Sashe 112
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allah Ya saka da alkhairi Abeey, Ya ƙara arziƙi me amfani." Murmushi kawai Daddy ya yi. Shi kam idan be yi wa su Abeey abu ba su wa ya kamata ya yi wa? Mutanen da suka renar masa ɗa tun yana jinjiri har girma. Lokacin da ya je wa da Ummeey da maganar Daddyn ba ƙaramin farin ciki ta yi ba. Ta shiga kwararowa Daddyn addu'o'i cike kuma da fatan Allah Ya sa a dace. Cikin ƙanƙanin lokaci Daddy ya shiga shirya musu tafiyar. Cikin haka ne kuma Mommah ta bayar da shawarar tafiya tare da Didi da Areef su ma su je su ziyarci ɗakin Allah, su kuma roƙawa Abeeyn lafiya. Gefe guda kuma kafin su dawo ginin gidan da ake musu duka ya kammala, an gama komai a tsanake. Idan ya so suna dawowa se su yi can ɗin. Su ma kuma su Ummeey su shige nasu gidan. Da ma tafiyar za a yita ne tare da Lulu tun da sai mijinta ma ze je. Shi kenan yanzu se su tafi gaba ɗaya. Sosai Daddy ya yi na'am da shawarar Mommahn, dan haka babu ɓata lokaci aka fara duk wasu shirye shiryen tafiyar har da su gaba ɗaya.
.. A ɓangarensu Mom kuwa ana can gidan yari an soma girbar abin da aka shuka, zuwa lokacin ta yi laushi matuƙa. Maimunatu kuwa da ma tuntuni ta tuba ta bi Allah. Wannan dalilin ne ma ya sa Daddy ya roƙa mata sassauci ko dan albarkacin tona wannan ɓoyayyan sirrin da ta yi, wanda idan ba dan Allah Ya sa ta tona ba, da tuni ba wannan zancen ake ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO82*
___ Cikin ƙanƙanin lokaci suka cigaba da shirye-shiryen tafiya Saudiyyar. Ta gefe guda kuma har lokacin Abeey na asibiti ana cigaba da kula da lafiyarsa. Kwanakin da suka ɗauka na shirye shiryen cikin kuma kwanakin ne kowanne ya sake zage damtse wajen kula da matarsa. Hakan ne kuma dalili da ya sa shaƙuwa sosai ta shiga tsakaninsu. Musamman ta ɓangaren Gwani da Lulu, da yanzu ta gama bayar da kai bori ya hau. Ta saki jikinta ta maida hankali wajen kula da mijinta da yanzun take matuƙar ƙauna, shi ma kuma ta ɓangarensa hakan ne. Ɓangaren Bad Man da Didi ma sosai ake samun cigaba, musamman da ya kasance Bad Man ɗin ɗan soyayya ne. Kai idan yana wani abun se ka ɗauka ya taɓa samun wani horo ne na musamman a kan soyayya. Kulawa da kuma soyayyar da yake nuna mata ita ce silar da ta sa take iya ƙoƙarinta wajen ganin ta faranta masa, ta kuma saki jikinta gaba ɗaya da shi, tun da dai ta san tana ƙaunarsa. Musamman a kwanakin nan da ƙaunar tasa take ƙaruwa a cikin zuciyarta saboda tsananin kulawarsa gareta.
.. A compound ɗin gidan suka rabu da Kaseem, kai tsaye sashensu ya wuce. A gajiye yake liƙis, dan haka duk wani burinsa be wuce ya watsa ruwa a jikinsa ya zo ya baje ba. A nutse ya tura ƙofar ɗakin duk da baccin da yake ji amma idanunsa na cike da fatan ya ganta. Saboda tun safe ya fita daga gidan se yanzu ya shigo. A kishingiɗe ya sameta kan kujera tana bacci, hannunta ɗauke da littafi, da alama karatu take bacci ya ɗauketa. Ƙarasawa ya yi yana murmushi. A hankali ya saka hannunsa ya ɗagata gaba ɗaya ya maidata kan gado. A nutse ya kai bakinsa kan goshinta ya yi kissing. Kafin ya sauko da bakin nasa kan cute lips ɗinta da suka sake tsukewa saboda baccin da take. Sumbata me ɗan tsayi ya bawa bakin nata. Har se da hakan ya farkar da ita. Cikin kulawa da karyar da kai yace
"Tuba nake." Se ta tura red lips ɗin nata da ya sake yin ja saboda sumbatar da ya sha tana ɗan murza idanunta. Har ga Allah baccin ya mata daɗi. Ta ji daɗinsa, duk da ba tare da ta sani ba ya ɗauketa. Ganin da gasken bacci take ji, ya sanya shi miƙewa tsaye. Ya sake kallanta a nutse yace
"Baccin ne?" Jinjina kai ta yi tana sake lumshe idanunta kamar er maye. Kallanta ya yi sosai kafin yace
"Toh mu je ki samu ki watsa ruwa ke ma." Ya yi maganar ba tare da ya jira amsarta ba ya ɗauketa gaba ɗaya. Kai tsaye toilet ya wuce da ita, ya kulle ƙofar. Ganin da ya yi baccin da take ji ya fi nasa ya sanya shi sauƙaƙe mata wahala ya wanketa tass, kafin ya wanke kansa. Ai gaba ɗaya baccin ji ta yi ya tafi babu alamunsa. Dan kuwa ita dai har yanzu ta kasa sakin jikinta gaba ɗaya. Har yanzu wannan kunyar akwai ta. Dan haka yanzun ma ji ta yi kamar ta nutse dan kunya, musamman da ta ga yana abubuwansa ko a jikinsa shi kam. Se ita yake bari da kunya kullum. Ko da suka fito ma be ƙyaleta ba, duk da yanda take ta zillewa a kan za ta shirya da kanta, ya ƙi barinta se da ya shiryata tsaff cikin wata doguwar rigar bacci mara nauyi kamin yace yana kallanta
"Ni ba ki shirya ni ba." Ya ƙare maganar a marairaice se ka ce wani maraya. Ɗaga narkakkun idanunta ta yi ta kalle shi. Tilas murmushi ya suɓuce mata ta sunkuyar da kanta.
"In haƙura koh? Ni ba wanda ke sona." Ya sake marairaice murya fiye da ɗazun. Yanzu kam da sauri ta ɗaga idanunta ta kalle shi.
"A'ah fa ni dai ba.." Se kuma ta ƙi ƙarasawa. Jinjina mata kai ya yi sau ɗaya alamar ta ƙarasa. Se ta turo baki kawai ba tace komai ba. Kawai se ya yi murmushi yana girgiza kai. Duk wani ƙoƙari da ze yi se ya yi shi wannan kunyar ta ajjiyeta. Se da ya shirya tsaff cikin rigar bacci kafin ya dawo inda ya barta kamar saƙaguwa. Surarta ya yi zuwa kan gadon, ya kwantar. Kafin shi ma ya kwanta yana ɗan lumshe idanunsa jin baccin ya dawo. Ya ja ta cikin jikinsa ya rungume yana gyara kwanciyarsa yanda za ta ji daɗin kwanciyar kafin ya ja musu bargon ya lulluɓe su. Ya kai wajen minti 5 yana jin yanda bugun zuciyarsu ke fita a tare. Ya buɗe baki da niyyar yi mata magana, se ya lura da yanda numfashinta ke sauka a kan wuyansa a hankali. Da sauri ya leƙa fuskarta cike da mamaki, dan be yi tunanin a ɗan wannan lokacin har ta yi bacci ba. Se dai da alama ba ma yanzu ta yi baccin ba, kawai dai se yanzu ya yi nisa. Ya sake gyara mata kwanciyar kafin ya lumshe idanunsa shi ma.
... Kai tsaye palourn Mommah suka wuce, suna sanye cikin wata atamfa me kyau, ɗinkin riga da skirt. Sun yi mugun kyau, kamaninsu sun sake fitowa sosai musamman da suke cikin kaya iri ɗaya. Se dai yanzu kam a kallan farko za ka fahimci yanda Lulu ta fi Didi murjewar jiki. Dab da za su shiga ɗakin Mommahn Didi tace
"Allah kuwa Lulu yanzu kin zama er lukuta." Didi ta faɗa tana ɓoye dariyarta. Harara Lulu ta ɓalla mata kafin tace
"Wallahi ba wani nan." Ta faɗa tana tura bakinta gaba.
"Kin ga fa yanda kayan nan suka miki.. Chaɓɓ..!"
"Allah Didi ba na so.." Lulu ta katseta da faɗin hakan tana bubbuga ƙafa kamar za ta saka ihu. Se da Didi ta yi dariyarta kafin ta tsuke bakinta ta yi shiru. Kafin kuma tace
"Shi kenan, yi haƙuri." Didi ta faɗa. Maƙe kafaɗa Lulu ta yi ba tace komai ba. Didi ta langaɓar da kanta tana kama kunnenta, tace a marairaice
"Pls mana.." Se kuma Lulun ta yi murmushi kafin tace
"Na haƙura." A haka suka ƙarasa cikin ɗakin Mommahn. A palour suka sameta, tana magana da Baba Atine. Suka ƙarasa da sallama ɗauke a bakunansu. Da fara'a Mommah ta karɓe su, cike da jin daɗin zuwansu. Baba Atine ma miƙewa ta yi tana musu barka da zuwa. Suka amsa suna neman waje suka zauna. Se da suka gaisa da Baba Atine kafin ta yi sallama da uwar ɗakin nata ta fice daga ɗakin.
"Barkanku da zuwa.." Mommah ta sake faɗa da murmushi ɗauke a kan fuskarta. Kusan a tare suka amsa da
"Barka dai Mommah."
"Ya shirye shirye?" Ta tambaya tana kallansu.
"Alhamdulillah." Nan ma suka amsa a tare.
"Allah Ya taimaka, Ya nuna mana lokacin, Ya kai ku lafiya Ya kuma dawo mana da ku lafiya."
"Ameen." Maida dubanta kan Lulu Mommah ta yi tace cikin kulawa
"Ya jikin naki Daughter? Fatan dai babu abin da ke damunki?" Ɗan murmushi Lulu ta yi tana murza hannunta da ɗayan hannunta kafin tace
"Eh."
"Kin tabbatar?"
"Ehh Mommah." Ta ba ta amsa har lokacin ba ta kalleta ba. Mommah ta yi murmushi tana maida dubanta kan Didi.
"Afrah ya wajen naki? Ina fata dai babu matsala?" Ta yi tambayar da kodayaushe ba ta gajiya da yinta, kullum kuma cikin fatan amsar da za ta fito daga bakin Didin ta kasance "Ehh" ne.
"Ehh Mommah." Didi ta faɗi hakan. Murmushi Mommah ta yi kafin tace
"Toh madallah.." Daga haka se suka ɗan taɓa hira, har zuwa lokacin da Mommah ta umarce su suka fice daga ɗakin. Kai tsaye compound suka wuce driver ya ɗauke su zuwa gida, bayan Mommah ta bayar da saƙo a kai wa Ammi har ma da Little.
Ammi sam ba ta san da zuwansu ba, dan haka tana zaune cikin ɗaki ita da Little tana koya masa hadda, sallamar en biyun nata ta ratsa kunnenta. Kusan a tare suka ɗaga kai ita da Little suka kalle su. A guje Little ya sauka daga kan kujerar har yana ƙoƙarin kifawa ya ƙarasa ya rungume en uwan nasa.
.. A ɓangarensu Mom kuwa ana can gidan yari an soma girbar abin da aka shuka, zuwa lokacin ta yi laushi matuƙa. Maimunatu kuwa da ma tuntuni ta tuba ta bi Allah. Wannan dalilin ne ma ya sa Daddy ya roƙa mata sassauci ko dan albarkacin tona wannan ɓoyayyan sirrin da ta yi, wanda idan ba dan Allah Ya sa ta tona ba, da tuni ba wannan zancen ake ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO82*
___ Cikin ƙanƙanin lokaci suka cigaba da shirye-shiryen tafiya Saudiyyar. Ta gefe guda kuma har lokacin Abeey na asibiti ana cigaba da kula da lafiyarsa. Kwanakin da suka ɗauka na shirye shiryen cikin kuma kwanakin ne kowanne ya sake zage damtse wajen kula da matarsa. Hakan ne kuma dalili da ya sa shaƙuwa sosai ta shiga tsakaninsu. Musamman ta ɓangaren Gwani da Lulu, da yanzu ta gama bayar da kai bori ya hau. Ta saki jikinta ta maida hankali wajen kula da mijinta da yanzun take matuƙar ƙauna, shi ma kuma ta ɓangarensa hakan ne. Ɓangaren Bad Man da Didi ma sosai ake samun cigaba, musamman da ya kasance Bad Man ɗin ɗan soyayya ne. Kai idan yana wani abun se ka ɗauka ya taɓa samun wani horo ne na musamman a kan soyayya. Kulawa da kuma soyayyar da yake nuna mata ita ce silar da ta sa take iya ƙoƙarinta wajen ganin ta faranta masa, ta kuma saki jikinta gaba ɗaya da shi, tun da dai ta san tana ƙaunarsa. Musamman a kwanakin nan da ƙaunar tasa take ƙaruwa a cikin zuciyarta saboda tsananin kulawarsa gareta.
.. A compound ɗin gidan suka rabu da Kaseem, kai tsaye sashensu ya wuce. A gajiye yake liƙis, dan haka duk wani burinsa be wuce ya watsa ruwa a jikinsa ya zo ya baje ba. A nutse ya tura ƙofar ɗakin duk da baccin da yake ji amma idanunsa na cike da fatan ya ganta. Saboda tun safe ya fita daga gidan se yanzu ya shigo. A kishingiɗe ya sameta kan kujera tana bacci, hannunta ɗauke da littafi, da alama karatu take bacci ya ɗauketa. Ƙarasawa ya yi yana murmushi. A hankali ya saka hannunsa ya ɗagata gaba ɗaya ya maidata kan gado. A nutse ya kai bakinsa kan goshinta ya yi kissing. Kafin ya sauko da bakin nasa kan cute lips ɗinta da suka sake tsukewa saboda baccin da take. Sumbata me ɗan tsayi ya bawa bakin nata. Har se da hakan ya farkar da ita. Cikin kulawa da karyar da kai yace
"Tuba nake." Se ta tura red lips ɗin nata da ya sake yin ja saboda sumbatar da ya sha tana ɗan murza idanunta. Har ga Allah baccin ya mata daɗi. Ta ji daɗinsa, duk da ba tare da ta sani ba ya ɗauketa. Ganin da gasken bacci take ji, ya sanya shi miƙewa tsaye. Ya sake kallanta a nutse yace
"Baccin ne?" Jinjina kai ta yi tana sake lumshe idanunta kamar er maye. Kallanta ya yi sosai kafin yace
"Toh mu je ki samu ki watsa ruwa ke ma." Ya yi maganar ba tare da ya jira amsarta ba ya ɗauketa gaba ɗaya. Kai tsaye toilet ya wuce da ita, ya kulle ƙofar. Ganin da ya yi baccin da take ji ya fi nasa ya sanya shi sauƙaƙe mata wahala ya wanketa tass, kafin ya wanke kansa. Ai gaba ɗaya baccin ji ta yi ya tafi babu alamunsa. Dan kuwa ita dai har yanzu ta kasa sakin jikinta gaba ɗaya. Har yanzu wannan kunyar akwai ta. Dan haka yanzun ma ji ta yi kamar ta nutse dan kunya, musamman da ta ga yana abubuwansa ko a jikinsa shi kam. Se ita yake bari da kunya kullum. Ko da suka fito ma be ƙyaleta ba, duk da yanda take ta zillewa a kan za ta shirya da kanta, ya ƙi barinta se da ya shiryata tsaff cikin wata doguwar rigar bacci mara nauyi kamin yace yana kallanta
"Ni ba ki shirya ni ba." Ya ƙare maganar a marairaice se ka ce wani maraya. Ɗaga narkakkun idanunta ta yi ta kalle shi. Tilas murmushi ya suɓuce mata ta sunkuyar da kanta.
"In haƙura koh? Ni ba wanda ke sona." Ya sake marairaice murya fiye da ɗazun. Yanzu kam da sauri ta ɗaga idanunta ta kalle shi.
"A'ah fa ni dai ba.." Se kuma ta ƙi ƙarasawa. Jinjina mata kai ya yi sau ɗaya alamar ta ƙarasa. Se ta turo baki kawai ba tace komai ba. Kawai se ya yi murmushi yana girgiza kai. Duk wani ƙoƙari da ze yi se ya yi shi wannan kunyar ta ajjiyeta. Se da ya shirya tsaff cikin rigar bacci kafin ya dawo inda ya barta kamar saƙaguwa. Surarta ya yi zuwa kan gadon, ya kwantar. Kafin shi ma ya kwanta yana ɗan lumshe idanunsa jin baccin ya dawo. Ya ja ta cikin jikinsa ya rungume yana gyara kwanciyarsa yanda za ta ji daɗin kwanciyar kafin ya ja musu bargon ya lulluɓe su. Ya kai wajen minti 5 yana jin yanda bugun zuciyarsu ke fita a tare. Ya buɗe baki da niyyar yi mata magana, se ya lura da yanda numfashinta ke sauka a kan wuyansa a hankali. Da sauri ya leƙa fuskarta cike da mamaki, dan be yi tunanin a ɗan wannan lokacin har ta yi bacci ba. Se dai da alama ba ma yanzu ta yi baccin ba, kawai dai se yanzu ya yi nisa. Ya sake gyara mata kwanciyar kafin ya lumshe idanunsa shi ma.
... Kai tsaye palourn Mommah suka wuce, suna sanye cikin wata atamfa me kyau, ɗinkin riga da skirt. Sun yi mugun kyau, kamaninsu sun sake fitowa sosai musamman da suke cikin kaya iri ɗaya. Se dai yanzu kam a kallan farko za ka fahimci yanda Lulu ta fi Didi murjewar jiki. Dab da za su shiga ɗakin Mommahn Didi tace
"Allah kuwa Lulu yanzu kin zama er lukuta." Didi ta faɗa tana ɓoye dariyarta. Harara Lulu ta ɓalla mata kafin tace
"Wallahi ba wani nan." Ta faɗa tana tura bakinta gaba.
"Kin ga fa yanda kayan nan suka miki.. Chaɓɓ..!"
"Allah Didi ba na so.." Lulu ta katseta da faɗin hakan tana bubbuga ƙafa kamar za ta saka ihu. Se da Didi ta yi dariyarta kafin ta tsuke bakinta ta yi shiru. Kafin kuma tace
"Shi kenan, yi haƙuri." Didi ta faɗa. Maƙe kafaɗa Lulu ta yi ba tace komai ba. Didi ta langaɓar da kanta tana kama kunnenta, tace a marairaice
"Pls mana.." Se kuma Lulun ta yi murmushi kafin tace
"Na haƙura." A haka suka ƙarasa cikin ɗakin Mommahn. A palour suka sameta, tana magana da Baba Atine. Suka ƙarasa da sallama ɗauke a bakunansu. Da fara'a Mommah ta karɓe su, cike da jin daɗin zuwansu. Baba Atine ma miƙewa ta yi tana musu barka da zuwa. Suka amsa suna neman waje suka zauna. Se da suka gaisa da Baba Atine kafin ta yi sallama da uwar ɗakin nata ta fice daga ɗakin.
"Barkanku da zuwa.." Mommah ta sake faɗa da murmushi ɗauke a kan fuskarta. Kusan a tare suka amsa da
"Barka dai Mommah."
"Ya shirye shirye?" Ta tambaya tana kallansu.
"Alhamdulillah." Nan ma suka amsa a tare.
"Allah Ya taimaka, Ya nuna mana lokacin, Ya kai ku lafiya Ya kuma dawo mana da ku lafiya."
"Ameen." Maida dubanta kan Lulu Mommah ta yi tace cikin kulawa
"Ya jikin naki Daughter? Fatan dai babu abin da ke damunki?" Ɗan murmushi Lulu ta yi tana murza hannunta da ɗayan hannunta kafin tace
"Eh."
"Kin tabbatar?"
"Ehh Mommah." Ta ba ta amsa har lokacin ba ta kalleta ba. Mommah ta yi murmushi tana maida dubanta kan Didi.
"Afrah ya wajen naki? Ina fata dai babu matsala?" Ta yi tambayar da kodayaushe ba ta gajiya da yinta, kullum kuma cikin fatan amsar da za ta fito daga bakin Didin ta kasance "Ehh" ne.
"Ehh Mommah." Didi ta faɗi hakan. Murmushi Mommah ta yi kafin tace
"Toh madallah.." Daga haka se suka ɗan taɓa hira, har zuwa lokacin da Mommah ta umarce su suka fice daga ɗakin. Kai tsaye compound suka wuce driver ya ɗauke su zuwa gida, bayan Mommah ta bayar da saƙo a kai wa Ammi har ma da Little.
Ammi sam ba ta san da zuwansu ba, dan haka tana zaune cikin ɗaki ita da Little tana koya masa hadda, sallamar en biyun nata ta ratsa kunnenta. Kusan a tare suka ɗaga kai ita da Little suka kalle su. A guje Little ya sauka daga kan kujerar har yana ƙoƙarin kifawa ya ƙarasa ya rungume en uwan nasa.