Sashe 14
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ɗakinki?" Ya tambaya a mamakance. Jinjina kai Ummeey ta yi tana mamakin yanda ya yi tambayar cike da mamaki kamar wadda ta faɗi saɓo. Da sauri kuma ya basar kawai ya yi murmushi. Da sauri ya ƙarasa taya Ummeeyn ninkin, se da suka gama tsaff, sannan ya kwaso su duka zuwa cikin ɗakin nata. Tana zaune cikin ɗakin kamar wata munafuka se rarraba idanu take yi. Tunda ya mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa, ya ƙarasa cikin ɗakin ya ajje kayan, daidai lokacin da Ummeey ma ta shigo ta ajje na hannunta.
"Ɗiyata tashi ku je, ai ma kin yi ƙoƙari. Zama kai ɗayan nan ba shi da daɗi sam.." Kamar jira take yi se kuwa ta miƙe zumbur, har tana riga shi yin gaba. Da mamaki ya ɗan kalleta se kuma ya maida dubansa kan Ummeey. Yana shirin cewa wani abu tace
"Ɗauki abincin nan ka tafi mata da shi.. Ba taci komai ba tun zuwanta ɗakin nan, ina ga ko kunya take ji. Ka sakata ta ci ko da kaɗan ne."
"Toh" ya amsa da hakan yana ɗaukar abincin.
Ƙarasawa ya yi ya ajje abincin inda ya ajje na ɗazu. Ga mamakinsa komai da ya shigo da su ɗazun duk suna wajen, babu alamar ma an taɓa su. Hakan na nufin kenan babu abin da ta ci tun jiya? Juyawa ya yi ya kalleta inda take tsaye wajen bakin ƙofa. Idanunta sun cika fall da ƙwallar baƙin ciki, haushi da abubuwa da dama. Yana shirin ɗauke kansa ya ji muryarta tana faɗin
"Ka sake ni gidanmu zan koma. Ba na sonka.. Kuma ai ba a aure dole." Tsayawa ya yi yana kallanta, cike da ganin ƙoƙarinta na iya tsayawa gabansa tana faɗar hakan. Se da ya ɗan yi murmushin gefen baki sannan yace
"Saki kike so?" Cikin sauri ta amsa da
"Ehh. Saboda ba na sonka, ba na sonka, ba na sonka.." Ɗan runtse manyan kyawawan idanunsa ya yi, duk da shi ɗin ma ba sonta yake ba, amma tabbas ya ji zafin waɗannan kalaman nata ainun, ya ji zafinsu fiye da zaton me tsammani. Shi kansa ba dan wasu abubuwa ba da babu abin da ze hana shi sawwaƙe matan. Se dai kuma tana nuna kamar umarni take ba shi, daga kuma lokacin da ya bi umarnin nata ya saketa ya zama lusarin namiji kenan, ya zama sokon namiji wanda mace kan iya sarrafa shi. Dan haka se ya ɗan ciji lips ɗinsa da ɗan ƙarfi kafin ya watsa mata idanunsa, se ya soma matsowa zuwa inda take fuskarsa a haɗe fiye da yanda take a da. Se da ya zo dab da ita sannan ya dakata ya ɗauki hannayensa duka biyun ya saƙala a ƙirjinsa sannan ya zuba mata idanunsa masu matuƙar kyau da kwarjini. Yanda ta gan shi kusa da ita ne sosai ya sanyata ɗan ruɗewa, ta ji ƙirjinta ya wani irin bugawa duk da rashin kunya da tsiwar da take ji amma ganinsa kusa da ita ya sanya ta ɗan ji tsoro. Se kawai ta maaze ta ɗan gyara ƙafarta saboda yanda ta ji har ita ma rawa take yi kamar wadda ke shirin ƙin ɗaukarta. Cikin dakakkiyar muryarsa ya soma faɗin
"Waye ya faɗa miki ni sonki nake yi? Ko ki na tunanin hakan ne?" Se ya girgiza kansa cike da takaicin halayen Lulun yace
"Ki dena yaudarar kanki.. Ina zaune, ba tare da na nema ba aka ba ni aurenki.. Dan haka ki dena wani fiffiƙa ki yi ƙoƙarin kwantar da kanki ƙasa dan cigaba da zama da ni.. Saki kuma idan har ba ni na ga dama ba, za ki cigaba da zama ne cikin gidan nan har se lokacin da na yi niyyar sakinki. Idan kuma a hannunki yake maza ɗauki takadda ki rubuta ki tafi da ita.." Yana kaiwa nan ya dakata. Wani irin tafasa zuciyarta ke yi sanda maganganun ke sauka cikin kunnenta. Se ta shiga sauke ajiyar zuciya da sauri sauri, wani irin kukan baƙin ciki na taso mata. Cikin ɗaga murya ta buɗe baki da iya ƙarfinta ta soma faɗin cikin kuka
"Toh ka sake ni mana ka huta.. Ni ka sake ni na faɗa maka ba na sonka. Ba zan iya zama da kai ba har abada.. Ba na sonka." Kafin ta cigaba da maganar ta soma ƙoƙarin zubewa a wajen tana kuka wiwi. Tana shirin sake faɗar wasu maganganun dan sake baƙanta masa, da tunzura shi ya saketa, hakan ne ya sanyata ƙoƙarin sake ɗaga murya dan maganar yanzun tafi shigarsa se ji ta yi ruff, an rufe mata baki da wani abu da ta kasa gane meye saboda tsabar taushinsa. Ni kaina ba zan iya cewa ha lokacin da ya riƙota ba. Se kawai ganinta na yi a hannunsa. Hannunsa ɗaya ya saka shi ne a bayanta ya riƙota dab da jikinsa, yayin da ɗayan hannun nasa da shi ya yi amfani wajen rufe mata bakin, dan ba ya buƙatar duk wani abu da ze faru Ummeey ta san da shi, saboda baya son ɓata mata farin cikin da ya gani a tattare da ita tun bayan auren. Musamman kuma tun zuwan Lulu gidan. Yanda ta buɗe idanu a razane cikin matuƙar ruɗewa ya sanya idanunta sauka a kan fuskarsa, sanda shi ma nasa idanun ke kan fuskarta a haɗe, dan hatta da idanunsa se da suka chanja colour. Cikin kausashshiyar murya me cike da gargaɗi yace
"Keee!!" Ya faɗa har lokacin tana kan hannunsa, ɗayan hannun nasa kuma na kan bakinta. Ita sam ba ma fahimtar abin da ya faɗa ta yi ba, se ƙoƙarin tashi da take yi ƙirjinta na wani irin bugawa. Ga shi ta kasa cewa komai, ga shi ta kasa aikata komai, hakan ne ya sanya ƙwallar da ta taru cikin idanunta damar zubowa a kan fuskarta tana sake yunƙurin miƙewa cike da ƙarfin hali..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO31*
___"Ba ki da hankali? So kike ki nunawa kowa rashin kunyarki? So kike kowa ya fahimci ba kya amfani da tarbiyyar da iyayenki suka miki? So kike ki sake nuna min da gasken ke fitsararriya ce?" Gwani ya ƙarasa faɗa yana kallan cikin idanunta ransa a mugun ɓace. Ba ta san sanda ta runtse idanunta ba, jin ƙoƙarin miƙewar da take yi ya faskara ya sanyata haƙura kawai se ruwan hawayen dake ambaliya daga idanunta. Ga shi kuma ya hanata cewa komai saboda rufe bakinta da ya yi, ballantana ta yi amfani da bakin wajen yin rashin kunyar da ta saba. Se dai kamin ta ida tunanin ta sake jiyo kausassar muryarsa yana faɗin
"Daga yau.. duk ranar da kika sake yunƙurin yi wa wani a cikin gidan nan rashin kunya wallahi zan kawar da mutuncin mahaifinki da nake gani, na saɓa miki.. Hatta bakin rashin kunyar da kike taƙama da shi zan gurje shi ne ko da a jikin bango ne, yanda ba za ki sake yunƙurin aikata hakan ba. Shashashar yarinya.." Ya ida faɗa yana ɗan fesar da numfashi saboda yanda ya ji kansa ya sara da ƙarfin gaske. Se kuma ya janye hannunsa daga kan bakinta sannan ya saketa a hankali, ba tare da jiran komai ba ya fice daga ɗakin hannunsa dafe da kansa. Zubewa kawai ta yi a wajen tana fashewa da kukan takaici. Ai koma mene ne ya faru Abba ne ya janyo mata, ita ya za ta yi da rayuwarta ne? Me za ta yi ta ji daɗi, ta fita daga wannan ƙuncin da ta shiga a cikin gidan nan. Mami tace mata za ta zo su san abin yi, amma har yanzu ba ta zo ba. Shin guduwa ya kamata ta yi ko mene ne? Ta ɗauka rashin kunyarta za ta yi tasiri a wajen Gwanin, ganin cewar ba ya son raini, ba ya kuma ɗaukarsa, ta ɗauka cikin ƙanƙanin lokaci za ta fusata shi ya saketa, se dai ba ta ga alamar hakan ba. Toh ita kam ya za ta yi da rayuwarta?. Kawai se ta kifa kanta a ƙasa duk da kukan da take hakan be hanata sauke ajiyar zuciya ba cikin rashin sanin abin yi. Jin yanda ƙamshin jikinsa ke cigaba da tashi a jikinta ne ya sanyata sake fusata, se ta cigaba da rusar kukanta lokacin da ta miƙe dan tuɓe kayan ko za ta rabu da jin ƙamshin turaren nasa da a wajenta ba shi da maraba da ɗoyin tutu.
Se da ya ɗan tsaya na tsawon minti 2 sannan ya wuce ɗakin Ummeeyn. Kallansa ta yi cike da mamakin ganin yanayinsa tace
"Affan lafiya kuwa?" Ta tambaya cike da kulawa. Se da ya yamutsa fuska, dan be yi tunanin ma ɓacin ran nasa ya bayyana har kan fuskarta ba, sannan yace
"Kaina ke ciwo Ummeey.. Amma zan sha magani.."
"Toh gwara dai ka sha.. Ka kalli har yanayinka ya chanja.."
"Tohm.." ya faɗa yana gyara zamansa, sannan ya ɗora masa
"Ummeey.. maganar kayan nan dama nake so mu yi dake ɗazun. Ya ba ni kayan, ya kuma ce zan iya juya su har zuwa lokacin da nake so.. Se na maida masa da kuɗinsa.." Cikin farin ciki Ummeey tace
"Kai Masha Allah.. Masha Allah.. Allah ya sa a fara a sa'a. Allah ya saka masa da alkhairi ya ƙara masa arziƙi.."
"Ameen Ameen.." ya amsa a nutse.
"Kun yi maganar da Abeeynka?" Girgiza kai ya yi yace
"A'ah Ummeey na ga yana buƙatar hutu ne kin ga ba ya wani jin daɗi.. So kuma na ga yana bacci ne shi ya sa na bari se ya farka se na faɗa masa."
"Toh madallah.." Ummeey ta faɗa cike da farin ciki, dan babu ƙarya ta ji daɗin wannan al'amari sosai.
... "Rankiyadaɗe wata magana na zo da ita.. Se dai ban san yanda za ki ɗauketa ba.." Atine ta faɗa kanta a ƙasa.
"Ɗiyata tashi ku je, ai ma kin yi ƙoƙari. Zama kai ɗayan nan ba shi da daɗi sam.." Kamar jira take yi se kuwa ta miƙe zumbur, har tana riga shi yin gaba. Da mamaki ya ɗan kalleta se kuma ya maida dubansa kan Ummeey. Yana shirin cewa wani abu tace
"Ɗauki abincin nan ka tafi mata da shi.. Ba taci komai ba tun zuwanta ɗakin nan, ina ga ko kunya take ji. Ka sakata ta ci ko da kaɗan ne."
"Toh" ya amsa da hakan yana ɗaukar abincin.
Ƙarasawa ya yi ya ajje abincin inda ya ajje na ɗazu. Ga mamakinsa komai da ya shigo da su ɗazun duk suna wajen, babu alamar ma an taɓa su. Hakan na nufin kenan babu abin da ta ci tun jiya? Juyawa ya yi ya kalleta inda take tsaye wajen bakin ƙofa. Idanunta sun cika fall da ƙwallar baƙin ciki, haushi da abubuwa da dama. Yana shirin ɗauke kansa ya ji muryarta tana faɗin
"Ka sake ni gidanmu zan koma. Ba na sonka.. Kuma ai ba a aure dole." Tsayawa ya yi yana kallanta, cike da ganin ƙoƙarinta na iya tsayawa gabansa tana faɗar hakan. Se da ya ɗan yi murmushin gefen baki sannan yace
"Saki kike so?" Cikin sauri ta amsa da
"Ehh. Saboda ba na sonka, ba na sonka, ba na sonka.." Ɗan runtse manyan kyawawan idanunsa ya yi, duk da shi ɗin ma ba sonta yake ba, amma tabbas ya ji zafin waɗannan kalaman nata ainun, ya ji zafinsu fiye da zaton me tsammani. Shi kansa ba dan wasu abubuwa ba da babu abin da ze hana shi sawwaƙe matan. Se dai kuma tana nuna kamar umarni take ba shi, daga kuma lokacin da ya bi umarnin nata ya saketa ya zama lusarin namiji kenan, ya zama sokon namiji wanda mace kan iya sarrafa shi. Dan haka se ya ɗan ciji lips ɗinsa da ɗan ƙarfi kafin ya watsa mata idanunsa, se ya soma matsowa zuwa inda take fuskarsa a haɗe fiye da yanda take a da. Se da ya zo dab da ita sannan ya dakata ya ɗauki hannayensa duka biyun ya saƙala a ƙirjinsa sannan ya zuba mata idanunsa masu matuƙar kyau da kwarjini. Yanda ta gan shi kusa da ita ne sosai ya sanyata ɗan ruɗewa, ta ji ƙirjinta ya wani irin bugawa duk da rashin kunya da tsiwar da take ji amma ganinsa kusa da ita ya sanya ta ɗan ji tsoro. Se kawai ta maaze ta ɗan gyara ƙafarta saboda yanda ta ji har ita ma rawa take yi kamar wadda ke shirin ƙin ɗaukarta. Cikin dakakkiyar muryarsa ya soma faɗin
"Waye ya faɗa miki ni sonki nake yi? Ko ki na tunanin hakan ne?" Se ya girgiza kansa cike da takaicin halayen Lulun yace
"Ki dena yaudarar kanki.. Ina zaune, ba tare da na nema ba aka ba ni aurenki.. Dan haka ki dena wani fiffiƙa ki yi ƙoƙarin kwantar da kanki ƙasa dan cigaba da zama da ni.. Saki kuma idan har ba ni na ga dama ba, za ki cigaba da zama ne cikin gidan nan har se lokacin da na yi niyyar sakinki. Idan kuma a hannunki yake maza ɗauki takadda ki rubuta ki tafi da ita.." Yana kaiwa nan ya dakata. Wani irin tafasa zuciyarta ke yi sanda maganganun ke sauka cikin kunnenta. Se ta shiga sauke ajiyar zuciya da sauri sauri, wani irin kukan baƙin ciki na taso mata. Cikin ɗaga murya ta buɗe baki da iya ƙarfinta ta soma faɗin cikin kuka
"Toh ka sake ni mana ka huta.. Ni ka sake ni na faɗa maka ba na sonka. Ba zan iya zama da kai ba har abada.. Ba na sonka." Kafin ta cigaba da maganar ta soma ƙoƙarin zubewa a wajen tana kuka wiwi. Tana shirin sake faɗar wasu maganganun dan sake baƙanta masa, da tunzura shi ya saketa, hakan ne ya sanyata ƙoƙarin sake ɗaga murya dan maganar yanzun tafi shigarsa se ji ta yi ruff, an rufe mata baki da wani abu da ta kasa gane meye saboda tsabar taushinsa. Ni kaina ba zan iya cewa ha lokacin da ya riƙota ba. Se kawai ganinta na yi a hannunsa. Hannunsa ɗaya ya saka shi ne a bayanta ya riƙota dab da jikinsa, yayin da ɗayan hannun nasa da shi ya yi amfani wajen rufe mata bakin, dan ba ya buƙatar duk wani abu da ze faru Ummeey ta san da shi, saboda baya son ɓata mata farin cikin da ya gani a tattare da ita tun bayan auren. Musamman kuma tun zuwan Lulu gidan. Yanda ta buɗe idanu a razane cikin matuƙar ruɗewa ya sanya idanunta sauka a kan fuskarsa, sanda shi ma nasa idanun ke kan fuskarta a haɗe, dan hatta da idanunsa se da suka chanja colour. Cikin kausashshiyar murya me cike da gargaɗi yace
"Keee!!" Ya faɗa har lokacin tana kan hannunsa, ɗayan hannun nasa kuma na kan bakinta. Ita sam ba ma fahimtar abin da ya faɗa ta yi ba, se ƙoƙarin tashi da take yi ƙirjinta na wani irin bugawa. Ga shi ta kasa cewa komai, ga shi ta kasa aikata komai, hakan ne ya sanya ƙwallar da ta taru cikin idanunta damar zubowa a kan fuskarta tana sake yunƙurin miƙewa cike da ƙarfin hali..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO31*
___"Ba ki da hankali? So kike ki nunawa kowa rashin kunyarki? So kike kowa ya fahimci ba kya amfani da tarbiyyar da iyayenki suka miki? So kike ki sake nuna min da gasken ke fitsararriya ce?" Gwani ya ƙarasa faɗa yana kallan cikin idanunta ransa a mugun ɓace. Ba ta san sanda ta runtse idanunta ba, jin ƙoƙarin miƙewar da take yi ya faskara ya sanyata haƙura kawai se ruwan hawayen dake ambaliya daga idanunta. Ga shi kuma ya hanata cewa komai saboda rufe bakinta da ya yi, ballantana ta yi amfani da bakin wajen yin rashin kunyar da ta saba. Se dai kamin ta ida tunanin ta sake jiyo kausassar muryarsa yana faɗin
"Daga yau.. duk ranar da kika sake yunƙurin yi wa wani a cikin gidan nan rashin kunya wallahi zan kawar da mutuncin mahaifinki da nake gani, na saɓa miki.. Hatta bakin rashin kunyar da kike taƙama da shi zan gurje shi ne ko da a jikin bango ne, yanda ba za ki sake yunƙurin aikata hakan ba. Shashashar yarinya.." Ya ida faɗa yana ɗan fesar da numfashi saboda yanda ya ji kansa ya sara da ƙarfin gaske. Se kuma ya janye hannunsa daga kan bakinta sannan ya saketa a hankali, ba tare da jiran komai ba ya fice daga ɗakin hannunsa dafe da kansa. Zubewa kawai ta yi a wajen tana fashewa da kukan takaici. Ai koma mene ne ya faru Abba ne ya janyo mata, ita ya za ta yi da rayuwarta ne? Me za ta yi ta ji daɗi, ta fita daga wannan ƙuncin da ta shiga a cikin gidan nan. Mami tace mata za ta zo su san abin yi, amma har yanzu ba ta zo ba. Shin guduwa ya kamata ta yi ko mene ne? Ta ɗauka rashin kunyarta za ta yi tasiri a wajen Gwanin, ganin cewar ba ya son raini, ba ya kuma ɗaukarsa, ta ɗauka cikin ƙanƙanin lokaci za ta fusata shi ya saketa, se dai ba ta ga alamar hakan ba. Toh ita kam ya za ta yi da rayuwarta?. Kawai se ta kifa kanta a ƙasa duk da kukan da take hakan be hanata sauke ajiyar zuciya ba cikin rashin sanin abin yi. Jin yanda ƙamshin jikinsa ke cigaba da tashi a jikinta ne ya sanyata sake fusata, se ta cigaba da rusar kukanta lokacin da ta miƙe dan tuɓe kayan ko za ta rabu da jin ƙamshin turaren nasa da a wajenta ba shi da maraba da ɗoyin tutu.
Se da ya ɗan tsaya na tsawon minti 2 sannan ya wuce ɗakin Ummeeyn. Kallansa ta yi cike da mamakin ganin yanayinsa tace
"Affan lafiya kuwa?" Ta tambaya cike da kulawa. Se da ya yamutsa fuska, dan be yi tunanin ma ɓacin ran nasa ya bayyana har kan fuskarta ba, sannan yace
"Kaina ke ciwo Ummeey.. Amma zan sha magani.."
"Toh gwara dai ka sha.. Ka kalli har yanayinka ya chanja.."
"Tohm.." ya faɗa yana gyara zamansa, sannan ya ɗora masa
"Ummeey.. maganar kayan nan dama nake so mu yi dake ɗazun. Ya ba ni kayan, ya kuma ce zan iya juya su har zuwa lokacin da nake so.. Se na maida masa da kuɗinsa.." Cikin farin ciki Ummeey tace
"Kai Masha Allah.. Masha Allah.. Allah ya sa a fara a sa'a. Allah ya saka masa da alkhairi ya ƙara masa arziƙi.."
"Ameen Ameen.." ya amsa a nutse.
"Kun yi maganar da Abeeynka?" Girgiza kai ya yi yace
"A'ah Ummeey na ga yana buƙatar hutu ne kin ga ba ya wani jin daɗi.. So kuma na ga yana bacci ne shi ya sa na bari se ya farka se na faɗa masa."
"Toh madallah.." Ummeey ta faɗa cike da farin ciki, dan babu ƙarya ta ji daɗin wannan al'amari sosai.
... "Rankiyadaɗe wata magana na zo da ita.. Se dai ban san yanda za ki ɗauketa ba.." Atine ta faɗa kanta a ƙasa.