lokacin da idanunsa suka kaɗa, zuciyarsa na wani irin harbawa. Se dai ya kaasa furta komai. Shi kansa wannan lamari ya shammace shi, be taɓa tunanin watarana ze tsinci kansa cikin ƙaunar yarinyar ba. Shin mene ne mafita? Ze iya sakin nata ko kuwa?
"Mommah.." Ya sake faɗa murya a sanyaye. Ɗaga masa hannu Mommah ta yi tace
"Na gama magana Areef.. Ka je zan nemeka" Daga haka ta miƙe ta wuce cikin ainahin palournta. Dafa kujerar gefensa ya yi yana runtse idanunsa. A fili numfashinsa ya shiga fita da sauri da sauri har kuma lokacin be buɗe idanunsa ba. Me ye mafita? Ya tambayi kansa. Ya kai wajen minti 2 a haka kafin ya buɗe idanunsa lokacin da suka rine suka yi jajir. Se a lokacin ya bi inda Mommah ta yi da kallo sannan ya ɗaga ƙafafunsa cike da sassarfa ya fice daga ɗakin.
.. Kai tsaye ɗakin da su Didi ke ciki Mommah ta wuce, da ma Didi take son magana da ita. Se kuwa ta sameta zaune a kan kujerar ɗakin ta yi shiru kamar me tunani. Ƙarasawa Mommah ta yi ta zauna, Didi ta yi murmushi tana gaidata. Ta amsa cikin kulawa kafin tace
"Afrah.."
"Na'am Mommah.." Didi ta amsa da hakan tana tattaro duk wani hankalinta ta bawa Mommahn. Saboda jin yanda ta kira sunanta ta san muhimmiyar magana ce za ta mata.
"Wato duk da na kasance mahaifiya ga Areef amma har yanzu ba na goyon bayan halayensa. Wannan shi ne lokacin da ya dace, ina nufin wannan ce damar da kike da ita da za ki ƙwatowa kanki 'yanci. Yana sonki yanzun dan haka ina neman alfarma a wajenki don Allah ki yi amfani da wannan soyayyar da yake miki wajen taya ni ƙwato shi daga ɗabi'ar nan ta.." Se ta yi shiru ba tare da ta ƙarasa ba, dan yanda ma ta ƙarasa maganar kaɗai ya isa ya nuna maka yanda zuciyarta ta karye. Narkakkun idanunta Didi ta ɗaga ta kalli Mommah. Ta fahimci abin da take nufi dan haka babu amfanin ma se ta ƙarasa. Ita kanta da take amsa sunan matarsa ita kaɗai ta san takaicin hakan da take ji. Ballantana mahaifiyar da ta haife shi. Wadda ta ɗauki tsayin shekaru ba tare da shi a matsayin ɗanta ba. Ga shi kuma yanzun ya bayyana se dai da wata ɗabi'ar da babu wanda ze so ko waye na sa ya kasance da ita.
"Ki dena damuwa Mommah.. In Sha Allah zan yi duk abin da kika ce.. Kuma In Sha Allah Allah ze shirye shi.." Didi ta faɗa ita ma cikin karyayyiyar murya. Murmushi Mommah ta yi kafin ta kamo hannun Didin tace
"Allah Ya yi miki albarka. Ya daidaita tsakaninku nan ba da daɗewa ba. Ya saka miki da alkhairi, Ameen." Ba ta daɗe ba Mommahn ta fice daga ɗakin. Didi ta jinginar da kanta jikin kujera tana ji zuciyarta na sake karyewa.
"Allah Ka taimake ni, Ka shiryi bawan nan naka Ya Allah.." Ta ƙare tana runtse idanunta. Ba ta tsammata ba, se jin zaunawar Lulun kawai ta yi a gabanta da ƙarfi tana dariya hannunta a kan cinyarta. Buɗe ido ta yi da sauri ta kalleta tace a tsorace
"Me ye haka Lulu? Ba ki san yanzu ba ke kaɗai ba ce? Shi ne kike irin wannan abun.. me ye haka?" Ta ƙare tana riƙo hannunta ta ɗagata ta koma kusa da ita. Turo baki Lulu ta yi, ita fa sun fara takura mata, ko me ta yi se su ce wai ba ita kaɗai ba ce yanzu. Toh ashe ma ba sa ta kanta se ta abin cikin nata.
"Da ma Didi ba ta ni kike ba koh?" Ta yi maganar da iya gaskiyarta. Girgiza kai Didi ta yi dan ta lura ita har cikin ranta da gaske take.
"Ke ba fa haka ba ne.. Kin ga shi ai yanzu dole se an kula da shi saboda ingantarsa. Se kin dinga kula sosai Lulu don Allah, ko kuma ki na so mu rasa shi ne?" A hankali kuma se ta kai hannunta kan cikinta kamar wadda za ta jiyo motsin yaron tun yanzun. A sukwane ta girgiza kai tana kallan Didin. Murmushi Didi ta yi kafin tace
"Yawwah.."
"Toh wai da ma ki na son Areef ɗin ne?" Lulu ta faɗi abin da ke ranta tun ɗazun. Da sauri Didi ta buɗe idanunta tana kallan Lulun cike da mamakin dalilinta na faɗin haka.
"Me ya sa kika ce haka?"
"Toh gani na yi ki na ta masa addu'a hadda su kuka." Riƙe haɓa Didi ta yi ta shiga jinjina kai tana faɗin
"Iyeeee.. haka kika shahara Lulu."
"Toh ki ce ƙarya ne mana." Lulu ta yi maganar tana ɗage gira. Ta san yanzu ko me za ta cewa Lulun ba yadda za ta yi ba. Ƙila ma ta maida abin na tsokana.
"Ki kawo min Coffee.. Kar ki kawo min maganar Mommah dan ba karɓa zan yi ba. Ina nan ina jiranki a ɗakina, kar kuma ki sake ki sanarwa da Mommah." Ba ta san me ya gani ba ita dai ta ga ya yi saurin bi ta baya ya bar wajen. Se da ta ji maganar Mommah na faɗin
"Daughter.. lafiya?" Sannan ta yi saurin girgiza kai tana faɗin
"A'ah Mommah babu komai." Ta ƙare tana ƙaƙalo murmushi a kan fuskarta. Daga haka suka wuce cikin ɗakin tare da Mommahn.
... Ya fi minti 30 yana zagaye cikin ɗakin, yana jiran shigowar Didi. Dan ya saka a ransa ko me za ta yi yau cikin ɗakin za ta kwana ko ya samu ya fanshe kallanta da be samu ya yi ba jiya da yau. A karo na barkatai ya sake kallan agogo ya duba lokaci, har lokacin babu ita babu dalilinta. Har bayan Sallahr maghrib shiru babu Didi babu alamunta. Kenan me ta cigaba da zama ta yi a sashen Mommah? Ko dai Mommah ta san ya sakata aikin nan ne? Ko kuma ita ta sanar da Mommahn? Ya kaasa haƙuri har ga Allah zuciyarsa azalzalzalarsa take yi, hakan ne ya sa ya miƙe kawai ya fice daga ɗakin zuwa sashen Mommah. A madaidaicin palourn da za ka fara tararwa kafin ka kai ga ainahin palourn Mommah ya sameta tana shirin shiga palournta. Se ya dakata yana ji kamar ya koma, se dai kawai ya basar yace
"Barka da wannan lokaci Mommah.."
"Barka dai Son.." Mommah ta amsa da hakan.
"Amma kamar na ce maka ka dakata da shigowa ɗakin nan idan ba na nan koh?" Ɗaga idanunsa ya yi ya kalli Mommahn a narke ko da hakan ze sa ta ji tausayinsa. Yace a sanyaye
"Ki yi haƙuri Mommah.. ba tare da saninki ba na sakata kai min Coffee ne.. So na ji shiru shi ne na biyo baya.. Ban da haka babu komai wallahi."
"Wai me kake nufi da yarinyar nan ne? Na ɗauka ka ce ba ka sonta koh? Toh mun ji kuma mun amince, me ye kuma ya yi saura? Me ye na duk wannan shishshige matan?" Mommah ta faɗa fuskarta a haɗe, dan so take da gasken ta koya masa hankali. Runtse idanunsa ya yi kafin ya buɗe, ya ɗauki wajen second 30 kafin yace
"Mommah.. Don Allah ki dena tuna abin da ya wuce.. Wallahi ina sonta yanzu.. Don Allah ki bar ni ko da ganinta ne na yi." Ya ƙare a marairaice kai ba kace Bad Man ne ba. Shi sam ya ma manta akwai kunya a irin wannan maganar da ya faɗawa Mommahn. Shi dai kawai so yake Mommah ta yadda ya tuba, yana kuma son matarsa yanzun. Ɗauke kanta Mommah ta yi lokacin da murmushi ya suɓuce mata. Se kuma ta juyo bayan ta maida fuskarta kamar ɗazun tace bayan ta yi murmushi kamar na yaƙe
"Ka dena yaudarar kanka Areef.. Ka riga ka yi sake, dan haka ka shirya rubuta mata takardar saki dan kuwa daga nan se gidansu. Yarinya da gatanta ba aura maka ita aka yi dan ba a sonta ba." Be san lokacin da ya ɗaga idanunsa ya kalli Mommahn da sauri ba. Kallanta kawai yake yi yana ji kamar ta yi wani saɓo ne. Da gaske take tana nufin abin da ta faɗa? Wai an ya kuwa yanzu Mommah na ƙaunarsa? Ya tambayi kansa lokacin da idanunsa suka kaɗa, zuciyarsa na wani irin harbawa. Se dai ya kaasa furta komai. Shi kansa wannan lamari ya shammace shi, be taɓa tunanin watarana ze tsinci kansa cikin ƙaunar yarinyar ba. Shin mene ne mafita? Ze iya sakin nata ko kuwa?
"Mommah.." Ya sake faɗa murya a sanyaye. Ɗaga masa hannu Mommah ta yi tace
"Na gama magana Areef.. Ka je zan nemeka" Daga haka ta miƙe ta wuce cikin ainahin palournta. Dafa kujerar gefensa ya yi yana runtse idanunsa. A fili numfashinsa ya shiga fita da sauri da sauri har kuma lokacin be buɗe idanunsa ba. Me ye mafita? Ya tambayi kansa. Ya kai wajen minti 2 a haka kafin ya buɗe idanunsa lokacin da suka rine suka yi jajir. Se a lokacin ya bi inda Mommah ta yi da kallo sannan ya ɗaga ƙafafunsa cike da sassarfa ya fice daga ɗakin.
.. Kai tsaye ɗakin da su Didi ke ciki Mommah ta wuce, da ma Didi take son magana da ita. Se kuwa ta sameta zaune a kan kujerar ɗakin ta yi shiru kamar me tunani. Ƙarasawa Mommah ta yi ta zauna, Didi ta yi murmushi tana gaidata. Ta amsa cikin kulawa kafin tace
"Afrah.."
"Na'am Mommah.." Didi ta amsa da hakan tana tattaro duk wani hankalinta ta bawa Mommahn. Saboda jin yanda ta kira sunanta ta san muhimmiyar magana ce za ta mata.
"Wato duk da na kasance mahaifiya ga Areef amma har yanzu ba na goyon bayan halayensa. Wannan shi ne lokacin da ya dace, ina nufin wannan ce damar da kike da ita da za ki ƙwatowa kanki 'yanci. Yana sonki yanzun dan haka ina neman alfarma a wajenki don Allah ki yi amfani da wannan soyayyar da yake miki wajen taya ni ƙwato shi daga ɗabi'ar nan ta.." Se ta yi shiru ba tare da ta ƙarasa ba, dan yanda ma ta ƙarasa maganar kaɗai ya isa ya nuna maka yanda zuciyarta ta karye. Narkakkun idanunta Didi ta ɗaga ta kalli Mommah. Ta fahimci abin da take nufi dan haka babu amfanin ma se ta ƙarasa. Ita kanta da take amsa sunan matarsa ita kaɗai ta san takaicin hakan da take ji. Ballantana mahaifiyar da ta haife shi. Wadda ta ɗauki tsayin shekaru ba tare da shi a matsayin ɗanta ba. Ga shi kuma yanzun ya bayyana se dai da wata ɗabi'ar da babu wanda ze so ko waye na sa ya kasance da ita.
"Ki dena damuwa Mommah.. In Sha Allah zan yi duk abin da kika ce.. Kuma In Sha Allah Allah ze shirye shi.." Didi ta faɗa ita ma cikin karyayyiyar murya. Murmushi Mommah ta yi kafin ta kamo hannun Didin tace
"Allah Ya yi miki albarka. Ya daidaita tsakaninku nan ba da daɗewa ba. Ya saka miki da alkhairi, Ameen." Ba ta daɗe ba Mommahn ta fice daga ɗakin. Didi ta jinginar da kanta jikin kujera tana ji zuciyarta na sake karyewa.
"Allah Ka taimake ni, Ka shiryi bawan nan naka Ya Allah.." Ta ƙare tana runtse idanunta. Ba ta tsammata ba, se jin zaunawar Lulun kawai ta yi a gabanta da ƙarfi tana dariya hannunta a kan cinyarta. Buɗe ido ta yi da sauri ta kalleta tace a tsorace
"Me ye haka Lulu? Ba ki san yanzu ba ke kaɗai ba ce? Shi ne kike irin wannan abun.. me ye haka?" Ta ƙare tana riƙo hannunta ta ɗagata ta koma kusa da ita. Turo baki Lulu ta yi, ita fa sun fara takura mata, ko me ta yi se su ce wai ba ita kaɗai ba ce yanzu. Toh ashe ma ba sa ta kanta se ta abin cikin nata.
"Da ma Didi ba ta ni kike ba koh?" Ta yi maganar da iya gaskiyarta. Girgiza kai Didi ta yi dan ta lura ita har cikin ranta da gaske take.
"Ke ba fa haka ba ne.. Kin ga shi ai yanzu dole se an kula da shi saboda ingantarsa. Se kin dinga kula sosai Lulu don Allah, ko kuma ki na so mu rasa shi ne?" A hankali kuma se ta kai hannunta kan cikinta kamar wadda za ta jiyo motsin yaron tun yanzun. A sukwane ta girgiza kai tana kallan Didin. Murmushi Didi ta yi kafin tace
"Yawwah.."
"Toh wai da ma ki na son Areef ɗin ne?" Lulu ta faɗi abin da ke ranta tun ɗazun. Da sauri Didi ta buɗe idanunta tana kallan Lulun cike da mamakin dalilinta na faɗin haka.
"Me ya sa kika ce haka?"
"Toh gani na yi ki na ta masa addu'a hadda su kuka." Riƙe haɓa Didi ta yi ta shiga jinjina kai tana faɗin
"Iyeeee.. haka kika shahara Lulu."
"Toh ki ce ƙarya ne mana." Lulu ta yi maganar tana ɗage gira. Ta san yanzu ko me za ta cewa Lulun ba yadda za ta yi ba. Ƙila ma ta maida abin na tsokana.