Sashe 115
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ehh Ummeey.. Ina tunanin na zauna saboda kar ki buƙaci wani abu kuma ba na kusa." Gwani ya faɗa. Girgiza kai Ummeey ta yi kafin tace
"A'ah, yau ɗin ma In Allah Ya yarda ba zan nemi komai ba.. Ai ba za ka bar 'yata ita ɗaya ba. Ku je Allah Ya muku albarka."
"Ameen." Suka amsa kusan a tare, kafin su ma suka mata sallama kana suka fice.
.. Tun ɗazu yake lura da ita, yanda yanayin tafiyarta ya sauya.
"Didi" Lulu da ke gefenta ta kira sunanta. Sake dafe kanta ta yi tana lumshe idanunta. Se dai duk da haka ba ta dena takawa ba. Wani jiri da ya kwashe ta shi ya tilasta mata dakatawa, ba tare da ta ankara ba ta tafi da niyyar zubewa. Ya yi saurin ƙarasawa ya saka hannunsa, hakan ne ya sanya ta faɗawa jikinsa. Ajiyar zuciya ya sauke lokaci guda ƙirjinsa na bugawa dan babu ƙarya ya tsorata. Gwani da Lulu kansu sun tsorata, dalili kenan da ya sanya dukkansu su ma suka dakata. Hannu Bad Man ya saka ya tallafo fuskarta da idanunta ke a rufe, dan ita kanta ta tsorata. Cikin kulawa yace
"Babe!" Se a lokacin ta shiga buɗe idanunta, ƙirjinta na harbawa da ƙarfi. Tashi ta soma ƙoƙarin yi, ya barta ta miƙe amma duk da haka tana jikinsa.
"Da ma ba ki da lafiya shi ne ba ki sanar da ni ba?" Ya tambaya yana kafe ta da idanunsa da suka ɗan sauya. Girgiza kai ta yi cike da gaskiyarta tace
"Lafiyata ƙalau." Iska ya fesar yana runtse idanunsa. Ya buɗe su yana kallan nata dai.
"Ba ki da lafiya.." Ya faɗa kamar shi ke da jikinta.
"Lafiyata.."
"Shhh.." Ya faɗa yana ɗora hannunsa a kan bakinsa. Kawai se ta yi shiru ta cigaba da kallan yanda cikin ƙanƙanin lokaci yanayinsa gaba ɗaya ya sauya. Kai ba za ka taɓa cewa shi ne ɗazun ba. Ita dai ba ta sake cewa komai ba har zuwa lokacin da ya miƙar da ita sosai.
"Bro za mu koma asibitin, ku ƙarasa kawai.." Bin Didi da kallo kawai Lulu take yi da idanunta da ita ma suka sauya, cike da tunanin abin da ke damun er uwar tata.
"Allah Ya ƙara sauƙi." Gwani ya faɗa.
"Ameen." Bad Man ya amsa da hakan yana juyawa, ya kama hannun Didi suka fice daga cikin hotel ɗin da ba su yi nisa da shigo shi ba.
"Mu je koh?" Gwani ya faɗa yana kallan Lulu da ta bi su da kallo. Ganin yanda duk ita ma yanayinta ya sauya ne ya sanya shi ƙarasawa kusa da ita sosai. Cikin rarrashi yace
"Ki kwantar da hankalinki, babu abin da ze faru In Sha Allah.." Ya yi maganar yana kallanta sosai.
"Didina ba ta.."
"Kar ki ce komai.. Babu abin da ze faru Uhmm?" Se da ta sauke wani dogon numfashi kafin ta jinjina kanta jiki a sanyaye. Haka suka ƙarasa ɗakinsu zuciyarta fall tunanin Didinta.
.. "Ina taya ka murna, matarka na ɗauke da juna biyu.." Shi ne bayanin da likitar ta faɗa masa bayan gwajin da aka yi wa Didi. Kallan likitar yake yi lokacin da take bayanin, amma be san lokacin da idanunsa suka koma kan Didi ba. Tun daga nan kuma be sake fahimtar abin da take faɗa ba. Ita ma Didi kanta kallansa take yi, tana jin abun kamar a mafarki. Da gaske matar take ciki ne da ita? Lallai Allah me iko. Ba ta san lokacin da Bad ya ƙaraso inda take ba, se ji ta yi kawai an ɗaga ta gaba ɗaya ana juyi da ita cikin ɗakin. Cikin matuƙar farin ciki ya rungume ta yana ji kamar ya maida ta cikinsa. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin ya sauketa a kan kujerar da ya ɗauke ta daga kai, ya sake zuba mata idanunsa da kalarsu ta chanja. Iya su kaɗai ko fuskarsa kaɗai za ka kalla ka fahimci farin cikin da yake ciki. Ya kasa furta komai, jin abin yake kamar almara. Ita kam likitar murmushi kawai take yi tana kallansu, dan babu ƙarya soyayyar tasu ta burge ta matuƙa. Yanda farin cikin Bad Man ɗin ya kasa ɓoyuwa ya burge ta.
"Allah Ya miki albarka, Ya biya miki dukkanin buƙatunki, Ya albarkaci rayuwarki, Ya inganta abin da ke cikinki, Ya fito mana da shi lafiya, rayayye kuma lafiyayye. Ameen." Ita dai Didi babu baki se binsa kawai take da kallo ta kasa furta komai.
"Ina tuni dai, a dinga barinta tana hutawa.." Likitar ta sake faɗa lokacin da take ƙoƙarin ficewa daga cikin office ɗin nata da ya fi kama da wani tanƙamemen palour me kyau da ƙayatarwa. Ya jinjina kai yana murmushi dan sam ɗazu be ji ta ba ma saboda farin cikin da ya samu kansa a ciki.
.. "Ki faɗa min duk abin da kike buƙata a faɗin duniyar nan, wanda zan ɗauka in ba ki shi a matsayin tukwuici." Ya ƙarasa maganar yana kallan cikin asibitin, kafin ya dawo da dubansa kanta yana gyara zamansa a kan kujerar. Murmushin da ita kanta Didi ya ƙi barin fuskarta ta yi, har yanzu jin abin take kamar wasa, wai tana da juna biyu.
"Ni kai nake so.."
"Ni kuma?" Bad Man ya tambaya yana nuna kansa. Se ta jinjina kai cike da tabbatarwa. Ya girgiza kai yana murmushi
"Da ma tun can ni ɗin ai naki ne.. Wani abun za ki zaɓa.."
"Allah kuwa da gaske ni kai nake so.. So nake ka mallaka min kanka har abada." Ta ƙare maganar a narke. Kwantar da kansa ya yi kan kujera ya kalli saman motar. Be ma san ta inda ze soma mata bayanin ya mallaka mata kansa har abada kamar yanda take buƙata ba. Se dai kawai ya sake dawo da dubansa kanta. Kusan minti 1 yana kallanta, cike da so, ƙaunarta da kuma abin da ke cikinta.
"Idan dai har ni ne, toh ki saka a ranki da ma can ni naki ne.. Se dai tun da ki na son ki sake tabbatarwa, toh ni Areef na mallaka miki kaina gaba ɗaya ki yi yanda kika ga dama da ni. Allah Ya yi miki albarka, Ya ƙara miki lafiya.. Ina sonki.." Ya ƙare yana haɗe ta da jikinsa.
"Ni ma ina sonka.." Ta maida masa da amsar tana sake rungume shi idanunta a lumshe.
Tun a daren ranar komai hana ta yi ya yi, daga ta so yin abu ze ce ta bar shi ze yi. Da ma kuma ita kanta yau ɗin ba ta wani ji daɗin jikinta ba, dalili kenan da ya sanya ta kwantawa kamar yadda ya umarce ta. Haka har washegari ma, dan dai ta tabbatar masa da ba ta jin komai a jikinta ne kafin ya barta fitar da za su yi zuwa asibiti. Ko da ya gama shirya ta cikin doguwar rigar abaya da mayafinta. Be ƙyale ta ba, se ya saƙala hannunsa cikin nata. Ta juya ta kalle shi da sauri, tace kamar me shirin fashewa da kuka.
"Babe za mu haɗu da su Gwani fa.." Taɓe baki ya yi kafin yace cikin basarwa
"Me na aikata?" Se ta kalli hannun nasa, ya basar kamar be gani ba yana cigaba da tafiya har suka fice daga ɗakinsu. Daidai lokacin da Gwani da Lulu suka fito daga cikin nasu ɗakin, su ma sun yi kyau sosai abinsu.
"Madallah, ba za a wahalar min da mata ba." Bad Man ya faɗa yana ƙarasawa inda suke. Girgiza kai Gwani ya yi yana ɗan murmushi. Kafin ya maaze yace
"Malam me ye haka?" Ya faɗa yana watsa masa idanunsa. Se da ya ɗan yamutsa fuska kafin ya ɗan marairaice ta yace
"Amma dai bro a gabanka jiya ta kusa faɗuwa koh? Kuma ma dai likita tace ta dinga hutawa." Ya ƙare yana ɗan satar kallan Didi da ke ta taɓo shi alamar ya yi shiru. Se ta yi amfani da wannan damar wajen zame hannunta. Ya kalle ta kana ya jinjina kai, irin za ki sani ɗin nan. Ta turo baki tana kautar da kanta.
"Me yake damunki Didi?" Lulu ta faɗa lokacin da ta ƙarasa kusa da Didin, tana jin tashin hankali na zuwar mata.
"Ba komai fa Lulu.." Didi ta ƙare maganar tana kallan Bad Man. Se kuwa aka yi sa'a su yake kalla. Ta girgiza masa kai, ya maƙe kafaɗa yana murmushi gami da kautar da kai. Ta rausayar da kai tana ji a ranta shi kenan a gaban Gwanin ze tona mata asiri.
"Wallahi ba wani nan.. Yaya areef me ke damunta?" Lulu ta faɗa idanunta cike fall da ƙwallar da ta taru lokaci guda. Se da ya saci kallan Didi kafin su haɗa ido ya dawo da dubansa kan Lulu yace
"Amm.." Ya ɗan yi shiru yana shafa kwantacciyar sumar da ke kwance luff a ƙeyarsa.
"Yaronki ke wahalar da ita.." Ya yi maganar ƙasa ƙasa. Daga farko sam Lulu ba ta fahimci abin da yake nufi ba. Se kuma daga baya ta yi shiru tana sake nazarin maganarsa. Idan dai har ta fahimta da kyau, yana nufin kenan Didin na ɗauke da ciki? Ai ba ta san lokacin da ta juya ba, da gudu ta ƙarasa ta rungume Didi da ke tsaye tana ta raba idanu. Hannu Gwani ya kai kamar me shirin tare ta. Dan tsoro ya ji kar ta faɗi. Garin wani farin cikin a tarwatsa wani.
"Wayyo Allah Didina.." Shi ne abin da ta faɗa kawai tana ƙanƙame er uwar tata, ita sam ta ma manta akwai abu a cikinta. Tsananin farin cikin da Didi ta gani a kan fuskar Lulu shi ne ya sanya ta sakin murmushi, har se da ta ji ƙwalla ta tarar mata cikin idanu. Ta rungume er uwar tata, wani farin cikin na sake lulluɓe ta.
"Ina taya ka murna.. Na kusa zama uban 'ya'ya biyu kenan." Gwani ya ƙare maganar yana murmushi idanunsa a kan Bad Man.
"Godiya nake bro.. Ƙwarai kuwa.." Bad Man ya amsa yana jinjina kansa hannunsa cikin na Gwani da ya miƙa masa suka gaisa. Kawai shi ma se ya rungume ɗan uwan nasa yana faɗin
"Ina taya mu farin ciki gaba ɗaya.. Allah Ya dawwamar mana da zaman lafiya me ɗorewa.."
"A'ah, yau ɗin ma In Allah Ya yarda ba zan nemi komai ba.. Ai ba za ka bar 'yata ita ɗaya ba. Ku je Allah Ya muku albarka."
"Ameen." Suka amsa kusan a tare, kafin su ma suka mata sallama kana suka fice.
.. Tun ɗazu yake lura da ita, yanda yanayin tafiyarta ya sauya.
"Didi" Lulu da ke gefenta ta kira sunanta. Sake dafe kanta ta yi tana lumshe idanunta. Se dai duk da haka ba ta dena takawa ba. Wani jiri da ya kwashe ta shi ya tilasta mata dakatawa, ba tare da ta ankara ba ta tafi da niyyar zubewa. Ya yi saurin ƙarasawa ya saka hannunsa, hakan ne ya sanya ta faɗawa jikinsa. Ajiyar zuciya ya sauke lokaci guda ƙirjinsa na bugawa dan babu ƙarya ya tsorata. Gwani da Lulu kansu sun tsorata, dalili kenan da ya sanya dukkansu su ma suka dakata. Hannu Bad Man ya saka ya tallafo fuskarta da idanunta ke a rufe, dan ita kanta ta tsorata. Cikin kulawa yace
"Babe!" Se a lokacin ta shiga buɗe idanunta, ƙirjinta na harbawa da ƙarfi. Tashi ta soma ƙoƙarin yi, ya barta ta miƙe amma duk da haka tana jikinsa.
"Da ma ba ki da lafiya shi ne ba ki sanar da ni ba?" Ya tambaya yana kafe ta da idanunsa da suka ɗan sauya. Girgiza kai ta yi cike da gaskiyarta tace
"Lafiyata ƙalau." Iska ya fesar yana runtse idanunsa. Ya buɗe su yana kallan nata dai.
"Ba ki da lafiya.." Ya faɗa kamar shi ke da jikinta.
"Lafiyata.."
"Shhh.." Ya faɗa yana ɗora hannunsa a kan bakinsa. Kawai se ta yi shiru ta cigaba da kallan yanda cikin ƙanƙanin lokaci yanayinsa gaba ɗaya ya sauya. Kai ba za ka taɓa cewa shi ne ɗazun ba. Ita dai ba ta sake cewa komai ba har zuwa lokacin da ya miƙar da ita sosai.
"Bro za mu koma asibitin, ku ƙarasa kawai.." Bin Didi da kallo kawai Lulu take yi da idanunta da ita ma suka sauya, cike da tunanin abin da ke damun er uwar tata.
"Allah Ya ƙara sauƙi." Gwani ya faɗa.
"Ameen." Bad Man ya amsa da hakan yana juyawa, ya kama hannun Didi suka fice daga cikin hotel ɗin da ba su yi nisa da shigo shi ba.
"Mu je koh?" Gwani ya faɗa yana kallan Lulu da ta bi su da kallo. Ganin yanda duk ita ma yanayinta ya sauya ne ya sanya shi ƙarasawa kusa da ita sosai. Cikin rarrashi yace
"Ki kwantar da hankalinki, babu abin da ze faru In Sha Allah.." Ya yi maganar yana kallanta sosai.
"Didina ba ta.."
"Kar ki ce komai.. Babu abin da ze faru Uhmm?" Se da ta sauke wani dogon numfashi kafin ta jinjina kanta jiki a sanyaye. Haka suka ƙarasa ɗakinsu zuciyarta fall tunanin Didinta.
.. "Ina taya ka murna, matarka na ɗauke da juna biyu.." Shi ne bayanin da likitar ta faɗa masa bayan gwajin da aka yi wa Didi. Kallan likitar yake yi lokacin da take bayanin, amma be san lokacin da idanunsa suka koma kan Didi ba. Tun daga nan kuma be sake fahimtar abin da take faɗa ba. Ita ma Didi kanta kallansa take yi, tana jin abun kamar a mafarki. Da gaske matar take ciki ne da ita? Lallai Allah me iko. Ba ta san lokacin da Bad ya ƙaraso inda take ba, se ji ta yi kawai an ɗaga ta gaba ɗaya ana juyi da ita cikin ɗakin. Cikin matuƙar farin ciki ya rungume ta yana ji kamar ya maida ta cikinsa. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin ya sauketa a kan kujerar da ya ɗauke ta daga kai, ya sake zuba mata idanunsa da kalarsu ta chanja. Iya su kaɗai ko fuskarsa kaɗai za ka kalla ka fahimci farin cikin da yake ciki. Ya kasa furta komai, jin abin yake kamar almara. Ita kam likitar murmushi kawai take yi tana kallansu, dan babu ƙarya soyayyar tasu ta burge ta matuƙa. Yanda farin cikin Bad Man ɗin ya kasa ɓoyuwa ya burge ta.
"Allah Ya miki albarka, Ya biya miki dukkanin buƙatunki, Ya albarkaci rayuwarki, Ya inganta abin da ke cikinki, Ya fito mana da shi lafiya, rayayye kuma lafiyayye. Ameen." Ita dai Didi babu baki se binsa kawai take da kallo ta kasa furta komai.
"Ina tuni dai, a dinga barinta tana hutawa.." Likitar ta sake faɗa lokacin da take ƙoƙarin ficewa daga cikin office ɗin nata da ya fi kama da wani tanƙamemen palour me kyau da ƙayatarwa. Ya jinjina kai yana murmushi dan sam ɗazu be ji ta ba ma saboda farin cikin da ya samu kansa a ciki.
.. "Ki faɗa min duk abin da kike buƙata a faɗin duniyar nan, wanda zan ɗauka in ba ki shi a matsayin tukwuici." Ya ƙarasa maganar yana kallan cikin asibitin, kafin ya dawo da dubansa kanta yana gyara zamansa a kan kujerar. Murmushin da ita kanta Didi ya ƙi barin fuskarta ta yi, har yanzu jin abin take kamar wasa, wai tana da juna biyu.
"Ni kai nake so.."
"Ni kuma?" Bad Man ya tambaya yana nuna kansa. Se ta jinjina kai cike da tabbatarwa. Ya girgiza kai yana murmushi
"Da ma tun can ni ɗin ai naki ne.. Wani abun za ki zaɓa.."
"Allah kuwa da gaske ni kai nake so.. So nake ka mallaka min kanka har abada." Ta ƙare maganar a narke. Kwantar da kansa ya yi kan kujera ya kalli saman motar. Be ma san ta inda ze soma mata bayanin ya mallaka mata kansa har abada kamar yanda take buƙata ba. Se dai kawai ya sake dawo da dubansa kanta. Kusan minti 1 yana kallanta, cike da so, ƙaunarta da kuma abin da ke cikinta.
"Idan dai har ni ne, toh ki saka a ranki da ma can ni naki ne.. Se dai tun da ki na son ki sake tabbatarwa, toh ni Areef na mallaka miki kaina gaba ɗaya ki yi yanda kika ga dama da ni. Allah Ya yi miki albarka, Ya ƙara miki lafiya.. Ina sonki.." Ya ƙare yana haɗe ta da jikinsa.
"Ni ma ina sonka.." Ta maida masa da amsar tana sake rungume shi idanunta a lumshe.
Tun a daren ranar komai hana ta yi ya yi, daga ta so yin abu ze ce ta bar shi ze yi. Da ma kuma ita kanta yau ɗin ba ta wani ji daɗin jikinta ba, dalili kenan da ya sanya ta kwantawa kamar yadda ya umarce ta. Haka har washegari ma, dan dai ta tabbatar masa da ba ta jin komai a jikinta ne kafin ya barta fitar da za su yi zuwa asibiti. Ko da ya gama shirya ta cikin doguwar rigar abaya da mayafinta. Be ƙyale ta ba, se ya saƙala hannunsa cikin nata. Ta juya ta kalle shi da sauri, tace kamar me shirin fashewa da kuka.
"Babe za mu haɗu da su Gwani fa.." Taɓe baki ya yi kafin yace cikin basarwa
"Me na aikata?" Se ta kalli hannun nasa, ya basar kamar be gani ba yana cigaba da tafiya har suka fice daga ɗakinsu. Daidai lokacin da Gwani da Lulu suka fito daga cikin nasu ɗakin, su ma sun yi kyau sosai abinsu.
"Madallah, ba za a wahalar min da mata ba." Bad Man ya faɗa yana ƙarasawa inda suke. Girgiza kai Gwani ya yi yana ɗan murmushi. Kafin ya maaze yace
"Malam me ye haka?" Ya faɗa yana watsa masa idanunsa. Se da ya ɗan yamutsa fuska kafin ya ɗan marairaice ta yace
"Amma dai bro a gabanka jiya ta kusa faɗuwa koh? Kuma ma dai likita tace ta dinga hutawa." Ya ƙare yana ɗan satar kallan Didi da ke ta taɓo shi alamar ya yi shiru. Se ta yi amfani da wannan damar wajen zame hannunta. Ya kalle ta kana ya jinjina kai, irin za ki sani ɗin nan. Ta turo baki tana kautar da kanta.
"Me yake damunki Didi?" Lulu ta faɗa lokacin da ta ƙarasa kusa da Didin, tana jin tashin hankali na zuwar mata.
"Ba komai fa Lulu.." Didi ta ƙare maganar tana kallan Bad Man. Se kuwa aka yi sa'a su yake kalla. Ta girgiza masa kai, ya maƙe kafaɗa yana murmushi gami da kautar da kai. Ta rausayar da kai tana ji a ranta shi kenan a gaban Gwanin ze tona mata asiri.
"Wallahi ba wani nan.. Yaya areef me ke damunta?" Lulu ta faɗa idanunta cike fall da ƙwallar da ta taru lokaci guda. Se da ya saci kallan Didi kafin su haɗa ido ya dawo da dubansa kan Lulu yace
"Amm.." Ya ɗan yi shiru yana shafa kwantacciyar sumar da ke kwance luff a ƙeyarsa.
"Yaronki ke wahalar da ita.." Ya yi maganar ƙasa ƙasa. Daga farko sam Lulu ba ta fahimci abin da yake nufi ba. Se kuma daga baya ta yi shiru tana sake nazarin maganarsa. Idan dai har ta fahimta da kyau, yana nufin kenan Didin na ɗauke da ciki? Ai ba ta san lokacin da ta juya ba, da gudu ta ƙarasa ta rungume Didi da ke tsaye tana ta raba idanu. Hannu Gwani ya kai kamar me shirin tare ta. Dan tsoro ya ji kar ta faɗi. Garin wani farin cikin a tarwatsa wani.
"Wayyo Allah Didina.." Shi ne abin da ta faɗa kawai tana ƙanƙame er uwar tata, ita sam ta ma manta akwai abu a cikinta. Tsananin farin cikin da Didi ta gani a kan fuskar Lulu shi ne ya sanya ta sakin murmushi, har se da ta ji ƙwalla ta tarar mata cikin idanu. Ta rungume er uwar tata, wani farin cikin na sake lulluɓe ta.
"Ina taya ka murna.. Na kusa zama uban 'ya'ya biyu kenan." Gwani ya ƙare maganar yana murmushi idanunsa a kan Bad Man.
"Godiya nake bro.. Ƙwarai kuwa.." Bad Man ya amsa yana jinjina kansa hannunsa cikin na Gwani da ya miƙa masa suka gaisa. Kawai shi ma se ya rungume ɗan uwan nasa yana faɗin
"Ina taya mu farin ciki gaba ɗaya.. Allah Ya dawwamar mana da zaman lafiya me ɗorewa.."