Sashe 83
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ku yi haƙuri Yallaɓai.. Amma na duba files ɗin nan babu wani da ke nuni da ko da makamancin abin da ya faru ne a ranar.. Duka nan kawo su aka yi daga wani wajen, mutum biyu kuma tsintarsu aka yi.. Amma babu wanda aka tsinta a ƙofar gidan nan.."
"Ya ilahy.." Daddy shi kaɗai ya iya ƙarfin halin faɗar hakan. Se da ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Kuma ka duba sosai?" Jinjina kai ya yi dan tabbatarwa da Daddyn abin da ze faɗa kafin yace
"Ƙwarai kuwa Yallaɓai... Amma kuma ina tunanin ko ba nan aka ce muku ba?" Girgiza kai Daddy ya yi kamin yace
"A'ah dan waje kam tabbas nan ne.. Se dai..." Sallamar mutumin nan da ya kawo files ɗazu ita ta dakatar da Daddy daga maganar da ya soma. Ya ƙaraso ɗauke da wani file guda ɗaya a hannunsa, ya miƙa masa yace
"Ga wani ma na ranar ne.." Karɓa ya yi yana faɗin
"Sannu da ƙoƙari." Daga haka ya fice daga ɗakin. Gaba ɗaya hankalinsu se ya koma kan file ɗin. Kusan dukansu ji suke kamar su ce ya basu su duba da kansu. Se dai suka cigaba da zuba na mujiya cike da fatan jin alkhairi.
"Yess!! Yallaɓai tabbas wannan ya yi daidai da abin da kuka faɗa.. Ƙwarai ma kuwa.." Ya faɗa har lokacin kansa na kan file ɗin se dai da murmushi kan fuskarsa.
"Alhamdulillah.." Suka haɗa baki wajen faɗin hakan. Mommah ji take kamar ta yi magana ta tambayi inda ɗanta yake tun da an gano file ɗin, dan har yanzu hankalinta a tashe yake. Se dai ta bari ta yi shiru ta cigaba da saurarar abin da ze faru.
"Kar ku damu, In Sha Allah kun samu ɗanku kun gama.. Amma dai gaskiya ina tunanin..." Se kuma ya yi shiru be ƙarasa ba, ya miƙe ya fita daga ɗakin. Runtse idanunta Mommah ta yi tana jin faɗuwar gaba, kawai se ta bar idanunta a rufe, ta shiga karanto duk addu'ar da ta zo bakinta tana kuma roƙon Allah a kan ya bayyana mata ɗanta, dan haka kawai ta ji jikinta ya yi sanyi da maganar mutumin. Gyarawa Little da ke bacci kwanciya Bad Man ya yi yana furzar da iska daga bakinsa. Me yake nufi da maganarsa ta ƙarshe?.
Bayan kusan minti 20 se ga mutumin ya dawo, har lokacin suna zaune suna jiransa. Dukansu suka ɗaga kai suka kalle shi. Ya ƙaraso ya zauna, ya kalli Alhaji Matawalle yace
"Yallaɓai Alhamdulillah Alhamdulillah..." Tun kafin su ji me ze ce Bad Man da Mommah suka sauke ajiyar zuciya kusan a tare.
"Wato cikin yaddar Ubangiji yaronka yana nan a raye har yanzun.. Tun ranar da aka tsince shi, wani bawan Allah ya zo nan da matarsa da nufin suna neman ɗa, kasancewar matarsa ba ta haihuwa.. Toh da yake dai Allah Ya ƙaddara ɗanku ze rena se aka ba su shi.. Kuma cikin yaddar Allah har yanzu yana can tare da su.."
"Allah na gode maka.. Allah Ka ƙarawa Annabi daraja." Mommah ta faɗa sanda ta runtse idanunta tsananin farin ciki na ratsata.
"Lallai Allah abun godiya.. Yanzu ya za a yi kenan?"
... Sallamar da aka yi cikin ɗakin ita ce ta sanyasu amsawa. Daddy ya kalli me sallamar daidai lokacin da shi ma ya kalle shi. Cike da mamaki dukansu suke kallan juna, kafin Abeey ya ƙaraso ya miƙawa Daddy hannu suka gaisa.
"A'ah Malam.. Barka da zuwa.." Daddy ya faɗa cike da girmamawa.
"Barka dai Yallaɓai.." Abeey ya amsa da hakan yana neman waje ya zauna bayan sun gaisa da ragowar mutanen da ke cikin ɗakin.
"Ikon Allah kwana da yawa ba mu haɗu ba.. Ba mu kuma taɓa kaiwa juna ziyara ba.. Gaskiya duk mun yi laifi.." Murmushi Abeey ya yi. Shi kullum sake ganin mutuncin Daddyn yake yi, dan tun farko be yi tunanin haka yake ba. Se da ya mu'amalance shi sannan ya fahimci halinsa. Yace
"Gaskiya kam.. Ka san da yake kwana biyu ban ji daɗi ba shi ya sa.. Toh yanzun ma dai wani muhimmin abu ne ya kawo ni cikin gidan nan.."
"Ikon Allah!! Toh Allah Ya ƙara sauƙi."
"Da ma kun san juna ne?" Dattijon mutumin nan ya faɗa yana kallansu cike da mamaki. Jinjina kai suka yi kusan a tare, kafin Daddy ya amsa da
"Ƙwarai kuwa.."
"Ikon Allah!!" Mutumin ya faɗa yana jinjina kai. Duk kuma se suka cigaba da kallansa daidai lokacin da ya fara faɗin
"Malam waɗannan su ne mutanen da na faɗa maka.. Wato ina nufin iyayen yaron nan.." Da sauri Abeey ya ɗaga ido ya kalli Daddy wanda shi ma shi yake kalla.
"Yallaɓai, Malam Abubakar shi ne wanda ya ɗauki yaron ya riƙe shi tun ranar da aka haife shi. Shi ne yaron da kowanne uba ze yi alfaharin kasancewarsa ɗansa. Ina tayaka murna." Shi fa Daddy har yanzu kansa ya kulle. A karo na barkatai ya sake kallan Abeey yace
"Wanne ɗa ake magana a kai?" Murmushi Abeey ya yi wanda iyakarsa kan fuskarsa. Wato duk da ya daɗe yana jiran wannan rana, yau ɗin kuma da ta zo tun a yanzun ilahirin jikinsa ya yi sanyi. Dan kuwa duk wata alama da ke nuna iyayen Affan sun bayyana a yau ɗin ta bayyana. Abin da be sani ba kawai me ze faru nan gaba?
"Ɗa ɗaya ke gare ni shi ne Affan.. Shi ne wanda ake magana a kai yanzu, kuma shi ɗin ne dai wanda kake tunani, yaron da na aurawa er uwar tagwaitakar sirikarka.."
"Allah buwaya gagara misali.." Daddy ya faɗa yana jinjina kai cike da mamaki. Duk da ba taɓa ganinsa ya yi ba amma tun ranar da aka ɗaura auren ya san shi a baki. Shi ya sa abun ya matuƙar ɗaure masa kai. Ashe kenan Malam ɗin ba shi da ɗa ko ɗaya se Affan? Yaron da yanzu ake magana a kansa cewar shi ne ɗan nasu da suke nema?. Sun shafe kusan rabin awa a cikin ɗakin, kafin Abeey ya miƙe a sukwane yace
"Ina ganin ya kamata ku tashi mu je can gidan.." Mommah ta riga kowa miƙewa, murmushi ya ƙi barin kan fuskarta, wato ita kaɗai ta san farin cikin da take ji a yau ɗin. Ji take kamar ta yi tsuntsuwa ta ganta cikin gidan da za ta ga ɗayan yaron nata. Saɓa Little Bad Man ya yi a kafaɗa, shi kansa ya ƙagu ya gan shi cikin gidan ko dan ya ga ɗan uwansa. Daga haka bayan sun sake yiwa Mutumin nan godiya suka fito daga ɗakin zuwa harabar gidan. A yanzu ma Daddy da kansa ya jasu. Duk suka yi ƙwam da su a baya kusan dukansu kamar su yi tsuntsuwa su gansu a gidan Abeey.
... Da sallama Abeey ya shigo cikin gidan. Lulu da ke zaune kusa da Ummeey da plate ɗin yaɗiyar da ta ji kayan haɗi da ƙuli da Ummeey ta kwaɗa a gabanta tana ci.
"Sannu da zuwa Abeey.." Lulu ta faɗa tana tsayawa da cin yaɗiyar.
"Yawwah 'yata Sannu ka dai.." Ya faɗa yana ƙarasowa cikin gidan.
"A'ah Malam.. Da ma ba daɗewa za ka yi ba ashe?"
"Wallahi kuwa.." Ya amsa mata da hakan.
"Toh sannu da zuwa.."
"Yawwah... Mu na da baƙi fa.." Ya yi maganar yana kallanta. Se ta tashi daga inda take zaune tana faɗin
"Ikon Allah baƙi kuma?"
"Ƙwarai kuwa.. Ki shirya yanzu za su shigo." Babu musu ta amsa da "Toh." Ba tare da ta tambayi su waye ba. Dan ta san da da buƙatar ta sani ɗin ze faɗa mata tun kafin ta tambaya. Lulu na shirin miƙewa Abeey yace
"Yi zamanki ɗiyata.. kar ki je ko ina.. Zauna ki ci abinki." Babu musu kuwa ta koma, dan da ma har ga Allah ba ta ji daɗin katsewa ba. Se kuwa ta cigaba da cin abarta da take ji kamar ta ma fi ta ranar nan da ta ci daɗi. Bin Abeey Ummeey ta yi da kallo lokacin da yake ƙoƙarin ficewa daga gidan. Ita dai tun da ya shigo se take ganin kamar yanayinsa duk ba daidai ba. Jikinsa a matuƙar sanyaye yake, dan hatta maganarsa ma a sanyi yake yinta. Ba dai tace komai ba musamman da ta ji yace akwai baƙi. Se kawai ta shiga ɗakin bayan ta furta
"Ce musu su shigo.. Bari a shimfiɗa tabarmar.."
.. Didi da Mommah ne suka fara shigowa cikin gidan. Duk da Ummeey ba ta shaida fuskar Mommah ba hakan be hanata faɗin
"Maraba lale.." Ta ƙare tana kallan Didi. Se ta yi murmushi fahimtar da ta yi wannan ɗin er uwar tagwaitakar Lulu ce. So se ma ta ɗauka ko wadda suke tare ita ce babarsu. Kamar an ce ta ɗaga kai se idanunta suka sauka a kan Didinta. Ba ta san lokacin da ta cire hannu daga cikin plate ɗin ba ta tashi da gudu tana faɗin
"Didina.." Ta ƙare lokacin da ta rungumeta bakinta kamar ze tsage saboda murmushi. Rungumeta ita ma Didi ta yi cike da mamakin ganin Lulun cikin gidan.
"Shi ne ba ki faɗa min za ki zo ba?" Lulu ta faɗa tana turo baki.
"Ya ilahy.." Daddy shi kaɗai ya iya ƙarfin halin faɗar hakan. Se da ya sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Kuma ka duba sosai?" Jinjina kai ya yi dan tabbatarwa da Daddyn abin da ze faɗa kafin yace
"Ƙwarai kuwa Yallaɓai... Amma kuma ina tunanin ko ba nan aka ce muku ba?" Girgiza kai Daddy ya yi kamin yace
"A'ah dan waje kam tabbas nan ne.. Se dai..." Sallamar mutumin nan da ya kawo files ɗazu ita ta dakatar da Daddy daga maganar da ya soma. Ya ƙaraso ɗauke da wani file guda ɗaya a hannunsa, ya miƙa masa yace
"Ga wani ma na ranar ne.." Karɓa ya yi yana faɗin
"Sannu da ƙoƙari." Daga haka ya fice daga ɗakin. Gaba ɗaya hankalinsu se ya koma kan file ɗin. Kusan dukansu ji suke kamar su ce ya basu su duba da kansu. Se dai suka cigaba da zuba na mujiya cike da fatan jin alkhairi.
"Yess!! Yallaɓai tabbas wannan ya yi daidai da abin da kuka faɗa.. Ƙwarai ma kuwa.." Ya faɗa har lokacin kansa na kan file ɗin se dai da murmushi kan fuskarsa.
"Alhamdulillah.." Suka haɗa baki wajen faɗin hakan. Mommah ji take kamar ta yi magana ta tambayi inda ɗanta yake tun da an gano file ɗin, dan har yanzu hankalinta a tashe yake. Se dai ta bari ta yi shiru ta cigaba da saurarar abin da ze faru.
"Kar ku damu, In Sha Allah kun samu ɗanku kun gama.. Amma dai gaskiya ina tunanin..." Se kuma ya yi shiru be ƙarasa ba, ya miƙe ya fita daga ɗakin. Runtse idanunta Mommah ta yi tana jin faɗuwar gaba, kawai se ta bar idanunta a rufe, ta shiga karanto duk addu'ar da ta zo bakinta tana kuma roƙon Allah a kan ya bayyana mata ɗanta, dan haka kawai ta ji jikinta ya yi sanyi da maganar mutumin. Gyarawa Little da ke bacci kwanciya Bad Man ya yi yana furzar da iska daga bakinsa. Me yake nufi da maganarsa ta ƙarshe?.
Bayan kusan minti 20 se ga mutumin ya dawo, har lokacin suna zaune suna jiransa. Dukansu suka ɗaga kai suka kalle shi. Ya ƙaraso ya zauna, ya kalli Alhaji Matawalle yace
"Yallaɓai Alhamdulillah Alhamdulillah..." Tun kafin su ji me ze ce Bad Man da Mommah suka sauke ajiyar zuciya kusan a tare.
"Wato cikin yaddar Ubangiji yaronka yana nan a raye har yanzun.. Tun ranar da aka tsince shi, wani bawan Allah ya zo nan da matarsa da nufin suna neman ɗa, kasancewar matarsa ba ta haihuwa.. Toh da yake dai Allah Ya ƙaddara ɗanku ze rena se aka ba su shi.. Kuma cikin yaddar Allah har yanzu yana can tare da su.."
"Allah na gode maka.. Allah Ka ƙarawa Annabi daraja." Mommah ta faɗa sanda ta runtse idanunta tsananin farin ciki na ratsata.
"Lallai Allah abun godiya.. Yanzu ya za a yi kenan?"
... Sallamar da aka yi cikin ɗakin ita ce ta sanyasu amsawa. Daddy ya kalli me sallamar daidai lokacin da shi ma ya kalle shi. Cike da mamaki dukansu suke kallan juna, kafin Abeey ya ƙaraso ya miƙawa Daddy hannu suka gaisa.
"A'ah Malam.. Barka da zuwa.." Daddy ya faɗa cike da girmamawa.
"Barka dai Yallaɓai.." Abeey ya amsa da hakan yana neman waje ya zauna bayan sun gaisa da ragowar mutanen da ke cikin ɗakin.
"Ikon Allah kwana da yawa ba mu haɗu ba.. Ba mu kuma taɓa kaiwa juna ziyara ba.. Gaskiya duk mun yi laifi.." Murmushi Abeey ya yi. Shi kullum sake ganin mutuncin Daddyn yake yi, dan tun farko be yi tunanin haka yake ba. Se da ya mu'amalance shi sannan ya fahimci halinsa. Yace
"Gaskiya kam.. Ka san da yake kwana biyu ban ji daɗi ba shi ya sa.. Toh yanzun ma dai wani muhimmin abu ne ya kawo ni cikin gidan nan.."
"Ikon Allah!! Toh Allah Ya ƙara sauƙi."
"Da ma kun san juna ne?" Dattijon mutumin nan ya faɗa yana kallansu cike da mamaki. Jinjina kai suka yi kusan a tare, kafin Daddy ya amsa da
"Ƙwarai kuwa.."
"Ikon Allah!!" Mutumin ya faɗa yana jinjina kai. Duk kuma se suka cigaba da kallansa daidai lokacin da ya fara faɗin
"Malam waɗannan su ne mutanen da na faɗa maka.. Wato ina nufin iyayen yaron nan.." Da sauri Abeey ya ɗaga ido ya kalli Daddy wanda shi ma shi yake kalla.
"Yallaɓai, Malam Abubakar shi ne wanda ya ɗauki yaron ya riƙe shi tun ranar da aka haife shi. Shi ne yaron da kowanne uba ze yi alfaharin kasancewarsa ɗansa. Ina tayaka murna." Shi fa Daddy har yanzu kansa ya kulle. A karo na barkatai ya sake kallan Abeey yace
"Wanne ɗa ake magana a kai?" Murmushi Abeey ya yi wanda iyakarsa kan fuskarsa. Wato duk da ya daɗe yana jiran wannan rana, yau ɗin kuma da ta zo tun a yanzun ilahirin jikinsa ya yi sanyi. Dan kuwa duk wata alama da ke nuna iyayen Affan sun bayyana a yau ɗin ta bayyana. Abin da be sani ba kawai me ze faru nan gaba?
"Ɗa ɗaya ke gare ni shi ne Affan.. Shi ne wanda ake magana a kai yanzu, kuma shi ɗin ne dai wanda kake tunani, yaron da na aurawa er uwar tagwaitakar sirikarka.."
"Allah buwaya gagara misali.." Daddy ya faɗa yana jinjina kai cike da mamaki. Duk da ba taɓa ganinsa ya yi ba amma tun ranar da aka ɗaura auren ya san shi a baki. Shi ya sa abun ya matuƙar ɗaure masa kai. Ashe kenan Malam ɗin ba shi da ɗa ko ɗaya se Affan? Yaron da yanzu ake magana a kansa cewar shi ne ɗan nasu da suke nema?. Sun shafe kusan rabin awa a cikin ɗakin, kafin Abeey ya miƙe a sukwane yace
"Ina ganin ya kamata ku tashi mu je can gidan.." Mommah ta riga kowa miƙewa, murmushi ya ƙi barin kan fuskarta, wato ita kaɗai ta san farin cikin da take ji a yau ɗin. Ji take kamar ta yi tsuntsuwa ta ganta cikin gidan da za ta ga ɗayan yaron nata. Saɓa Little Bad Man ya yi a kafaɗa, shi kansa ya ƙagu ya gan shi cikin gidan ko dan ya ga ɗan uwansa. Daga haka bayan sun sake yiwa Mutumin nan godiya suka fito daga ɗakin zuwa harabar gidan. A yanzu ma Daddy da kansa ya jasu. Duk suka yi ƙwam da su a baya kusan dukansu kamar su yi tsuntsuwa su gansu a gidan Abeey.
... Da sallama Abeey ya shigo cikin gidan. Lulu da ke zaune kusa da Ummeey da plate ɗin yaɗiyar da ta ji kayan haɗi da ƙuli da Ummeey ta kwaɗa a gabanta tana ci.
"Sannu da zuwa Abeey.." Lulu ta faɗa tana tsayawa da cin yaɗiyar.
"Yawwah 'yata Sannu ka dai.." Ya faɗa yana ƙarasowa cikin gidan.
"A'ah Malam.. Da ma ba daɗewa za ka yi ba ashe?"
"Wallahi kuwa.." Ya amsa mata da hakan.
"Toh sannu da zuwa.."
"Yawwah... Mu na da baƙi fa.." Ya yi maganar yana kallanta. Se ta tashi daga inda take zaune tana faɗin
"Ikon Allah baƙi kuma?"
"Ƙwarai kuwa.. Ki shirya yanzu za su shigo." Babu musu ta amsa da "Toh." Ba tare da ta tambayi su waye ba. Dan ta san da da buƙatar ta sani ɗin ze faɗa mata tun kafin ta tambaya. Lulu na shirin miƙewa Abeey yace
"Yi zamanki ɗiyata.. kar ki je ko ina.. Zauna ki ci abinki." Babu musu kuwa ta koma, dan da ma har ga Allah ba ta ji daɗin katsewa ba. Se kuwa ta cigaba da cin abarta da take ji kamar ta ma fi ta ranar nan da ta ci daɗi. Bin Abeey Ummeey ta yi da kallo lokacin da yake ƙoƙarin ficewa daga gidan. Ita dai tun da ya shigo se take ganin kamar yanayinsa duk ba daidai ba. Jikinsa a matuƙar sanyaye yake, dan hatta maganarsa ma a sanyi yake yinta. Ba dai tace komai ba musamman da ta ji yace akwai baƙi. Se kawai ta shiga ɗakin bayan ta furta
"Ce musu su shigo.. Bari a shimfiɗa tabarmar.."
.. Didi da Mommah ne suka fara shigowa cikin gidan. Duk da Ummeey ba ta shaida fuskar Mommah ba hakan be hanata faɗin
"Maraba lale.." Ta ƙare tana kallan Didi. Se ta yi murmushi fahimtar da ta yi wannan ɗin er uwar tagwaitakar Lulu ce. So se ma ta ɗauka ko wadda suke tare ita ce babarsu. Kamar an ce ta ɗaga kai se idanunta suka sauka a kan Didinta. Ba ta san lokacin da ta cire hannu daga cikin plate ɗin ba ta tashi da gudu tana faɗin
"Didina.." Ta ƙare lokacin da ta rungumeta bakinta kamar ze tsage saboda murmushi. Rungumeta ita ma Didi ta yi cike da mamakin ganin Lulun cikin gidan.
"Shi ne ba ki faɗa min za ki zo ba?" Lulu ta faɗa tana turo baki.