← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 122

Sashe 22

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kar ka matso nan. Kar ka taɓa ni na ce maka. Idan ba haka ba wallahi se na tona maka asiri a wajen duk waɗanda ke maka kallan Malamin Addini.." Ta faɗa a tsorace tana kallansa sanda ya rage saura tazara kaɗan ya cike wadda ke tsakaninsu. Yanzu kam se da ya yi dariya yana girgiza kai cike da mamakin wannan wautar ta yarinyar nan. Dan dai a samu lafiya se ya koma kan gadon ya zauna yace yana kallanta.

"Na ji ba zan taɓa ki ba. Kuma kar ki tona min asiri, amma ki ci abincin nan.." Ya faɗa kamar ba Gwanin da muka sani ba.

"Ba na ci.." ta sake faɗa tana kauda kai a zafafe. Zuwa yanzu kam yana ganin gwara ya san abin yi dan kar ta sake kai shi bango. Ga kansa dake ciwo, ga baccin da yake ji amma tana ƙoƙarin ɓata masa rai da lokaci. Se da ya daure sannan ya iya furta

"Ba ki yadda da abin da na faɗa ba kenan? Fyn.." ya yi maganar yana miƙewa. Hannu ta kai ta janyo plate ɗin da sauri wasu hawaye na kwarayowa daga cikin idanunta, ba ta san sanda ta fara kai abincin bakinta ba. Duk da cikin nata ya ɗan lafa, amma har yanzu da akwai ragowa. Tana yi kuma tana cigaba da kukanta da ƙananun maganganu a kan laɓɓanta. Se da ta ɗan ci ba laifi duk da yanda abincin ya yi daɗi har a bakinta amma taurin kai irin nata ba ze bari ta yi abin da ze sa ya ɗauka umarninsa take bi ba, ta ture plate ɗin gefe tace a kufule

"Ai dai se.."

"Shhhh!!" Ya faɗa yana ɗora hannunsa a kan laɓɓansa idanunsa a kanta yana maka mata wani kallo. Duk da ba ta kalle shi ba amma ta fahimci kallan gargaɗin da yake mata, hakan ne ya sanyata haɗiye maganar da ta yi niyyar faɗa. Ya tura mata ruwa kaɗan cikin kofi ba tare da yace komai ba. Se da ta gallawa ruwan harara sannan ta ɗauka ta sha kaɗan ɗin. Se a lokacin ya sauke ajiyar zuciya ya miƙe daga kan gadon ya fice daga wajen ma gaba ɗaya zuwa inda ya saka bargonsa yana sake jin yanda kansa ke wani irin sara masa. Binsa ta yi da harara tana faɗin

"Mugu kawai.." ta murguɗa baki tana miƙewa tana leƙen inda ya fita ɗin. Se ta miƙe duk da tana jin jiri na ɗan kwasarta amma ta ƙudurcewa kanta ba za ta sake kwana a ɗakin ba koma me za a yi mata. Dan haka wannan ƙaramin ɗakin dake cikin ɗakin ta shiga leƙawa. Da yake akwai nepa a lokacin ya sanya tana iya ganin cikin ɗakin. Komawa ta yi kan gadon, ta yayo zanin gadon da Pillow ta shiga cikin ɗakin da ƙarar kukan ƙwari ta cika shi. Jefar da zanin gadon kawai ta yi dan ba ta da ƙarfin tsayawa ta saita shi, ta yada pillown hannunta. Tana shirin kwanciya aka ɗauke nepa. Take wani uban duhu ya mamaye gaba ɗaya ɗakin, kukan ƙwarin kuma kamar an daɗa shi ya ƙaru. Cikin matuƙar tsoro da kiɗimewa ta buga wani uban tsalle ganin da ta yi gaba ɗaya idanunta ya mamaye da duhu kawai. Se dai ba ma ta san inda ta nufa ɗin ba ƙofa ba ne. Jin da ta yi ta taɓa gini ne ya sanyata kawai ta saki ƙara a matuƙar tsorace ta shiga lalube da hannayenta dan gano inda ƙofar take. Daidai lokacin da ta zo inda ƙofar take, shi kuma ya shigo cikin ɗakin saboda ihun da ya ji ta saki wanda ya tsorata shi yana fatan ba wani abun ne kuma ya sameta cikin ɗakin ba. Se hannunta ya sauka a kan ƙirjinsa, da yake ba ta tsammata ba se kawai ta yo gaba kamar za ta kifa. Be yi ƙoƙarin tareta ba saboda duhun da ya mamaye ɗakin, se da ya ji tace

"Wayyyyo.." Sannan ya yi saurin saka tattausan hannunsa ya riƙo tsintsiyar hannunta. A tsorace jin hannunta cikin wani hannun ta buɗe baki cike da sarewa da saddaƙarwa cewar yau ta haɗu da aljanu ta fashe da kuka tana kuma ƙwace hannunta lokaci ɗaya tana faɗin

"Na shiga uku.." Jin yanda hannun nata ke rawa ne da yanda take magana alamar gaba ɗaya a tsorace take ya sanya shi ɗan lumshe idanunsa ya buɗesu a lokaci ɗaya, kawai se ya janyo hannun nata se gata ta faɗo cikin jikinsa. Daidai lokacin da ilahirin jikinta ya sake ɗaukar rawa fiye da yadda be tsammata ba. Gaba ɗaya a birkice take, a matuƙar tsorace take, kamar ma wadda ba a hayyacinta take ba, ga muryarta da ta dena fita, haka zalika ba ta da wani ƙarfi. Amma duk da haka ba ta dena magana ba tana kuma ƙoƙarin ƙwace kanta. Hannunsa ya ɗauka duka biyun ya zagayeta da su cikin jikinsa sannan a hankali ya kai bakinsa saitin kunnenta yace

"Kee!! Ki yi shiru.. ki samu nutsuwa babu abin da ze faru.." ya faɗa a nutse, a ransa yana mamakin dama haka take?..

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO35*

___Runtse idanunta ta yi zuciyarta na cigaba da harbawa dan tabbas ta matuƙar tsorata. Har hakan ya sa ta kasa taɓuka komai kawai ta shiga sauke ajiyar zuciya da sauri da sauri, har kuma lokacin ta kasa buɗe idanunta. Maganarsa da ta ji ita ce ta sanar da ita inda take. Hakanne ya sanyata buɗe ido da sauri ta ture hannunsa dake bayanta sannan ta fice daga jikinsa daidai lokacin da bugun zuciyarta ya ƙaru. Kamar haɗin baki se ga nepa sun dawo da ita. Wasu zafafan hawaye suka zubo mata a kan fuskarta har kuma lokacin bata dena jin tsoro ba, ga kuma buɗe ido da ta yi ta ganta a jikin Gwanin. Ita ta rasa abin da ke damunsa, dama tun can ɗan iska ne? Shi ne ba ta sani ba. Shi burinsa kawai ya taɓata? Ina ruwansa da duk abin da ya sameta? Ai dama haka take so, daga nan kuma kawai ta wuce a zo a fiddata daga gidan nan. Sauri ta yi ta koma kan gadon ta haye, ko bi ta kan zanin gadon ba ta yi ba, ta kwanta kawai tana jan hijab ɗinta ta lulluɓe jikinta da shi. Har lokacin jikinta be bar rawa ba, haushin Gwanin na sake cikata. Ji take kamar ta fasa ihu ko za ta ji sanyi a ranta. Se dai kuma ta san tana yin ihun ze sake shigowa ne ƙila ma ya sake taɓata. Hakan ne ya sa ta kama bakinta ta dinga jan sheshsheƙar kuka a hankali. Se a lokacin ya sauke ajiyar zuciya lokacin da ya lura da ta kwanta kuma babu kukan, ko babu komai ze samu ya ɗan runtsa ko yaya ne.

... "Ni kina ba ni mamaki Yaya wallahi. Gaggawar ta meye ne? Se kace baki san wane ne Areef ba? Kin riga dai kin san halinsa ballantana ki ce kina tsoron wani abun.."

"Uhmm Makiyy ba za ki gane ba ne. Wallahi bana son auren nan kwata_kwata. Ban san dalilin da ya sa ba na so ba. Ke ko da ba Daddynsa da kansa ya samo masa matar nan ba, shi ya kawota da kansa, ba na tunanin zan bari ya auri yarinyar. Haka nan kawai na ji na tsaneta wallahi.." Girgiza kai Aunt Makiyy ta yi kamar Mom ɗin na kusa da ita tace

"Duk wannan ba wata damuwa ba ce. Za a raba auren dama ai, ko ta miki ko ba ta miki ba kuwa. Dan ba ze taɓa yiwuwa a yi wa Areef auren cushe ba, ba tare kuma da garin nan gaba ɗaya ya jijjiga ba.. Yanzu dai kin san abin da nake so dake?" Girgiza kai Mom ta yi tace

"A'ah ina jin ki.."

"Kar ki sake komawa sashen nan.. Ki kuma yi duk yanda za ki yi Daddyn Areef ya san da hakan.. Watan nan na cika komai ze baje.. Ki bar komai a hannuna, na miki alƙawarin gyara komai sannan in wargaza abin da ba ma so.." Dariya Mom ta yi cike da yabawa da wannan ƙoƙarin na ƙanwar tata tace

"Toh shi kenan Makiyy. Na san ba za ki ba ni kunya ba. Zan kuma yi iya bakin ƙoƙarina na ga ban sake zuwa sashen ba.."

"Haka nake so.." Aunt Makiyy ta faɗa tana murmushi.

... Sanye cikin doguwar rigar atamfa da ta matuƙar amsar ƙaramin jikinta. Ta saka wani baby hijab shi ma da ya karɓi zagayayyiyar doguwar farar fuskarta. Qur'an ne a hannunta tana karanta suratul baƙara. Baba Atine ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama. Da yake dab take da ƙarasa karanta ayar ƙarshe, ya sanyata ƙarasawa ta yi addu'a kana ta ajje Qur'an ɗin a kan bedside drawer ta juya ta amsa sallamar Baba Atinen. Murmushi suka sakarwa junansu, kafin Baba Atine tace

"Karatun ne?" Ta tambaya tana murmushi. Ita ma murmushin ta yi kamin ta jinjina kai kawai.

"Toh Allah ya taimaka.." In ji Baba Atine. Se da ta amsa da "Ameen" sannan tace

"Kin kai coffee ɗin kuwa?" Da sauri ta ɗaga kai ta kalli Baba Atinen ba ta san sanda a furta

"Yau ma se an kai?" Murmushi Baba Atine ta sake yi tace

"Ki daure dai 'yata.. ki cigaba da kaiwa ɗin.." Miƙewa kawai ta yi, dan dama ba ta san maganar tata ta fito fili ba.

"Ai kam kin yi kyau a hakan nan. Ki je a haka kin ji?" Ta faɗa tana murmushi. Murmushin yaƙe Didi ta yi kafin ta amsa da
Chapter 22 · 0% Book details