Sashe 119
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ko dai Babyna ne?" Ya yi maganar yana ɗora hannunsa a kan cikinta da ya ƙara girma sosai. Kallan hannun nasa ta yi na tsawon sakanni kamar me nazari, se kuma ta girgiza kai tana kai hannunta ta ɗora a kan nasa hannun lokaci ɗaya tana lumshe idanunta. Murmushi ya yi kafin yace
"Yawwah ko ke fa.." Daidai lokacin ta buɗe idanunta
"Wajen Lulu zan je.." Ta faɗa bayan ta ɗora idanunta a kan fuskarsa. Cike da mamaki yace
"Lulu kuma? Me ya faru?" Girgiza kai ta yi tana ƙoƙarin miƙewa tace
"Ni dai wajenta zan je.. Ina so in ganta." Da sauri ya miƙe, ya riƙota sosai yana sake tambayarta lafiya?
"Ba komai, so nake na ganta." Amsar da take ta ba shi kenan. Shi dai abun mamaki yake ba shi, se ka ce wadda za ta fara ganin Afaaf ɗin yau? Anya kuwa? Ko dai akwai wani abun da ya faru ne be sani ba? Ganin da ya yi ta ƙi ba shi haɗin kai ne ya sanya shi janta cikin jikinsa ya rungume. Ya ɗora hannunsa duka biyu a bayanta, cikin rarrashi yake faɗin
"Ki nutsu! Ki nutsu Uhmm?" Da sauri sauri numfashinta ke fita tamkar wadda ta yi tsere. Zuwa can kuma se ya koma fita daidai. Ya sauke numfashi daidai lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi.
"Wajen Lulu zan je." Ta sake faɗa tana kallansa.
"Iko sai Allah." Ya faɗa yana ƙura mata idanunsa.
"Shi kenan mu je na raka ki." Wata ajiyar zuciya ta sauke tana yin gaba. Ya bi ta da kallo. A kan laɓɓansa ya furta
"Rigima dai kawai." kafin ya girgiza kai yana murmushi lokaci ɗaya yana bin bayanta.
A ɗaya ɓangaren kuwa zaune take a kan kujerar, se dai kusan fiye da awa ɗaya kenan bayan wasu mintuna ta kan kama ƙugu ta riƙe tana runtse idanunta. Kwata-kwata ta kasa zama a kan kujerar. Ita kaɗai ta san azabar da take ji. Wani irin ciwo take ji kamar za ta mutu. Ciwon da yake zuwa bayan wasu mintuna. Se ta ɗauka ta dena ji se ta ji wanda ya fi na da. Daidai lokacin Gwani ya shigo cikin ɗakin. Ya kalle ta sosai yana nazarinta. Ƙarasawa ya yi ya zauna a kusa da ita.
"Me ya faru?" Ya tambaye ta a karo na babu adadi. Saboda tun jiya yake ganinta wani iri. Da zarar ya tambaye ta se tace babu komai. Girgiza kai ta yi kafin tace komai irin ciwon da take ji ya sake dawowa. Hannunsa da ke gefenta ta dafe da ƙarfi tana runtse idanunta. Girgiza kai take tana sauke wahalallen numfashi cikin wata irin azaba da take ji. Ƙanƙame hannun nata ya yi cike da tsoro yake kallanta. Bayan wajen minti 1 ta koma sauke ajiyar zuciya. Idanunta sun yi muzu-muzu, duk ta yi wani yaɓe-yaɓe.
"Ko dai haihuwar ce?" Ya tambaya yana kallanta. Girgiza kai ta yi ta kalle shi da lumsassun idanunta tace
"Ina ganin juyi ne kawai.." Ta faɗa da muryarta da ta shige ciki saboda wahala. Shi dai haka nan kawai ya ji be yi na'am da hakan ba, ya dai yi shiru yana cigaba da nazarinta. Kanta ya ja ya kwantar a kan kafaɗarsa. Duk da jinta take kamar ba a hayyacinta ba hakan be hana ta kwantawa ɗin ba ta yi shiru a ranta tana fatan Allah Ya sa kar ciwon ya dawo. Se dai addu'ar tata ba ta karɓu ba, dan kuwa ba a ɗauki lokaci me tsayi ba ciwon da ya fi na ɗazu ya taso mata. Yanzu kam ruƙunƙume shi ta yi kamar za ta ɓalla ƙirjinsa ta shige. Cikin galabaita muryarta na rawa take faɗin
"Wayyo Allah na.. zan mutu.. Wayyo Allah na.." Abin da take iya faɗa kawai kenan, cikin lokaci ƙanƙani hankalin Gwani ya tashi. Ai babu shiri ya janyo wayarsa ya danna kiran Mommah. Mommah da ke tare da Yaya Amina a lokacin ta ɗauki wayar.
"Mommah Afaaf ba lafiya." Shi ne abin da ya faɗa ko sallama be iya yi ba.
"Ya salaam! Kuna cikin gidan ne?" Mommah ta faɗa.
"Ehh.." Ba ta ce komai ba ta katse wayar. Ta kalli Yaya Amina tace
"Tashi maza mu je.. Afaaf ba lafiya, ina kuma tunanin haihuwar ce.."
"Toh subhanallahi! Mu je.." Yaya Amina ta miƙe ta soma yafa mayafinta da ke ajje. Tare suka fita da Mommah. Kai tsaye sashensu Gwanin suka wuce. Lulun na kwance kane-kane a jikin Gwanin, dan zuwa lokacin har ta soma fita daga hayyacinta. Ciwon ke dawo mata a kai a kai babu tsayawa. Yaya Amina ce ta ƙarasa ta kamo Lulun da taimakon Gwani. Suka fito palour riƙe da ita. Se a lokacin sannan Mommah ta ƙarasa ta karɓi Gwani. Se faman jerawa Lulun da duk wata alamar wahala ta gama bayyana a tattare da ita sannu suke. Lulun da a yanzu ko ganewa ba ta yi. Daidai lokacin da suka fito daga sashen Areef da Didi suka ƙaraso bakin sashen. Gaba ɗaya idanunsu suka ɗaga suka ɗora a kansu Mommahn. A kan er uwarta idanunta suka soma sauka. Ƙirjinta ya wani irin bugawa, a take jikinta ya soma ɓari, zazzaɓin da ya so rufe ta tun ɗazu yanzu ya samu damar soma rufeta. Cikin ƙanƙanin lokaci cikinta ya yi wani daƙiƙin juyawa. Ba ta damu da hakan ba, halin da ta ga er uwarta ciki ya sanya ta mantawa ma da abin da ke cikin nata. Ba ta san lokacin da ta fincike hannunta daga cikin na Areef ba. Cikin azama kamar babu komai a jikinta ta saka kai zuwa wajen Lulun da take hangowa riƙe a hannunsu Mommah da alama ba ta cikin hayyacinta. Se dai cikin rashin sa'a ba ta kula da abin da ke gabanta ba, ta yi tuntuɓe, kafin kace me ne wannan ta faɗi a wajen. Tsautsayi ya sa ta faɗi a kan cikinta. Wani azababben zafi da tun da Ammi ta haifeta ba ta taɓa jin irinsa ba ya ziyarceta. Dalili kenan da ya sanya ta kai hannu kan cikin nata tana sakin wata ƙara cikin matsanancin azaba.
"Baby..!!!" Ya faɗa cikin ɗaga murya yana kallanta lokacin da yake durƙushe a wajen. Mommah da Yaya Amina cikin matuƙar tashin hankali suke kallan abin da ke faruwa. Kusan a lokaci guda suke sauke salati. Ga Lulu a hannunsu wadda suke dab da shigar da ita cikin mota, ga shi babu damar su zo su taimakawa Didi. Da sauri Mommah tace
"Maza ɗauke ta ka saka a mota." Inaa, shi ba ji yake ba, gaba ɗaya a hankalinsa na kan Didi da ke hannunsa, wadda take a kwance kamar babu rai a tattare da ita.
"Areef!!" Gwani ya faɗa yana dafa kafaɗar Areef ɗin. Se a lokacin sannan ya iya ɗaga jajayen idanunsa ya kalli Gwani.
"Ɗauke ta ka saka a mota mu wuce asibiti." Kamar wanda ya farka daga bacci, se ya maida dubansa kan Didi. Cikin azama ya miƙe ya saɓe ta se cikin mota. Ko driving kasawa ya yi, se sakawa ya yi ɗaya daga cikin drivers ɗin gidan ya tuƙa su. Yana baya hannunsa ɗauke da Didi da zuwa lokacin ta farfaɗo se dai kwata kwata ya kasa fahimtar abin da ke damunta. Cikinta kawai ta riƙe tana kuka gami da sallallami. Shi dai ya san cikinta be isa haihuwa ba ballantana yace ko haihuwa ce. A'ah toh me ya samu cikin? Kar dai wani abun ne ya same shi? Ya tambayi kansa har lokacin idanunsa na kan Didi
A tare suka isa asibitin. Babu ɓata lokaci aka karɓe su. I zuwa lokacin gaba ɗaya sun yi laushi sun yi tuɓus. Duk wahala ta gama jigata su. A harabar haɗɗɗen asibitin duk suke zaune, waɗanda ke a tsaye suna tsaye. Dan zuwa lokacin har Ummeey ta iso. Abun da ya bawa kowa mamaki shi ne lokacin da aka sanar musu da cewa ita ma Didi haihuwar ce ta taso mata gadan-gadan.
"Haihuwa kuma?" Areef ya tambayi kansa bayan jin abin da aka faɗa ɗin.
"Ka kwantar da hankalinka, hakan ba abun damuwa ba ne, da ma hakan kan iya faruwa.. so ba sabon abu ba ne." Yaya Amina ta faɗa wa Areef bayan ta dafa kafaɗarsa. Shi dai jinta kawai ya yi. Hakan ne ya sa be ce komai ba se jinjina kai da ya yi. Cikin ƙanƙanin lokaci kowa ya duƙufa wajen addu'a tare da fatan Allah Ya sauke su lafiya. Bayan shuɗewar awanni masu yawa ana fafatawa, ana ta gwagwarmaya, cikin ikon Allah, se ya ba su sa'a Lulu ce ta soma haifo santalelen ɗa namiji ƙato da shi. Ko minti 2 ba a yi ba Didi ma ta dire nata ɗa namijin, se dai shi be kai girman na Lulu ba. Kowannensu kawai bajewa ta yi a kan gadon jiki a matuƙar mace. Tabbas babu ƙarya sun sha wahala sosai, sun kuma jigata gaba ɗayansu.
"Alhamdulillah!" Mommah ta faɗa lokacin da ta jiyo kukan jinjiri daga cikin ɗakin. Dukkansu suka juyo suna kallanta. Ta jinjina kai lokacin da ƙwallar farin ciki ta taru a cikin idanunta.
"Tabbas wata ta haihu a cikinsu.." Mommah ta faɗa murmushin ya ƙi barin fuskarta. Se dai kafin ma ta sake cewa komai ko wani yace komai kukan wani jaririn da be kai wancan ba ya sake karaɗe wajen. A karo na biyu ta sake faɗin
"Alhamdulillah! Alhamdulillah.." Ta faɗa idanunta a lumshe. Dukansu kuma se hankalinsu ya koma kan ɗakin. Babu daɗewa midwives guda biyu suka fito daga cikin ɗakin kowaccensu ɗauke da Baby ɗaya lulluɓe cikin fararen tausasan towel, wanda suke cikin kayan da Ummeey ta taho da su, dan tashin hankali ya hana su ɗaukar komai na haihuwar. Gaba ɗayansu suka miƙe, har rige-rigen karɓar yaran ake yi. Areef ne ya yi nasarar saka hannu ya karɓesu su duka biyun, hannunsa har wani rawa yake yi. Cike da zumuɗin ganinsu ya ɗan yaye towel ɗin dan ya ga fuskarsu. Bacci ƙaramin ke yi hankalinsa kwance, yana sauke numfashi a hankali. Ɗayan kuma wanda shi ne babban idanunsa biyu yana ɗan wawurar bakinsa alamar abinci yake nema.
"Yawwah ko ke fa.." Daidai lokacin ta buɗe idanunta
"Wajen Lulu zan je.." Ta faɗa bayan ta ɗora idanunta a kan fuskarsa. Cike da mamaki yace
"Lulu kuma? Me ya faru?" Girgiza kai ta yi tana ƙoƙarin miƙewa tace
"Ni dai wajenta zan je.. Ina so in ganta." Da sauri ya miƙe, ya riƙota sosai yana sake tambayarta lafiya?
"Ba komai, so nake na ganta." Amsar da take ta ba shi kenan. Shi dai abun mamaki yake ba shi, se ka ce wadda za ta fara ganin Afaaf ɗin yau? Anya kuwa? Ko dai akwai wani abun da ya faru ne be sani ba? Ganin da ya yi ta ƙi ba shi haɗin kai ne ya sanya shi janta cikin jikinsa ya rungume. Ya ɗora hannunsa duka biyu a bayanta, cikin rarrashi yake faɗin
"Ki nutsu! Ki nutsu Uhmm?" Da sauri sauri numfashinta ke fita tamkar wadda ta yi tsere. Zuwa can kuma se ya koma fita daidai. Ya sauke numfashi daidai lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi.
"Wajen Lulu zan je." Ta sake faɗa tana kallansa.
"Iko sai Allah." Ya faɗa yana ƙura mata idanunsa.
"Shi kenan mu je na raka ki." Wata ajiyar zuciya ta sauke tana yin gaba. Ya bi ta da kallo. A kan laɓɓansa ya furta
"Rigima dai kawai." kafin ya girgiza kai yana murmushi lokaci ɗaya yana bin bayanta.
A ɗaya ɓangaren kuwa zaune take a kan kujerar, se dai kusan fiye da awa ɗaya kenan bayan wasu mintuna ta kan kama ƙugu ta riƙe tana runtse idanunta. Kwata-kwata ta kasa zama a kan kujerar. Ita kaɗai ta san azabar da take ji. Wani irin ciwo take ji kamar za ta mutu. Ciwon da yake zuwa bayan wasu mintuna. Se ta ɗauka ta dena ji se ta ji wanda ya fi na da. Daidai lokacin Gwani ya shigo cikin ɗakin. Ya kalle ta sosai yana nazarinta. Ƙarasawa ya yi ya zauna a kusa da ita.
"Me ya faru?" Ya tambaye ta a karo na babu adadi. Saboda tun jiya yake ganinta wani iri. Da zarar ya tambaye ta se tace babu komai. Girgiza kai ta yi kafin tace komai irin ciwon da take ji ya sake dawowa. Hannunsa da ke gefenta ta dafe da ƙarfi tana runtse idanunta. Girgiza kai take tana sauke wahalallen numfashi cikin wata irin azaba da take ji. Ƙanƙame hannun nata ya yi cike da tsoro yake kallanta. Bayan wajen minti 1 ta koma sauke ajiyar zuciya. Idanunta sun yi muzu-muzu, duk ta yi wani yaɓe-yaɓe.
"Ko dai haihuwar ce?" Ya tambaya yana kallanta. Girgiza kai ta yi ta kalle shi da lumsassun idanunta tace
"Ina ganin juyi ne kawai.." Ta faɗa da muryarta da ta shige ciki saboda wahala. Shi dai haka nan kawai ya ji be yi na'am da hakan ba, ya dai yi shiru yana cigaba da nazarinta. Kanta ya ja ya kwantar a kan kafaɗarsa. Duk da jinta take kamar ba a hayyacinta ba hakan be hana ta kwantawa ɗin ba ta yi shiru a ranta tana fatan Allah Ya sa kar ciwon ya dawo. Se dai addu'ar tata ba ta karɓu ba, dan kuwa ba a ɗauki lokaci me tsayi ba ciwon da ya fi na ɗazu ya taso mata. Yanzu kam ruƙunƙume shi ta yi kamar za ta ɓalla ƙirjinsa ta shige. Cikin galabaita muryarta na rawa take faɗin
"Wayyo Allah na.. zan mutu.. Wayyo Allah na.." Abin da take iya faɗa kawai kenan, cikin lokaci ƙanƙani hankalin Gwani ya tashi. Ai babu shiri ya janyo wayarsa ya danna kiran Mommah. Mommah da ke tare da Yaya Amina a lokacin ta ɗauki wayar.
"Mommah Afaaf ba lafiya." Shi ne abin da ya faɗa ko sallama be iya yi ba.
"Ya salaam! Kuna cikin gidan ne?" Mommah ta faɗa.
"Ehh.." Ba ta ce komai ba ta katse wayar. Ta kalli Yaya Amina tace
"Tashi maza mu je.. Afaaf ba lafiya, ina kuma tunanin haihuwar ce.."
"Toh subhanallahi! Mu je.." Yaya Amina ta miƙe ta soma yafa mayafinta da ke ajje. Tare suka fita da Mommah. Kai tsaye sashensu Gwanin suka wuce. Lulun na kwance kane-kane a jikin Gwanin, dan zuwa lokacin har ta soma fita daga hayyacinta. Ciwon ke dawo mata a kai a kai babu tsayawa. Yaya Amina ce ta ƙarasa ta kamo Lulun da taimakon Gwani. Suka fito palour riƙe da ita. Se a lokacin sannan Mommah ta ƙarasa ta karɓi Gwani. Se faman jerawa Lulun da duk wata alamar wahala ta gama bayyana a tattare da ita sannu suke. Lulun da a yanzu ko ganewa ba ta yi. Daidai lokacin da suka fito daga sashen Areef da Didi suka ƙaraso bakin sashen. Gaba ɗaya idanunsu suka ɗaga suka ɗora a kansu Mommahn. A kan er uwarta idanunta suka soma sauka. Ƙirjinta ya wani irin bugawa, a take jikinta ya soma ɓari, zazzaɓin da ya so rufe ta tun ɗazu yanzu ya samu damar soma rufeta. Cikin ƙanƙanin lokaci cikinta ya yi wani daƙiƙin juyawa. Ba ta damu da hakan ba, halin da ta ga er uwarta ciki ya sanya ta mantawa ma da abin da ke cikin nata. Ba ta san lokacin da ta fincike hannunta daga cikin na Areef ba. Cikin azama kamar babu komai a jikinta ta saka kai zuwa wajen Lulun da take hangowa riƙe a hannunsu Mommah da alama ba ta cikin hayyacinta. Se dai cikin rashin sa'a ba ta kula da abin da ke gabanta ba, ta yi tuntuɓe, kafin kace me ne wannan ta faɗi a wajen. Tsautsayi ya sa ta faɗi a kan cikinta. Wani azababben zafi da tun da Ammi ta haifeta ba ta taɓa jin irinsa ba ya ziyarceta. Dalili kenan da ya sanya ta kai hannu kan cikin nata tana sakin wata ƙara cikin matsanancin azaba.
"Baby..!!!" Ya faɗa cikin ɗaga murya yana kallanta lokacin da yake durƙushe a wajen. Mommah da Yaya Amina cikin matuƙar tashin hankali suke kallan abin da ke faruwa. Kusan a lokaci guda suke sauke salati. Ga Lulu a hannunsu wadda suke dab da shigar da ita cikin mota, ga shi babu damar su zo su taimakawa Didi. Da sauri Mommah tace
"Maza ɗauke ta ka saka a mota." Inaa, shi ba ji yake ba, gaba ɗaya a hankalinsa na kan Didi da ke hannunsa, wadda take a kwance kamar babu rai a tattare da ita.
"Areef!!" Gwani ya faɗa yana dafa kafaɗar Areef ɗin. Se a lokacin sannan ya iya ɗaga jajayen idanunsa ya kalli Gwani.
"Ɗauke ta ka saka a mota mu wuce asibiti." Kamar wanda ya farka daga bacci, se ya maida dubansa kan Didi. Cikin azama ya miƙe ya saɓe ta se cikin mota. Ko driving kasawa ya yi, se sakawa ya yi ɗaya daga cikin drivers ɗin gidan ya tuƙa su. Yana baya hannunsa ɗauke da Didi da zuwa lokacin ta farfaɗo se dai kwata kwata ya kasa fahimtar abin da ke damunta. Cikinta kawai ta riƙe tana kuka gami da sallallami. Shi dai ya san cikinta be isa haihuwa ba ballantana yace ko haihuwa ce. A'ah toh me ya samu cikin? Kar dai wani abun ne ya same shi? Ya tambayi kansa har lokacin idanunsa na kan Didi
A tare suka isa asibitin. Babu ɓata lokaci aka karɓe su. I zuwa lokacin gaba ɗaya sun yi laushi sun yi tuɓus. Duk wahala ta gama jigata su. A harabar haɗɗɗen asibitin duk suke zaune, waɗanda ke a tsaye suna tsaye. Dan zuwa lokacin har Ummeey ta iso. Abun da ya bawa kowa mamaki shi ne lokacin da aka sanar musu da cewa ita ma Didi haihuwar ce ta taso mata gadan-gadan.
"Haihuwa kuma?" Areef ya tambayi kansa bayan jin abin da aka faɗa ɗin.
"Ka kwantar da hankalinka, hakan ba abun damuwa ba ne, da ma hakan kan iya faruwa.. so ba sabon abu ba ne." Yaya Amina ta faɗa wa Areef bayan ta dafa kafaɗarsa. Shi dai jinta kawai ya yi. Hakan ne ya sa be ce komai ba se jinjina kai da ya yi. Cikin ƙanƙanin lokaci kowa ya duƙufa wajen addu'a tare da fatan Allah Ya sauke su lafiya. Bayan shuɗewar awanni masu yawa ana fafatawa, ana ta gwagwarmaya, cikin ikon Allah, se ya ba su sa'a Lulu ce ta soma haifo santalelen ɗa namiji ƙato da shi. Ko minti 2 ba a yi ba Didi ma ta dire nata ɗa namijin, se dai shi be kai girman na Lulu ba. Kowannensu kawai bajewa ta yi a kan gadon jiki a matuƙar mace. Tabbas babu ƙarya sun sha wahala sosai, sun kuma jigata gaba ɗayansu.
"Alhamdulillah!" Mommah ta faɗa lokacin da ta jiyo kukan jinjiri daga cikin ɗakin. Dukkansu suka juyo suna kallanta. Ta jinjina kai lokacin da ƙwallar farin ciki ta taru a cikin idanunta.
"Tabbas wata ta haihu a cikinsu.." Mommah ta faɗa murmushin ya ƙi barin fuskarta. Se dai kafin ma ta sake cewa komai ko wani yace komai kukan wani jaririn da be kai wancan ba ya sake karaɗe wajen. A karo na biyu ta sake faɗin
"Alhamdulillah! Alhamdulillah.." Ta faɗa idanunta a lumshe. Dukansu kuma se hankalinsu ya koma kan ɗakin. Babu daɗewa midwives guda biyu suka fito daga cikin ɗakin kowaccensu ɗauke da Baby ɗaya lulluɓe cikin fararen tausasan towel, wanda suke cikin kayan da Ummeey ta taho da su, dan tashin hankali ya hana su ɗaukar komai na haihuwar. Gaba ɗayansu suka miƙe, har rige-rigen karɓar yaran ake yi. Areef ne ya yi nasarar saka hannu ya karɓesu su duka biyun, hannunsa har wani rawa yake yi. Cike da zumuɗin ganinsu ya ɗan yaye towel ɗin dan ya ga fuskarsu. Bacci ƙaramin ke yi hankalinsa kwance, yana sauke numfashi a hankali. Ɗayan kuma wanda shi ne babban idanunsa biyu yana ɗan wawurar bakinsa alamar abinci yake nema.