Sashe 122
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shi kenan.. Amma fa kar na zo a ce min ba ka ci ba, zamu ɓata."
"Ehh, na yadda." Aryan ya faɗa yana buga tsalle kamar wani babba. Tilas Lulu ta yi dariya. Shi ma Gwani dariyar ya yi yana sakinsa ya tafi. Dab da ze fita Lulu ta jawo shi ta sumbaci goshinsa kafin ta ɗaga masa hannu. Shi ma sumbatarta ya yi a hannunta kana ya fice daga ɗakin a guje. Sauke ajiyar zuciya ta yi tana miƙewa dan ita ma ta samu ta shirya. Gwani ya saka hannu ya maidota ta koma inda take.
"Maza ba ni sumba ɗaya.." Ya faɗa yana juya mata gefen kumatunsa. Ta kalli gefe da gefe kamar me neman wani abu, maimakon ya ji saukar bakin nata a kan kumatunsa se jin saukar shi ya yi a kan laɓɓansa. Ya buɗe ido yana kallanta, ta kanne masa ido ɗaya tana soma kissing lips ɗin nasa. Hannu ya saka ya ɗan jawo ƙugunta, hakan ya sa suka sake samun kusanci sosai. Ya lumshe idanunsa shi ma ya shiga kissing ɗin nata. Ai se ta yi nadama, dan kuwa se ga Gwani na neman zarmewa. Fahimtar hakan ya sanya ta faɗin
"Habibi!!" Ta faɗa da muryarta da ta ɗan sauya. Kansa ya ɗora a kan wuyanta yace yana kallanta.
"Tun da an sallami Aryan ya kamata a sallami babansa." Turo baki ta yi kafin tace
"Habibi.." Ta ƙare a marairaice. Murmushi ya yi be ce komai ba, haka ita ma kafin ta sake cewa komai ya ɗauke ta gaba ɗaya se toilet. Bayan wasu mintuna suka fito, tare suka shirya. Shi ya shiryata ya yin da ita ma ta shirya shi. Cikin ƙanƙanin lokaci suka fito suka yi wani shahararren kyau. Shi cikin manyan kaya ya yin da Lulu ke cikin wani ɗinkin lace da ya gama fita a cikin fitattu.
A ɗaya ɓangaren kuwa da gudu Aryan ya ƙarasa shiga ɗakin. Duk suna zaune a palour. Didi ta cake ita ma cikin lace da mayafinsa, ɗaurin nan ya zauna ya yi mata mugun kyau. Ita kanta ta sake yin kyau, ta murje ta kuma yi ƙiba daidai misali.
"Maama." Aryan ya faɗa bayan ya shigo cikin ɗakin.
"Oyoyo my boy." Didi ta faɗa tana buɗe masa hannayenta. Babu musu ya faɗa ciki, ta rufe gam.
"Maama ni fa?" Ayaan ya faɗa yana turo baki. Dariya ta yi kafin tace
"Toh shi kenan, zo nan.." Ta faɗa tana buɗe hannun. Se kuwa ya ƙarasa ta haɗa su ta rungume. Baya ta matsar da su tana kallansu su duka yanda suka yi kyau sosai ya sanyata faɗin
"Allah Ya raya min ku." Ta faɗa ƙaunarsu da ba ta iya bambance su na sake mamaye zuciyarta.
"Na riga ka shiryawa." Ayaan ya faɗa yana yi wa Aryan gwalo.
"Maama kin gan shi koh?" Aryan ya faɗa yana kallan Didi. Girgiza kai Didi ta yi kafin tace
"A'ah Ayaan ba na son tsokana.. Ba ka ga tare kuka shirya ba?" Se da ya tura bakinsa kafin ya ɗaga kai kawai, dan shi dai so ya yi ya riga Aryan ɗin shiryawa. Gwalo Aryan ya yi masa jin da ya yi Maman ta bi bayansa. Daidai lokacin Areef ya shigo cikin ɗakin. Abun mamaki shi kansa cikin manyan kaya yake, abin da ya ba ni mamaki kenan. Rashin saba ganinsa da kayan da na yi ya sanya yau ɗin ya fita wani na daban, ya yi daƙiƙin kyau kamar ba shi ba. Ya zama wani babban mutum. Yau ɗin se ya yi yanayi da Gwani, kamar Gwani ne ya sauya kama.
"Dad.." Suka haɗa baki wajen faɗa suna tafiya da gudu wajensa. Ɗaukarsu ya yi gaba ɗaya kafin ya sauke su yana faɗin
"Na'am yaran Dad.." Ya saka hannu ya lakuce kumatun kowannensu.
"Bari na chanki wanda ya fi kyau.." Ya faɗa yana kallan nasu. Tsalle suka fara gaba ɗayansu, kowanne jira yake a ce ya fi kyau.
"Dukkanku kun yi kyau sosai." Ya ƙare yana kambaba kalmar ƙarshe.
"Yeehhh!!" Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.
"Let's go.." Ya faɗa yana kama hannun yaran se dai idanunsa na kan Didi da ita ma take kallansa saboda yadda ya mata kyau sosai yau ɗin nan. Miƙewa Didi ta yi tana gyara zaman mayafin jikinta. Sakin hannun Aryan da Ayaan Areef ya yi yace
"Ku wuce mu je.." Babu musu suka fita da sauri.
"Madam." Areef ya faɗa bayan ya riƙo hannun Didi. Tuni har Aryan da Ayaan sun fice daga ɗakin. Ta juyo da niyyar jin abin da ya sa ya kirata ɗin, se kawai jin bakinsa ta yi a kan nata. Ya rungumeta sosai ya shiga bata zazzafan sumbata. Duk da ba ta shirya ba, amma hakan be hana ta sakin jiki itama tana kissing ɗin nasa ba. Wajen minti 1 duka ɗauka a haka, kafin ta zare bakinta daga cikin nasa bayan ya bata dama.
"Wannan lipgloss ɗin da kika saka shi ya tsone min ido." Ya ƙare yana shafa sumar kansa.
"Ai dai ga shi yanzu babu shi.."
"Ƙwarai kuwa, shi ya sa na lashe abuna tass kar ma wani ya kalla." Ya faɗa yana kallanta ɗauke da murmushi a kan fuskarsa. Ita ma murmushin ta yi kafin tace
"Shi kenan koh Babe?" Jinjina kai ya yi kafin ya kai hannunsa ya riƙo nata hannun, daga haka suka fice daga cikin ɗakin. Daidai lokacin da suka fito su ma su Gwani suka fito. Kai da na gansu a tare duk se na rasa gane waɗanne ma'aurata ne suka fi kyau. Dan kowannensu kyau ne iya kyau, haɗuwa iya haɗuwa, dacewa iya dacewa. Hakan ne ya sa duk suka fito suka yi kyau abinsu. Da gudu Aryan da Ayaan suka tafi wajensu Gwani. Kusan a tare suka tsuguna suka rungume yaran.
"Mami ai na fi Aryan kyau koh?" Ayaan ya faɗa yana kwantar da rigar jikinsa kamar wani me yin guga. Dariya ta yi kafin tace komai Aryan yace
"Abbu ai na fi Ayaan kyau koh?"
"Dukka kun yi kyau kamar wasu Actors." Dariya duka suka saka suna jin daɗin yadda Abbun ya yabe su. Hannun Gwani duk suka kama lokacin da suka fara takawa.
"Kai da yaran naka ne?" Areef ya faɗa yana kallan Gwani. Jinjina kai Gwani ya yi yace
"Ai fa.. So ake a ƙure kowa yau." Dariya duka suka saka suna maida dubansu kan Aryan da Ayaan da ke ta wasansu duk da hannunsu har lokacin na cikin na Gwani ne.
"Mu wuce koh?" Gwani ya faɗa. Babu ɓata lokaci suka soma takawa dan isa inda motar take. Se a lokacin Didi da Lulu suka haɗe waje ɗaya. Sosai suka fito suka zama manyan mata. Kana ganinsu ka san kwanciyar hankali ya zauna musu.
"Wai na ga ki na yin ƙiba Didi.. Ko dai ko dai?"
"Ko dai me?" Didi ta faɗa tana buɗe ido.
"Aryan da Ayaan sun kusa samun ƙani mana." Lulu ta faɗa cikin basarwa. Duka Didi ta kai mata kafin tace
"Lulu haka kika zama koh? Ke ban ce ta wajenki muka kusa zama iyaye a karo na biyu ba se ni koh?"
"Ni ba ni da komai." Lulu ta faɗa tana tura bakinta.
"Kya dai ji da shi, ni fa gani ma na yi kamar har cikin naki ya soma fitowa." Didi ta faɗa cikin basarwa.
"Kin ji Didi daga magana kina neman ki juya abun kaina.. toh wallahi na janye da wasa nake.." Dariya Didi ta saka a fili tace
"Aou har kin janye?" Ita ma Lulun dariya ta yi tana faɗin
"Wallahi na janye, ai ban manta wahalar nan ba." Ta ƙare maganar ita ma tana dariya.
"Toh Allah Ya bamu masu albarka." Didi ta faɗa a hankali.
"Ameen Didi."
Haka suka ɗunguma cikin motar, Areef na driving ya yin da Didi ke gefensa. Gwani da Lulu na baya, Aryan da Ayaan na ta dabdalarsu a bayan su ma. Suna tafe suna hira gwanin ban sha'awa, cike da sabo, ƙauna da kuma farin ciki. A haka suka cigaba da tafiya se gidan Alhaji Matawalle..
Haka rayuwarsu ta cigaba da kasancewa a kodayaushe se dai a ce Alhamdulillah..
GAME OVER!!! 🔥
ALHAMDULILLAH!
ALHAMDULILLAH!!
ALHAMDULILLAH!!!
Da sukuwa da zamiya, a nan na kawo ƙarshen wannan littafi nawa me suna *A JINI TAKE (IZZATA)* Ina me roƙon Allah ya ba mu damar ɗaukar abubuwa masu kyau cikin labarin, sannan mu watsar da akasin su. Abin da na rubuta daidai Allah Ya haɗa mu a ladan, abin da na yi ba daidai ba kuma Allah Ka yafe min.
Ina neman afuwar duk wanda na ɓatawa rai tun fara littafin nan har zuwa ƙarshensa. Ina kuma me matuƙar godiya a gare ku en amana. Your willingness to join me on this journey and trust me with your time and emotions means so much to me. Thank you for reading and caring. Allah Ya bar zumunci.
A JINI TAKE (IZZATA) comment section, and A JINI TAKE PAID GROUP, ina gaishe ku cikin buhu. Allah Ya ƙara mana haƙuri da juna, Ya kuma bar mana zumunci har abada. Kamar yadda na saba kodayaushe yau ma In Sha Allah gaisuwa ta musamman za ta je ne zuwa ga en amanata na Paid group
1. A'isha Sabo
2. Khulsum
3. A'ishahumairaazare
4. A'ishatu Muhammad
5. Amina
6. Auterr Mamy
7. Azizaty
8. Jidda Galadima
9. Maman Faruk
10. Maman Ikram
11. Mrs Hypan
12. Ummi Ja'afar
13. Zainab Umar Aliyu
14. Khadija Abubakar Oum Ashraf
15. Zainab Abubakar Yakubu
16. MAMAN IKRAM
17. Mrs Majeed
18. Ummu Hussain
19. Shafa'atu Adam Sa'id
20. Rabi'atu Buhari Walida
21. Ruƙayya Rabi'u
22. Fatima Isma'il
23. A'isha Nasir
24. Hajiya
25. Humaira Bashir
26. Ruƙayya Yahuza
27. 🌸🌸5113
28. Fatima
29. Yahanasuisma'il
30. Shafa'atu Bello
31. Ruƙayya UST
32. Zulhikmarh
33. Fatima Bashir 😩😍
34. Ummulkhaer Yusuf 😩😍
Oppps na gaji 😩 Da sauran mutanen dai, duk ina gaishe da ku. Se dai fa ta waɗannan tafi girma, saboda kasancewarsu jajirtattu wajen yin sharhi da zarar Update ya sauka. Love yhu 😘❤️ Allah Ya bar zumunci.
Domin son magana da ni kai tsaye, sharhi ko ƙarin haske za a iya tuntuɓata ta 08124818273.
SUBHANAKALLAHUMMA, WA BI HAMDIKA, ASHHADU AN LA ILA HA ILLA ANTA, ASTAGFIRUKA, WA A TUBU ILAIKA.
"Ehh, na yadda." Aryan ya faɗa yana buga tsalle kamar wani babba. Tilas Lulu ta yi dariya. Shi ma Gwani dariyar ya yi yana sakinsa ya tafi. Dab da ze fita Lulu ta jawo shi ta sumbaci goshinsa kafin ta ɗaga masa hannu. Shi ma sumbatarta ya yi a hannunta kana ya fice daga ɗakin a guje. Sauke ajiyar zuciya ta yi tana miƙewa dan ita ma ta samu ta shirya. Gwani ya saka hannu ya maidota ta koma inda take.
"Maza ba ni sumba ɗaya.." Ya faɗa yana juya mata gefen kumatunsa. Ta kalli gefe da gefe kamar me neman wani abu, maimakon ya ji saukar bakin nata a kan kumatunsa se jin saukar shi ya yi a kan laɓɓansa. Ya buɗe ido yana kallanta, ta kanne masa ido ɗaya tana soma kissing lips ɗin nasa. Hannu ya saka ya ɗan jawo ƙugunta, hakan ya sa suka sake samun kusanci sosai. Ya lumshe idanunsa shi ma ya shiga kissing ɗin nata. Ai se ta yi nadama, dan kuwa se ga Gwani na neman zarmewa. Fahimtar hakan ya sanya ta faɗin
"Habibi!!" Ta faɗa da muryarta da ta ɗan sauya. Kansa ya ɗora a kan wuyanta yace yana kallanta.
"Tun da an sallami Aryan ya kamata a sallami babansa." Turo baki ta yi kafin tace
"Habibi.." Ta ƙare a marairaice. Murmushi ya yi be ce komai ba, haka ita ma kafin ta sake cewa komai ya ɗauke ta gaba ɗaya se toilet. Bayan wasu mintuna suka fito, tare suka shirya. Shi ya shiryata ya yin da ita ma ta shirya shi. Cikin ƙanƙanin lokaci suka fito suka yi wani shahararren kyau. Shi cikin manyan kaya ya yin da Lulu ke cikin wani ɗinkin lace da ya gama fita a cikin fitattu.
A ɗaya ɓangaren kuwa da gudu Aryan ya ƙarasa shiga ɗakin. Duk suna zaune a palour. Didi ta cake ita ma cikin lace da mayafinsa, ɗaurin nan ya zauna ya yi mata mugun kyau. Ita kanta ta sake yin kyau, ta murje ta kuma yi ƙiba daidai misali.
"Maama." Aryan ya faɗa bayan ya shigo cikin ɗakin.
"Oyoyo my boy." Didi ta faɗa tana buɗe masa hannayenta. Babu musu ya faɗa ciki, ta rufe gam.
"Maama ni fa?" Ayaan ya faɗa yana turo baki. Dariya ta yi kafin tace
"Toh shi kenan, zo nan.." Ta faɗa tana buɗe hannun. Se kuwa ya ƙarasa ta haɗa su ta rungume. Baya ta matsar da su tana kallansu su duka yanda suka yi kyau sosai ya sanyata faɗin
"Allah Ya raya min ku." Ta faɗa ƙaunarsu da ba ta iya bambance su na sake mamaye zuciyarta.
"Na riga ka shiryawa." Ayaan ya faɗa yana yi wa Aryan gwalo.
"Maama kin gan shi koh?" Aryan ya faɗa yana kallan Didi. Girgiza kai Didi ta yi kafin tace
"A'ah Ayaan ba na son tsokana.. Ba ka ga tare kuka shirya ba?" Se da ya tura bakinsa kafin ya ɗaga kai kawai, dan shi dai so ya yi ya riga Aryan ɗin shiryawa. Gwalo Aryan ya yi masa jin da ya yi Maman ta bi bayansa. Daidai lokacin Areef ya shigo cikin ɗakin. Abun mamaki shi kansa cikin manyan kaya yake, abin da ya ba ni mamaki kenan. Rashin saba ganinsa da kayan da na yi ya sanya yau ɗin ya fita wani na daban, ya yi daƙiƙin kyau kamar ba shi ba. Ya zama wani babban mutum. Yau ɗin se ya yi yanayi da Gwani, kamar Gwani ne ya sauya kama.
"Dad.." Suka haɗa baki wajen faɗa suna tafiya da gudu wajensa. Ɗaukarsu ya yi gaba ɗaya kafin ya sauke su yana faɗin
"Na'am yaran Dad.." Ya saka hannu ya lakuce kumatun kowannensu.
"Bari na chanki wanda ya fi kyau.." Ya faɗa yana kallan nasu. Tsalle suka fara gaba ɗayansu, kowanne jira yake a ce ya fi kyau.
"Dukkanku kun yi kyau sosai." Ya ƙare yana kambaba kalmar ƙarshe.
"Yeehhh!!" Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.
"Let's go.." Ya faɗa yana kama hannun yaran se dai idanunsa na kan Didi da ita ma take kallansa saboda yadda ya mata kyau sosai yau ɗin nan. Miƙewa Didi ta yi tana gyara zaman mayafin jikinta. Sakin hannun Aryan da Ayaan Areef ya yi yace
"Ku wuce mu je.." Babu musu suka fita da sauri.
"Madam." Areef ya faɗa bayan ya riƙo hannun Didi. Tuni har Aryan da Ayaan sun fice daga ɗakin. Ta juyo da niyyar jin abin da ya sa ya kirata ɗin, se kawai jin bakinsa ta yi a kan nata. Ya rungumeta sosai ya shiga bata zazzafan sumbata. Duk da ba ta shirya ba, amma hakan be hana ta sakin jiki itama tana kissing ɗin nasa ba. Wajen minti 1 duka ɗauka a haka, kafin ta zare bakinta daga cikin nasa bayan ya bata dama.
"Wannan lipgloss ɗin da kika saka shi ya tsone min ido." Ya ƙare yana shafa sumar kansa.
"Ai dai ga shi yanzu babu shi.."
"Ƙwarai kuwa, shi ya sa na lashe abuna tass kar ma wani ya kalla." Ya faɗa yana kallanta ɗauke da murmushi a kan fuskarsa. Ita ma murmushin ta yi kafin tace
"Shi kenan koh Babe?" Jinjina kai ya yi kafin ya kai hannunsa ya riƙo nata hannun, daga haka suka fice daga cikin ɗakin. Daidai lokacin da suka fito su ma su Gwani suka fito. Kai da na gansu a tare duk se na rasa gane waɗanne ma'aurata ne suka fi kyau. Dan kowannensu kyau ne iya kyau, haɗuwa iya haɗuwa, dacewa iya dacewa. Hakan ne ya sa duk suka fito suka yi kyau abinsu. Da gudu Aryan da Ayaan suka tafi wajensu Gwani. Kusan a tare suka tsuguna suka rungume yaran.
"Mami ai na fi Aryan kyau koh?" Ayaan ya faɗa yana kwantar da rigar jikinsa kamar wani me yin guga. Dariya ta yi kafin tace komai Aryan yace
"Abbu ai na fi Ayaan kyau koh?"
"Dukka kun yi kyau kamar wasu Actors." Dariya duka suka saka suna jin daɗin yadda Abbun ya yabe su. Hannun Gwani duk suka kama lokacin da suka fara takawa.
"Kai da yaran naka ne?" Areef ya faɗa yana kallan Gwani. Jinjina kai Gwani ya yi yace
"Ai fa.. So ake a ƙure kowa yau." Dariya duka suka saka suna maida dubansu kan Aryan da Ayaan da ke ta wasansu duk da hannunsu har lokacin na cikin na Gwani ne.
"Mu wuce koh?" Gwani ya faɗa. Babu ɓata lokaci suka soma takawa dan isa inda motar take. Se a lokacin Didi da Lulu suka haɗe waje ɗaya. Sosai suka fito suka zama manyan mata. Kana ganinsu ka san kwanciyar hankali ya zauna musu.
"Wai na ga ki na yin ƙiba Didi.. Ko dai ko dai?"
"Ko dai me?" Didi ta faɗa tana buɗe ido.
"Aryan da Ayaan sun kusa samun ƙani mana." Lulu ta faɗa cikin basarwa. Duka Didi ta kai mata kafin tace
"Lulu haka kika zama koh? Ke ban ce ta wajenki muka kusa zama iyaye a karo na biyu ba se ni koh?"
"Ni ba ni da komai." Lulu ta faɗa tana tura bakinta.
"Kya dai ji da shi, ni fa gani ma na yi kamar har cikin naki ya soma fitowa." Didi ta faɗa cikin basarwa.
"Kin ji Didi daga magana kina neman ki juya abun kaina.. toh wallahi na janye da wasa nake.." Dariya Didi ta saka a fili tace
"Aou har kin janye?" Ita ma Lulun dariya ta yi tana faɗin
"Wallahi na janye, ai ban manta wahalar nan ba." Ta ƙare maganar ita ma tana dariya.
"Toh Allah Ya bamu masu albarka." Didi ta faɗa a hankali.
"Ameen Didi."
Haka suka ɗunguma cikin motar, Areef na driving ya yin da Didi ke gefensa. Gwani da Lulu na baya, Aryan da Ayaan na ta dabdalarsu a bayan su ma. Suna tafe suna hira gwanin ban sha'awa, cike da sabo, ƙauna da kuma farin ciki. A haka suka cigaba da tafiya se gidan Alhaji Matawalle..
Haka rayuwarsu ta cigaba da kasancewa a kodayaushe se dai a ce Alhamdulillah..
GAME OVER!!! 🔥
ALHAMDULILLAH!
ALHAMDULILLAH!!
ALHAMDULILLAH!!!
Da sukuwa da zamiya, a nan na kawo ƙarshen wannan littafi nawa me suna *A JINI TAKE (IZZATA)* Ina me roƙon Allah ya ba mu damar ɗaukar abubuwa masu kyau cikin labarin, sannan mu watsar da akasin su. Abin da na rubuta daidai Allah Ya haɗa mu a ladan, abin da na yi ba daidai ba kuma Allah Ka yafe min.
Ina neman afuwar duk wanda na ɓatawa rai tun fara littafin nan har zuwa ƙarshensa. Ina kuma me matuƙar godiya a gare ku en amana. Your willingness to join me on this journey and trust me with your time and emotions means so much to me. Thank you for reading and caring. Allah Ya bar zumunci.
A JINI TAKE (IZZATA) comment section, and A JINI TAKE PAID GROUP, ina gaishe ku cikin buhu. Allah Ya ƙara mana haƙuri da juna, Ya kuma bar mana zumunci har abada. Kamar yadda na saba kodayaushe yau ma In Sha Allah gaisuwa ta musamman za ta je ne zuwa ga en amanata na Paid group
1. A'isha Sabo
2. Khulsum
3. A'ishahumairaazare
4. A'ishatu Muhammad
5. Amina
6. Auterr Mamy
7. Azizaty
8. Jidda Galadima
9. Maman Faruk
10. Maman Ikram
11. Mrs Hypan
12. Ummi Ja'afar
13. Zainab Umar Aliyu
14. Khadija Abubakar Oum Ashraf
15. Zainab Abubakar Yakubu
16. MAMAN IKRAM
17. Mrs Majeed
18. Ummu Hussain
19. Shafa'atu Adam Sa'id
20. Rabi'atu Buhari Walida
21. Ruƙayya Rabi'u
22. Fatima Isma'il
23. A'isha Nasir
24. Hajiya
25. Humaira Bashir
26. Ruƙayya Yahuza
27. 🌸🌸5113
28. Fatima
29. Yahanasuisma'il
30. Shafa'atu Bello
31. Ruƙayya UST
32. Zulhikmarh
33. Fatima Bashir 😩😍
34. Ummulkhaer Yusuf 😩😍
Oppps na gaji 😩 Da sauran mutanen dai, duk ina gaishe da ku. Se dai fa ta waɗannan tafi girma, saboda kasancewarsu jajirtattu wajen yin sharhi da zarar Update ya sauka. Love yhu 😘❤️ Allah Ya bar zumunci.
Domin son magana da ni kai tsaye, sharhi ko ƙarin haske za a iya tuntuɓata ta 08124818273.
SUBHANAKALLAHUMMA, WA BI HAMDIKA, ASHHADU AN LA ILA HA ILLA ANTA, ASTAGFIRUKA, WA A TUBU ILAIKA.