Sashe 69
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yallaɓiya ki zo ki zauna koh?" Daddy ya faɗa yana kallan Mom. Se kawai hawaye suka shiga zarya a kan fuskar Mom. Kafin kowa ya lura da hakan ta yi amfani da hannunta wajen gogewa, sannan ta taka har wani tangaɗi take kamar er maye ta yi inda Aunt Makiyy ta zauna ita ma ta zauna. Ji take kamar tace ba za ta zauna ba, ko kuma akwai inda za ta je, se dai ta kasa yin hakan. Tunaninta gaba ɗaya ya tsaya cakk. So kawai take ta farka daga wannan mummunan mafarkin da take yi. Dan kuwa a wajenta da ganin Maimunatu gwara a ce wata masifar ce ta same su. Kan hannun wata side chair Bad Man ya ɗosana jikinsa, shi dai yau ya ga yanda Mom za ta yi da waɗannan mutanen. Idan kuma a gabansu za ta yi magana da Daddy se ya gani.
"Wai me ye haka ne?" Aunt Makiyy da ta kasa fahimtar yanayin da Mom ke ciki ta faɗa tana kallanta. Shiru kawai Mom ta yi gaba ɗaya hankalinta da idanunta na kan Maimunatu ne.
"Uhmm.. babu damuwa ki faɗa min me ke tafe da ku." Daddy ya faɗa yana kallan Maimuna kamar yanda aka sanar da shi ita ce ta zo wajensa. Se da ta saka hannu ta share fuskarta sannan tace
"A yi min afuwa Rankayadaɗe.. Amma zan so a ce Hajiya Sa'adah na cikin ɗakin nan zan sanar da komai." Jinjina kai Daddy ya yi, kafin daga bisani ya sauke ajiyar zuciya. Be ce komai ba ya ɗauki wayarsa ya yi waya ta tsawon mintina 2 sannan ya sauke. Shiru ya wanzu cikin palourn. Har Bad Man ya miƙe da niyyar ficewa Mommah ta yi sallama cikin ɗakin. Sanye cikin wani lace me shegen kyau, ɗinkin riga da skirt. Kamar ko da yaushe ta yi ɗaurin ture ka ga tsiya, ta kuma yafa mayafinta madaidaici. Ta mugun yin kyau, kamar wadda ke shirin zuwa gasar sarauniyar kyau. Da mamaki take kallan cikin ɗakin, musamman da ta ga baƙin fuska. Se dai kawai ta isa kan kujera ta nemi waje ta zauna bayan ta yi jam'u wajen gaida su.
"Bismillah.." Daddy ya sake bata umarni a karo na biyu. Se ta haɗiyi yawu sannan tace
"Ka yi min afuwa da duk abin da ze fito daga bakina.. Haƙiƙa na san ni me laifi ce.. Na kuma san ze yi wuya ka yafe min.. Amma duk da haka ba zan iya ƙasa a gwuiwa ba wajen faɗa muku gaskiyar al'amari." Shiru ɗakin ya ɗauka kowa da abin da yake tunani. Ita Mommah sam ba ta shaida fuskar Maimuna ba, hakan ne ya sanyata kallanta kawai. Ya yin da Aunt Makiyy ke taɓe fuska tana mamakin ko wace Maimunan? Dan ita ma ba ta shaida fuskar ba. Ta ɓangaren Mom kuwa babu irin tunzuratar da zuciya ba ta yi ba a kan ta tashi ta fatattaki Maimunan tun kafin ta kwance musu zani a kasuwa. Se dai kuma daga lokacin da ta yi hakan ta gama kashe kanta. Hakan ne ya sa ta yi shiru, ta jira jin abin da Maimunan za ta faɗa kafin ta ɗauki mataki, duk kuwa da yanda ilahirin jikinta ke wani irin rawa kamar me jin sanyi.
_SHEKARUN BAYA_
Alhaji Abubakar Matawalle ya kasance matashin me kuɗi tun a wancan lokacin. Matashin da ke ji da kyau, ilimi da kuma kuɗi. Hakan ne ya sa mata da yawa suka din ga kawo masa tayi a kan ko ze aure su. Se dai shi duk ba sa gabansa. Mace ɗaya ce a gabansa, wato Sa'adah (Mommah) wadda ya haɗu da ita gidan wani Abokinsa da ta kasance ƙanwar matarsa. Tun daga wannan lokaci ya ji duk duniya babu wadda yake so se ita. Nan take ya je wa da mahaifiyarsa zancen. Se dai abin da ta faɗa masa ne ya sanya ya ji duk wani ƙwarin gwuiwarsa ya kau. Wato sanar da shi da ta yi tana so ya auri er ƙawarta Salma (Mom). Gyara zama ya yi kansa a ƙasa yace
"Ki yi haƙuri Hajiya.. Tun da na ga yarinyar nan wallahi na ji ina ƙaunarta. Ban san yanda zan ji ba idan kika ce min ba zan aureta ba." Girgiza kai Hajiya ta yi tace
"A'ah fa Abubakar.. Ni ba zan hanaka auren wadda kake so ba, matuƙar dai za ka haɗa da Salma. Saboda wannan ɗin alƙawari ne na ɗaukarwa mahaifiyarta, kuma ina son cika shi.
Se dai ka sani ba na goyon bayan rashin adalci. Idan har ka san ba za ka yi adalci ba, ka sanar da ni in san abin yi." Hajiya uwa ce a wajensa, wadda ta amsa sunan uwa har ma da mahaifi. Ba ya jin akwai wani abu da za ta saka shi kuma ya ƙi yi. Musamman a kan wannan abun da tace ta yi alƙawari. Idan har be karɓa ba kenan se tace ta fasa saboda ɗan nata ya ƙi amincewa? Ya girgiza kai yana faɗin
"Na amince Hajiya.. In Sha Allah kuma ba za ki same ni da rashin adalci ba." Murmushi Hajiya ta yi tana faɗin
"Toh Allah ya yi maka albarka."
"Ameen." Ya amsa da hakan yana miƙewa. Daga nan Hajiya da kanta ta je ta samu ƙanin mahaifinsa da maganar. Babu ɓata lokaci aka je aka yi magana a ko ina. Be samu tsaiko wajen Mommah ba, dan kuwa ita ma ta yaba da hankalinsa. Hakan ne ya sa suka soma zuba soyayyarsu babu kama hannun yaro. Ta ɓangaren Mom ma hakan take, dan kuwa ita tuntuni tana ƙaunar shi da ma. Shi ɗin ne dai a hankali yake ƙoƙarin ganin ya koyawa kansa. Kowaccensu ta san da zaman ɗaya. Haka kuma be ɓoyewa kowa gaskiyar al'amari ba. Duk da Mommah ta ji babu daɗi amma haka ta daure ta haƙura musamman saboda tana son shi. Ya yin da ta ɓangaren Mom kuwa hauka ne kawai ba ta yi ba lokacin da ta ji wai idan an tashi aurensu ba ita kaɗai ze aura ba. Da tausasawar mahaifiyarta ta samu ta haƙura ta dena ɗaga hankali. Se dai gefe guda kuma tuni ta soma shiryawa yanda zamanta da Mommahn ze kasance. A haka dai har aka ɗaura aure. Mom ita ce uwar gida ya yin da Mommah ta kasance Amarya. Hakan ba ƙaramin bawa Mom damar zuba rashin kirkinta ya yi ba. Ita a nata ganin ai ita ce uwar gida. Tun a satin farko Mommah ta soma fahimtar wace ce Mom. Hakan ne ya sanyata kama kanta. Ta fito mata a ainahin Sa'adahnta. Ita kam Mom babu abin da ke damunta irin kyawun Sa'adahn. Wadda wani lokacin take mata kama da en india. Ga wata shegiyar izza kamar er gidan sarauta. Ke idan ta yi shiga, ta saka kaya haɗaɗɗu tana takun nan nata ba Daddy kaɗai ba, ita kanta Mom ɗin ji take kamar kar ta dena kallanta. Hakan ba ƙaramin sosa mata rai yake yi ba, daurewa kawai take yi. Ta rasa wane irin abu ne wannan, wace irin yarinya ce Sa'adahn. Me za ta mata ta bar mata Alhaji Matawalle ita ɗaya? Da dai ta ga duk wannan ba mafita ba ce, se kawai ita ma ta shiga kamanta shiga irinta Mommahn ko za ta samu ta din ga fitowa kamar Mommahn. Se dai sam sam zaren ba kalar yadin ba ne.
Sam sam Daddy ba ya nuna banbanci tsakanin Mommahn da kuma Mom. Komai ze musu babu bambanci, haka zalika yana ƙoƙarin kwatanta adalci a komai musamman yanda cikin zuciyarsa yafi son Mommah. Se dai ba ya taɓa nuna hakan, ko dan ka da hakan ya janyo matsala a tsakaninsu. Duk da hakan ba ya isar Mom, se ta nemi wata hanyar da za ta takali Mommah faɗa da ita. Ita kam Mommah sam ba ta biye mata. Wanda hakan ba ƙaramin sake ingiza Mom yake ba. Gaba ɗaya burinta be wuce a ce Sa'adah kar ta haihu da Alhaji Matawalle ba. Ta fi so koma mene ne ita ta yi ta haihuwa da shi ya yin da Sa'adah za ta mutu a juya ba tare da ta ajje komai cikin gidan ba. Cikin wannan tsukun ne kuwa ta soma wani zazzaɓi me naci, da kasala. Da yake Daddy ba ya wasa da zuwa asibiti, ya sa kai tsaye asibiti ya ɗauketa ya kaita aka dubata. Binciken farko aka tabbatar da Mom ɗin na ɗauke da juna biyu. Farin ciki kamar ze kashe Mom dan daɗi. Ko babu komai alamar cikar burinta ya bayyana. Da alama dai Sa'adahn juya ce kamar yanda take fatan hakan a ranta kullum ko ta samu dama ta farko da za ta samu ta soma muzguna mata. Ta saki wani murmushi lokacin da Daddy ya yi parking motarsa cikin harabar gidan. Cikin ranta tana tsara irin rashin kirkin da za ta soma zubawa tun daga yau ɗin..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO62*
___Tun da ta hango Mommah ta fito daga sashenta, se ta tsiri wani yamutse fuska tana riƙe ƙugu, irin yanda wasu masu tsohon ciki suke yi. Kamar za ta wuce ba tare da ta nuna ta gansu ba, se kuma ta ga rashin dacewar hakan. Tun da ko babu komai tare suke da Daddy. Hakan ne ya sanyata juyawa ta ƙarasa inda suke tana faɗin
"Sannu da zuwa.."
"Yawwah sannu ka dai." Daddy ya faɗa da murmushi kan fuskarsa. Lura da hakan da Mom ta yi ne ya sanyata tamke fuska, ta faki idanunsu Dad ta saka ƙafa tana sane ta bigi wani ƙaramin gini da ke ƙasa a gefenta. Se kuwa ta saka ƙara tana yin baya kamar za ta faɗi, cike da fatan Daddy ya lura da ita ya riƙota. Cikin sa'a kuwa ya lura da itan, se ya yi saurin riƙota yana faɗin
"Subhanallahi.." Se da ta koma ta tsaya a kan ƙafafunta sannan tace tana sake yamutsa fuska
"Wai me ye haka ne?" Aunt Makiyy da ta kasa fahimtar yanayin da Mom ke ciki ta faɗa tana kallanta. Shiru kawai Mom ta yi gaba ɗaya hankalinta da idanunta na kan Maimunatu ne.
"Uhmm.. babu damuwa ki faɗa min me ke tafe da ku." Daddy ya faɗa yana kallan Maimuna kamar yanda aka sanar da shi ita ce ta zo wajensa. Se da ta saka hannu ta share fuskarta sannan tace
"A yi min afuwa Rankayadaɗe.. Amma zan so a ce Hajiya Sa'adah na cikin ɗakin nan zan sanar da komai." Jinjina kai Daddy ya yi, kafin daga bisani ya sauke ajiyar zuciya. Be ce komai ba ya ɗauki wayarsa ya yi waya ta tsawon mintina 2 sannan ya sauke. Shiru ya wanzu cikin palourn. Har Bad Man ya miƙe da niyyar ficewa Mommah ta yi sallama cikin ɗakin. Sanye cikin wani lace me shegen kyau, ɗinkin riga da skirt. Kamar ko da yaushe ta yi ɗaurin ture ka ga tsiya, ta kuma yafa mayafinta madaidaici. Ta mugun yin kyau, kamar wadda ke shirin zuwa gasar sarauniyar kyau. Da mamaki take kallan cikin ɗakin, musamman da ta ga baƙin fuska. Se dai kawai ta isa kan kujera ta nemi waje ta zauna bayan ta yi jam'u wajen gaida su.
"Bismillah.." Daddy ya sake bata umarni a karo na biyu. Se ta haɗiyi yawu sannan tace
"Ka yi min afuwa da duk abin da ze fito daga bakina.. Haƙiƙa na san ni me laifi ce.. Na kuma san ze yi wuya ka yafe min.. Amma duk da haka ba zan iya ƙasa a gwuiwa ba wajen faɗa muku gaskiyar al'amari." Shiru ɗakin ya ɗauka kowa da abin da yake tunani. Ita Mommah sam ba ta shaida fuskar Maimuna ba, hakan ne ya sanyata kallanta kawai. Ya yin da Aunt Makiyy ke taɓe fuska tana mamakin ko wace Maimunan? Dan ita ma ba ta shaida fuskar ba. Ta ɓangaren Mom kuwa babu irin tunzuratar da zuciya ba ta yi ba a kan ta tashi ta fatattaki Maimunan tun kafin ta kwance musu zani a kasuwa. Se dai kuma daga lokacin da ta yi hakan ta gama kashe kanta. Hakan ne ya sa ta yi shiru, ta jira jin abin da Maimunan za ta faɗa kafin ta ɗauki mataki, duk kuwa da yanda ilahirin jikinta ke wani irin rawa kamar me jin sanyi.
_SHEKARUN BAYA_
Alhaji Abubakar Matawalle ya kasance matashin me kuɗi tun a wancan lokacin. Matashin da ke ji da kyau, ilimi da kuma kuɗi. Hakan ne ya sa mata da yawa suka din ga kawo masa tayi a kan ko ze aure su. Se dai shi duk ba sa gabansa. Mace ɗaya ce a gabansa, wato Sa'adah (Mommah) wadda ya haɗu da ita gidan wani Abokinsa da ta kasance ƙanwar matarsa. Tun daga wannan lokaci ya ji duk duniya babu wadda yake so se ita. Nan take ya je wa da mahaifiyarsa zancen. Se dai abin da ta faɗa masa ne ya sanya ya ji duk wani ƙwarin gwuiwarsa ya kau. Wato sanar da shi da ta yi tana so ya auri er ƙawarta Salma (Mom). Gyara zama ya yi kansa a ƙasa yace
"Ki yi haƙuri Hajiya.. Tun da na ga yarinyar nan wallahi na ji ina ƙaunarta. Ban san yanda zan ji ba idan kika ce min ba zan aureta ba." Girgiza kai Hajiya ta yi tace
"A'ah fa Abubakar.. Ni ba zan hanaka auren wadda kake so ba, matuƙar dai za ka haɗa da Salma. Saboda wannan ɗin alƙawari ne na ɗaukarwa mahaifiyarta, kuma ina son cika shi.
Se dai ka sani ba na goyon bayan rashin adalci. Idan har ka san ba za ka yi adalci ba, ka sanar da ni in san abin yi." Hajiya uwa ce a wajensa, wadda ta amsa sunan uwa har ma da mahaifi. Ba ya jin akwai wani abu da za ta saka shi kuma ya ƙi yi. Musamman a kan wannan abun da tace ta yi alƙawari. Idan har be karɓa ba kenan se tace ta fasa saboda ɗan nata ya ƙi amincewa? Ya girgiza kai yana faɗin
"Na amince Hajiya.. In Sha Allah kuma ba za ki same ni da rashin adalci ba." Murmushi Hajiya ta yi tana faɗin
"Toh Allah ya yi maka albarka."
"Ameen." Ya amsa da hakan yana miƙewa. Daga nan Hajiya da kanta ta je ta samu ƙanin mahaifinsa da maganar. Babu ɓata lokaci aka je aka yi magana a ko ina. Be samu tsaiko wajen Mommah ba, dan kuwa ita ma ta yaba da hankalinsa. Hakan ne ya sa suka soma zuba soyayyarsu babu kama hannun yaro. Ta ɓangaren Mom ma hakan take, dan kuwa ita tuntuni tana ƙaunar shi da ma. Shi ɗin ne dai a hankali yake ƙoƙarin ganin ya koyawa kansa. Kowaccensu ta san da zaman ɗaya. Haka kuma be ɓoyewa kowa gaskiyar al'amari ba. Duk da Mommah ta ji babu daɗi amma haka ta daure ta haƙura musamman saboda tana son shi. Ya yin da ta ɓangaren Mom kuwa hauka ne kawai ba ta yi ba lokacin da ta ji wai idan an tashi aurensu ba ita kaɗai ze aura ba. Da tausasawar mahaifiyarta ta samu ta haƙura ta dena ɗaga hankali. Se dai gefe guda kuma tuni ta soma shiryawa yanda zamanta da Mommahn ze kasance. A haka dai har aka ɗaura aure. Mom ita ce uwar gida ya yin da Mommah ta kasance Amarya. Hakan ba ƙaramin bawa Mom damar zuba rashin kirkinta ya yi ba. Ita a nata ganin ai ita ce uwar gida. Tun a satin farko Mommah ta soma fahimtar wace ce Mom. Hakan ne ya sanyata kama kanta. Ta fito mata a ainahin Sa'adahnta. Ita kam Mom babu abin da ke damunta irin kyawun Sa'adahn. Wadda wani lokacin take mata kama da en india. Ga wata shegiyar izza kamar er gidan sarauta. Ke idan ta yi shiga, ta saka kaya haɗaɗɗu tana takun nan nata ba Daddy kaɗai ba, ita kanta Mom ɗin ji take kamar kar ta dena kallanta. Hakan ba ƙaramin sosa mata rai yake yi ba, daurewa kawai take yi. Ta rasa wane irin abu ne wannan, wace irin yarinya ce Sa'adahn. Me za ta mata ta bar mata Alhaji Matawalle ita ɗaya? Da dai ta ga duk wannan ba mafita ba ce, se kawai ita ma ta shiga kamanta shiga irinta Mommahn ko za ta samu ta din ga fitowa kamar Mommahn. Se dai sam sam zaren ba kalar yadin ba ne.
Sam sam Daddy ba ya nuna banbanci tsakanin Mommahn da kuma Mom. Komai ze musu babu bambanci, haka zalika yana ƙoƙarin kwatanta adalci a komai musamman yanda cikin zuciyarsa yafi son Mommah. Se dai ba ya taɓa nuna hakan, ko dan ka da hakan ya janyo matsala a tsakaninsu. Duk da hakan ba ya isar Mom, se ta nemi wata hanyar da za ta takali Mommah faɗa da ita. Ita kam Mommah sam ba ta biye mata. Wanda hakan ba ƙaramin sake ingiza Mom yake ba. Gaba ɗaya burinta be wuce a ce Sa'adah kar ta haihu da Alhaji Matawalle ba. Ta fi so koma mene ne ita ta yi ta haihuwa da shi ya yin da Sa'adah za ta mutu a juya ba tare da ta ajje komai cikin gidan ba. Cikin wannan tsukun ne kuwa ta soma wani zazzaɓi me naci, da kasala. Da yake Daddy ba ya wasa da zuwa asibiti, ya sa kai tsaye asibiti ya ɗauketa ya kaita aka dubata. Binciken farko aka tabbatar da Mom ɗin na ɗauke da juna biyu. Farin ciki kamar ze kashe Mom dan daɗi. Ko babu komai alamar cikar burinta ya bayyana. Da alama dai Sa'adahn juya ce kamar yanda take fatan hakan a ranta kullum ko ta samu dama ta farko da za ta samu ta soma muzguna mata. Ta saki wani murmushi lokacin da Daddy ya yi parking motarsa cikin harabar gidan. Cikin ranta tana tsara irin rashin kirkin da za ta soma zubawa tun daga yau ɗin..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO62*
___Tun da ta hango Mommah ta fito daga sashenta, se ta tsiri wani yamutse fuska tana riƙe ƙugu, irin yanda wasu masu tsohon ciki suke yi. Kamar za ta wuce ba tare da ta nuna ta gansu ba, se kuma ta ga rashin dacewar hakan. Tun da ko babu komai tare suke da Daddy. Hakan ne ya sanyata juyawa ta ƙarasa inda suke tana faɗin
"Sannu da zuwa.."
"Yawwah sannu ka dai." Daddy ya faɗa da murmushi kan fuskarsa. Lura da hakan da Mom ta yi ne ya sanyata tamke fuska, ta faki idanunsu Dad ta saka ƙafa tana sane ta bigi wani ƙaramin gini da ke ƙasa a gefenta. Se kuwa ta saka ƙara tana yin baya kamar za ta faɗi, cike da fatan Daddy ya lura da ita ya riƙota. Cikin sa'a kuwa ya lura da itan, se ya yi saurin riƙota yana faɗin
"Subhanallahi.." Se da ta koma ta tsaya a kan ƙafafunta sannan tace tana sake yamutsa fuska