Sashe 73
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mom na shiga ɗaki kai tsaye jefar da mukullin ta yi a kan kujera, ta nemi waje ta zauna tana ƙaƙalo murmushi. Ba ta jin ko me take ji za ta iya barin cikin gidan nan ba tare da ganin an fito da gawar Sa'adah da abin da ta haifa ba. Dan a yanda ta hangeta idan ta ɗauki lokaci me yawa ba tare da taimakon kowa ba za ta iya sheƙawa. Tana kuma da tabbacin babu wanda ze ganta tun da babu me shiga ɗakin se Daddy. Baba Atine iyakacinta palour ne. Idan ma za ta iya jin motsinta ga mukullin a hannunta babu damar buɗewa. Ballantana ma tana sane ta kaɗata aike waje me nisa da nufin ta aikatawa Mommahn wani abu. Se ga shi cikin mintina kaɗan ba tare da ta saka hannu ba Sa'adahn ta kusa sheƙawa ita da abin da ke cikinta. Tana nan zaune cikin ɗakin ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ɗan cikinta ya mata wani ƙebebe, ya hanata sakat. Ta kasa zama ta kuma kasa tsayuwar, se zagaye take tana cigaba da daurewa, saboda abin da take jira. Se dai ina.. cikin ƙanƙanin lokaci naƙuda ta tasarma Mom gadan gadan. Tun tana ganin za ta iya har ta haƙura, ta buɗe baki da ƙyar ta kira sunan Maimuna. Maimuna da ke zaune a palour tana jin wannan uban kiran ta miƙe da sauri se ga ta cikin ɗakin. A halin da ta tarar da Mom ɗin ne ya sanyata ruɗewa. Ta yi maza ta ɗauki wayar Mom da niyyar kiran Daddy, da sauri Mom ta janyo hannunta wayar ta faɗi.
"Ki taimaka min kawai.. Babu inda zan je wallahi.." Shi ne abin da Mom ta faɗa tana sauke numfashi a wahalce. Maimuna ta sake binta da kallo jikinta na matuƙar karkarwa. Ta rasa yanda za ta yi, ta kuma rasa fa'idar Mom ɗin na hanata kiran Daddy. Hakan ne ya sanyata zubawa sarautar Allah ido. Aikuwa cikin taimakonsa babu ɗaukar wani lokaci Mom ta haihu a kan gadonta. Ta sauke wata ƙatuwar ajiyar zuciya tana komawa kan gadon idanunta a rufe tana sauke ajiyar zuciya. Ta kai wajen minti 1 a haka tana jiran jin kukan jinjiri ko hakan ze alamta mata jinsin da ta haifa, se dai ba ta ji komai ba. Ita sam ba ta jikinta take ba, ba ta lafiyarta ko lafiyar abin da ta haifa take ba, a'ah ita burinta kawai ta ji Maimunan tace mata namiji ta haifa. Hakan ne ya sanyata kallan Maimuna da Babyn ke hannunta tace
"Me na haifa? Maza ki faɗa min me na haifa?" Kallanta Maimuna ta yi, fuskarta kamar ɗauke da farin ciki, kamar kuma ɗauke da akasin hakan. Muryarta a ɗan raunane tace
"Namiji!!" Komawa Mom ta yi ta baje a kan gadon tana faɗin
"Allah na gode maka.. Alhamdulillah." Ta faɗa tana lumshe idanunta.
"Hajiya duba shi ki ga.. kamar ba ya motsi." Maimuna ta faɗa bayan shuɗewar wasu mintuna tana cigaba da tattaɓa yaron ta ji ko yana motsi. Ƙirjin Mom ya buga da ƙarfin gaske. Ta ɗaga jajayen idanunta ta watsawa Maimunan da take ji kamar ta miƙe ta shaƙo wuyanta. Hannunta na rawa ta sanya wajen karɓar yaron a hannun Maimuna, se kuwa ya biyo hannunta. Ta sake jin wata sabuwar faɗuwar gaban ta ziyarceta. Amma duk da haka ba ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen tattaɓa shi ko za ta ga ya yi motsi kamar yanda jarirai ke yi, se dai sam be yi ba. Hasalima kamar yanda Maimunan ta faɗa babu rai a tare da yaron. Rungume shi Mom ta yi tana faɗin
"Na shiga 3 ni Salma.. Na shiga 3 na lalace." Ta faɗa ilahirin jikinta na rawa saboda tsananin tashin hankali. Kamar kuma wadda aka kunna se ta ajje jaririn a gefenta tana saka hannu ta goge hawayen fuskarta. Ta kalli Maimuna da ke kallanta cike da tausayawa tace bayan ta yamutsa fuska saboda yanda take jin jikinta.
"Ɗauki mukullin can ki je sashen Sa'adah ki duba min halin da take ciki cikin dabara, ki gano min abin da ta haifa." Ta ƙare tana sake share hawaye zuciyarta na bugawa da ƙarfin gaske.
"Toh Hajiya." Maimuna ta faɗa tana ficewa daga ɗakin.
"Na shiga 3 ni en nan.." Mom ta sake faɗa tana fashewa da wani sabon kukan idanunta a kan mataccen jaririnta.
Bayan shuɗewar wasu mintuna har lokacin Mom ba ta motsa daga inda take ba, se ga Maimuna ta faɗo ɗakin kamar wadda aka jefo. Har wani haki take yi, ta ƙaraso kusa da gadon ta tsaya, a gaggauce kamar wadda aka biyo tace
"Hajiya en biyu ne ta haifa.. Wallahi na rantse da girman Allah Hajiya en biyu ne." Maimuna ta faɗa gaba ɗaya jikinta na wani irin karkarwa. Tashin da Mom ba ta shirya ba se ganinta na yi kawai ta miƙe zaune, idanun nan kamar za su faɗo ƙasa tace
"En biyu kuma? An ya lafiyarki ƙalau kuwa?"
"Wallahi da gaske nake Hajiya.. Na duba su kuma duk maza ne.." Suman zaune kawai Mom ta yi ba tare da tace uffan ba. Idan ban da jikinta da ya ɗauki rawa kai se ka ɗauka sanyi take ji. Har wani hazo_hazo ta ga yana giftawa ta wajen idanunta, bakinta kuwa wani karkarwa yake yi wanda hakan ya hanata iya furta kowacce kalma. Ban da kallan Maimuna babu abin da take yi. Ji take kamar Maimunan za ta buɗe baki ne tace mata da wasa take yi. Mommahn na can rai a hannun Allah, abin da ta haifa kuma ya koma. Se ga shi yanzu ta zo tana mata wani wasan kwaikwayo..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO64*
___Ta ɗauki kusan mintuna 2 har lokacin ta kasa furta komai. A hankali kuma ta juya ta kalli mataccen jinjirinta da ke gefe a kwance. Kawai se ta fashe da kuka me sauti, ta shiga girgiza kai cikin rashin sanin abin yi.
"Ki yi haƙuri Hajiya.. Don Allah ki dena wannan kukan.." Shi ne abin da Maimuna ta faɗa tana kallan Mom ɗin cike da tausayawa. Hannu Mom ta kai fuskarta ta shiga ƙarar da hawayen da ke kan fuskarta da hannunta. Gaba ɗaya ita ta ma manta da yanda take jin jikinta, burinta ta nemowa kanta mafita kafin lokaci ya ƙure mata.
"A yaya kika samu Sa'adah?" Mom ta faɗa tana kallan Maimuna cikin idanunta. Se da ta ɗan yi shiru sannan tace bayan ta girgiza kai
"Duk da hankalina na kan abin da ta haifa.. Amma da ƙyar ne idan tana da rai fa. Dan wallahi ban ga alamar tana motsi ba. Idan kuwa tana yi to dab take da ƙarasawa.." Hannu Mom ta saka ta ɗauki jaririn da ta haifa, duk da yanda hannunta ke rawa hakan be hanata miƙawa Maimunatu shi ba tace lokacin da ƙirjinta ya buga kamar wadda ke jin tsoro.
"Je ki ajje mata wannan.. ki ɗauko min nata yaran da ta haifa." Kallan yaron Maimuna ta yi da sauri tana jin yanda cikin ƙanƙanin lokaci zuciyarta ta soma harbawa fiye da ƙa'ida. Muryarta har rawa take yi wajen furta
"Ha..jiya.." Wani banzan kallo Mom ta watsawa Maimuna tana ji kamar ta miƙe ta je ta aiwatar da abin da zuciyarta ta raya mata, ta kuma yi na'am da hakan ba tare da wani dogon tunani ba.
"Ba za ki yi ba ne in tashi da kaina in je in yi?" Da sauri Maimuna ta girgiza kai tana faɗin
"Ba haka ba ne Hajiya.. Kawai dai ina jin tsoro ne wallahi.. Kar in je a kama ni."
"Waye ze kama ki? Babu kowa cikin gidan nan.. Kin kuma san duk mazan da ke cikin gidan suna can suna harkokinsu. Faɗa min wanda ze ganki?" Ajiyar zuciya Maimuna ta sauke kafin tace komai Mom ta ɗora da faɗin
"Ki yi min wannan taimakon Maimuna. Jikina babu daɗi, ba ni da ƙarfin da zan tashi na je na ɗauko jarirai har biyu.. ina ganin kafin na zo nan an kama ni.. Ki taimaka ki min wannan taimakon Maimuna, ko kuwa da ma ba zaman amana muke yi da ke ba?" Hannunta Maimuna ta kamo ta riƙe tace
"A'ah Hajiya.. Zan iya miki ko wanne irin taimako ne.. Kin fi ƙarfin haka a wajena. Wannan ɗin ma kawai dan ina jin tsoro ne, amma kuma yanzu kin ƙarfafa min gwuiwa, dan haka ki jira dawowata yanzun nan." Wani irin sanyi Mom ta ji ya ratsata har cikin ranta. Ta ji tamkar ta miƙe ta rungume Maimunan, se dai ba ta da wannan ƙarfin. Hasali ma jikinta duk babu kyau, amma ta fi burin ganin samun yaran kafin ta dawo ta yi ta kanta.
"Na gode sosai Maimuna.." Mom ta faɗa daidai lokacin da Maimunan ke dab da ficewa daga ɗakin. Kamar wadda aka tsayar se ta dakata, ta juyo ta kalli Mom tace
"Hajiya ga shawara.. Ki ɗauki ɗaya ki bar mata ɗaya, tun da kin ga kowa ya san abin da za ki haifa ba biyu ba ne." Wata harara da ba ta shirya zuwanta ba ita ta makawa Maimuna, tace a fusace
"Ashe ma ba ni da hankali.. toh me kenan na yi? Da in yi hakan ba gwara na bar mata gaba ɗaya 'ya'yan ba. Ba na so ne ya zamana tana da ɗa ko ɗaya cikin gidan nan.. Maza ki je ki kwaso min su, kafin wani ya shigo gidan nan."
"Shi kenan.." Se a lokacin sannan Maimuna ta saka hannunta ta karɓi mataccen jaririn Mom ɗin. Ba tare da ta sake cewa komai ba ta fice daga cikin ɗakin, Mom ta runtse idanunta cike da fatan Maimunan ta je lafiya ta dawo lafiya tare da jira_jiran nan. Ba kuma tare da kowa ya ganta ba.
"Ki taimaka min kawai.. Babu inda zan je wallahi.." Shi ne abin da Mom ta faɗa tana sauke numfashi a wahalce. Maimuna ta sake binta da kallo jikinta na matuƙar karkarwa. Ta rasa yanda za ta yi, ta kuma rasa fa'idar Mom ɗin na hanata kiran Daddy. Hakan ne ya sanyata zubawa sarautar Allah ido. Aikuwa cikin taimakonsa babu ɗaukar wani lokaci Mom ta haihu a kan gadonta. Ta sauke wata ƙatuwar ajiyar zuciya tana komawa kan gadon idanunta a rufe tana sauke ajiyar zuciya. Ta kai wajen minti 1 a haka tana jiran jin kukan jinjiri ko hakan ze alamta mata jinsin da ta haifa, se dai ba ta ji komai ba. Ita sam ba ta jikinta take ba, ba ta lafiyarta ko lafiyar abin da ta haifa take ba, a'ah ita burinta kawai ta ji Maimunan tace mata namiji ta haifa. Hakan ne ya sanyata kallan Maimuna da Babyn ke hannunta tace
"Me na haifa? Maza ki faɗa min me na haifa?" Kallanta Maimuna ta yi, fuskarta kamar ɗauke da farin ciki, kamar kuma ɗauke da akasin hakan. Muryarta a ɗan raunane tace
"Namiji!!" Komawa Mom ta yi ta baje a kan gadon tana faɗin
"Allah na gode maka.. Alhamdulillah." Ta faɗa tana lumshe idanunta.
"Hajiya duba shi ki ga.. kamar ba ya motsi." Maimuna ta faɗa bayan shuɗewar wasu mintuna tana cigaba da tattaɓa yaron ta ji ko yana motsi. Ƙirjin Mom ya buga da ƙarfin gaske. Ta ɗaga jajayen idanunta ta watsawa Maimunan da take ji kamar ta miƙe ta shaƙo wuyanta. Hannunta na rawa ta sanya wajen karɓar yaron a hannun Maimuna, se kuwa ya biyo hannunta. Ta sake jin wata sabuwar faɗuwar gaban ta ziyarceta. Amma duk da haka ba ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen tattaɓa shi ko za ta ga ya yi motsi kamar yanda jarirai ke yi, se dai sam be yi ba. Hasalima kamar yanda Maimunan ta faɗa babu rai a tare da yaron. Rungume shi Mom ta yi tana faɗin
"Na shiga 3 ni Salma.. Na shiga 3 na lalace." Ta faɗa ilahirin jikinta na rawa saboda tsananin tashin hankali. Kamar kuma wadda aka kunna se ta ajje jaririn a gefenta tana saka hannu ta goge hawayen fuskarta. Ta kalli Maimuna da ke kallanta cike da tausayawa tace bayan ta yamutsa fuska saboda yanda take jin jikinta.
"Ɗauki mukullin can ki je sashen Sa'adah ki duba min halin da take ciki cikin dabara, ki gano min abin da ta haifa." Ta ƙare tana sake share hawaye zuciyarta na bugawa da ƙarfin gaske.
"Toh Hajiya." Maimuna ta faɗa tana ficewa daga ɗakin.
"Na shiga 3 ni en nan.." Mom ta sake faɗa tana fashewa da wani sabon kukan idanunta a kan mataccen jaririnta.
Bayan shuɗewar wasu mintuna har lokacin Mom ba ta motsa daga inda take ba, se ga Maimuna ta faɗo ɗakin kamar wadda aka jefo. Har wani haki take yi, ta ƙaraso kusa da gadon ta tsaya, a gaggauce kamar wadda aka biyo tace
"Hajiya en biyu ne ta haifa.. Wallahi na rantse da girman Allah Hajiya en biyu ne." Maimuna ta faɗa gaba ɗaya jikinta na wani irin karkarwa. Tashin da Mom ba ta shirya ba se ganinta na yi kawai ta miƙe zaune, idanun nan kamar za su faɗo ƙasa tace
"En biyu kuma? An ya lafiyarki ƙalau kuwa?"
"Wallahi da gaske nake Hajiya.. Na duba su kuma duk maza ne.." Suman zaune kawai Mom ta yi ba tare da tace uffan ba. Idan ban da jikinta da ya ɗauki rawa kai se ka ɗauka sanyi take ji. Har wani hazo_hazo ta ga yana giftawa ta wajen idanunta, bakinta kuwa wani karkarwa yake yi wanda hakan ya hanata iya furta kowacce kalma. Ban da kallan Maimuna babu abin da take yi. Ji take kamar Maimunan za ta buɗe baki ne tace mata da wasa take yi. Mommahn na can rai a hannun Allah, abin da ta haifa kuma ya koma. Se ga shi yanzu ta zo tana mata wani wasan kwaikwayo..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO64*
___Ta ɗauki kusan mintuna 2 har lokacin ta kasa furta komai. A hankali kuma ta juya ta kalli mataccen jinjirinta da ke gefe a kwance. Kawai se ta fashe da kuka me sauti, ta shiga girgiza kai cikin rashin sanin abin yi.
"Ki yi haƙuri Hajiya.. Don Allah ki dena wannan kukan.." Shi ne abin da Maimuna ta faɗa tana kallan Mom ɗin cike da tausayawa. Hannu Mom ta kai fuskarta ta shiga ƙarar da hawayen da ke kan fuskarta da hannunta. Gaba ɗaya ita ta ma manta da yanda take jin jikinta, burinta ta nemowa kanta mafita kafin lokaci ya ƙure mata.
"A yaya kika samu Sa'adah?" Mom ta faɗa tana kallan Maimuna cikin idanunta. Se da ta ɗan yi shiru sannan tace bayan ta girgiza kai
"Duk da hankalina na kan abin da ta haifa.. Amma da ƙyar ne idan tana da rai fa. Dan wallahi ban ga alamar tana motsi ba. Idan kuwa tana yi to dab take da ƙarasawa.." Hannu Mom ta saka ta ɗauki jaririn da ta haifa, duk da yanda hannunta ke rawa hakan be hanata miƙawa Maimunatu shi ba tace lokacin da ƙirjinta ya buga kamar wadda ke jin tsoro.
"Je ki ajje mata wannan.. ki ɗauko min nata yaran da ta haifa." Kallan yaron Maimuna ta yi da sauri tana jin yanda cikin ƙanƙanin lokaci zuciyarta ta soma harbawa fiye da ƙa'ida. Muryarta har rawa take yi wajen furta
"Ha..jiya.." Wani banzan kallo Mom ta watsawa Maimuna tana ji kamar ta miƙe ta je ta aiwatar da abin da zuciyarta ta raya mata, ta kuma yi na'am da hakan ba tare da wani dogon tunani ba.
"Ba za ki yi ba ne in tashi da kaina in je in yi?" Da sauri Maimuna ta girgiza kai tana faɗin
"Ba haka ba ne Hajiya.. Kawai dai ina jin tsoro ne wallahi.. Kar in je a kama ni."
"Waye ze kama ki? Babu kowa cikin gidan nan.. Kin kuma san duk mazan da ke cikin gidan suna can suna harkokinsu. Faɗa min wanda ze ganki?" Ajiyar zuciya Maimuna ta sauke kafin tace komai Mom ta ɗora da faɗin
"Ki yi min wannan taimakon Maimuna. Jikina babu daɗi, ba ni da ƙarfin da zan tashi na je na ɗauko jarirai har biyu.. ina ganin kafin na zo nan an kama ni.. Ki taimaka ki min wannan taimakon Maimuna, ko kuwa da ma ba zaman amana muke yi da ke ba?" Hannunta Maimuna ta kamo ta riƙe tace
"A'ah Hajiya.. Zan iya miki ko wanne irin taimako ne.. Kin fi ƙarfin haka a wajena. Wannan ɗin ma kawai dan ina jin tsoro ne, amma kuma yanzu kin ƙarfafa min gwuiwa, dan haka ki jira dawowata yanzun nan." Wani irin sanyi Mom ta ji ya ratsata har cikin ranta. Ta ji tamkar ta miƙe ta rungume Maimunan, se dai ba ta da wannan ƙarfin. Hasali ma jikinta duk babu kyau, amma ta fi burin ganin samun yaran kafin ta dawo ta yi ta kanta.
"Na gode sosai Maimuna.." Mom ta faɗa daidai lokacin da Maimunan ke dab da ficewa daga ɗakin. Kamar wadda aka tsayar se ta dakata, ta juyo ta kalli Mom tace
"Hajiya ga shawara.. Ki ɗauki ɗaya ki bar mata ɗaya, tun da kin ga kowa ya san abin da za ki haifa ba biyu ba ne." Wata harara da ba ta shirya zuwanta ba ita ta makawa Maimuna, tace a fusace
"Ashe ma ba ni da hankali.. toh me kenan na yi? Da in yi hakan ba gwara na bar mata gaba ɗaya 'ya'yan ba. Ba na so ne ya zamana tana da ɗa ko ɗaya cikin gidan nan.. Maza ki je ki kwaso min su, kafin wani ya shigo gidan nan."
"Shi kenan.." Se a lokacin sannan Maimuna ta saka hannunta ta karɓi mataccen jaririn Mom ɗin. Ba tare da ta sake cewa komai ba ta fice daga cikin ɗakin, Mom ta runtse idanunta cike da fatan Maimunan ta je lafiya ta dawo lafiya tare da jira_jiran nan. Ba kuma tare da kowa ya ganta ba.