Sashe 54
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'ah ban sani ba. Allah Ya tsare hanya."
"Ameen in da gaske kike.." Mom ta faɗa tana sake kautar da kai.
"Salma!!" Daddy ya faɗi sunanta gatsal. Wanda ba kasafai ya saba faɗar sunan kowaccensu ba. Se dai abin da Mom ɗin ta faɗa ya sanya shi faɗin hakan. Dan ya fahimci abin da take nufi..
"Na'am.." Mom ta amsa da hakan tana kallan Daddy dan ba ta yi tunanin ya ji abin da ta faɗa ɗin ba. Se dai yanayin yanda ya kira sunan nata ne ya sanyata fahimtar ya ji abin da ta faɗa. Ita dai Mommah nunawa ma ta yi kamar ba ta ji abin da ta faɗa ba.
"Tashi kawai ki je.. Allah ya tsare.. Idan kin sauka a Abujar za mu yi magana."
"Toh. Zan kiraka kuwa Rankayadaɗe da zarar na sauka" Ta ƙare tana miƙewa gami da sakarwa Daddyn wani murmushi. Ya maida mata martanin murmushin sannan yace
"Bari na musu magana su kai ki.."
"A'ah Yallaɓai.. Ni da nake da ɗa me ye kuma zan buƙaci driver?" Ta faɗa tana satar kallan Mommah da ko kallanta ba ta yi ba.
"Ba jiya kuka yi da shi za ki je ba? Ka da kuma ki same shi busy.." Se da ta juyo sosai sannan tace
"Ni fa na haifi abuna Yallaɓai.. Da ma ban haifa ba ne se na ji wani abu.. Amma ko yanzu na ce ya min abu ai shi me min ne.. Idan ma na ce zan nemi wani bayan ga ɗana ai ma kamar na butulcewa Allah kenan bayan ya ba ni wanda zan saka ya min ba se na nema ba.." Ta tsaya a nan. Lura da ta yi Daddy ya ɗauki wayarsa da aka kira ze amsa ya sanyata ɗorawa da faɗin
"Ko ba haka ba ne Hajiya Sa'adah..?"
"Uhmm.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Dan duk wani take taken Mom ɗin ta fahimceta. Tun da ba yau ne karon farko da take mata irin haka ba. Tun tana damuwa yanzu ma har ta dena damuwa. Ta samawa kanta salama.
"Tun da na haifa dole na yi alfahari da shi, na kuma godewa Allah da be yo ni juya ba." Ta yi abin da ko yaushe da shi take amfani wajen son ganin ta ƙunsawa Mommahn baƙin cikin da ze hanata bacci. Dan ta riga ta san da wannan ɗin ne kaɗai take iya ƙuntatawa Mommahn. Yanzun ma haushi ta bata shi ya sa ta yi amfani da wannan damar wajen ƙuntata mata ita ma. Kafin Daddy yace komai ta yi saurin ficewa daga ɗakin dan ta san idan ba ta yi hakan ba dole yace wani abun. Idan ma yanzun be yi magana ba toh ta tabbatar wani lokacin ze yi. Ita dai tun da ta zubar da abin da ke ranta ai shi kenan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO53*
___Se da ta gama shiryawa tsaff cikin doguwar riga me kyau. Ta sanya baby hijab ɗin da ya kasance mahaɗin rigar. Ba ƙaramin kyau ta yi ba, kamar wadda ta tsaya ta ɓata lokaci me tsayi tana shiryawar. Neman waje ta yi ta zauna a gefen gadon. Ita dai har ga Allah ta saka a ranta ba za ta sake shiga ɗakin nan nasa ba ko mene ne kuwa. Gefe guda kuma har yanzu ba ta fidda ran tsamo shi daga wannan mummunar ɗabi'a ta shi ta shaye shaye ba da yaddar Ubangiji. Se dai kuma ba ta fatan sake shiga ɗakin nasa. Ji take tamkar ta sanarwa da Mommah abin da ke faruwa ko ta taimaka mata da shawarar yanda za su ɓillowa lamarin. Amma sam se ta ji hakan be kwanta mata ba. Da so samu ne har ta cimma burinta ma ba su sani ba. Tafi minti 10 zaune a hakan, kamar ba za ta tashi ba se kuma ta miƙe ta fice daga ɗakin. A daidai lokacin da ta kusa kitchen ɗin shi kuma ya fito daga cikin ɗakin. Shi ma ya yi matuƙar kyau kamar ko yaushe. Ji ta yi kamar ta koma kawai ta haƙura da shiga kitchen ɗin. Se dai kawai ta maaze ta ɗan runtse idanunta lokacin da take ƙoƙarin gifta shi. Ba zaka ɗauka za ta gaishe shi ba se dai cikin sanyin muryar nan tata tace
"Ina wuni?" Ba tare da ta jira amsarsa ba ta yi wuff ta faɗa kitchen. Duk da be yi niyyar amsa gaisuwar tata ba, amma kuma se ya bi bayanta da kallo yanda take ta wani sum sum da kai kamar munafuka ko kuma wadda ta ga wani dodo. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana girgiza kai sannan ya ƙarasa ficewa daga ɗakin.
... Wayarsa da ta yi ƙara ya ɗaga kai ya kalla. Ya ɗan sake buɗe idanunsa a kan wayar sannan ya miƙe. Cikin nutsuwa ya yi sallama bayan ya kara wayar a kunnensa. Daga can ɓangaren aka amsa sallamar tasa sannan aka ɗora da
"Malam Affan mu jiraka ne bayan Sallah?" A nutse ya ɗaga kansa ya kalli Lulu da ke kwance tana baccin da yanzun ba wani daɗinsa take ji ba. Hakan ne ya sanya sam ya ƙi yin nauyi. Daga zarar ta soma se ta farka a tsorace kamar wadda ake tsoratawa.
"A yi min afuwa Malam ba zan samu damar zuwa ba.."
"Toh subhanallahi.. ina fata dai lafiya." Malam Ahmad ya faɗa dan ya san tun da Gwanin yace ba ze je ba ba ƙaramin uzuri ne ya taso masa ba.
"Ehh.. In Sha Allah.." Shi ne abin da Gwani ya faɗa yana sake maida dubansa kan Lulu.
"Toh shi kenan.. Babu damuwa."
"Ina godiya.." Gwani ya faɗa ba tare da ya jira komai ba ya ajje wayar. Kai tsaye ya sake komawa inda ya tashi ɗazun. Ya sake zama yana cigaba da kallanta cike da tausayinta. Saboda duk da yanda take cikin bargo amma hakan be hana shi ganin yanda take ta mutsu mutsu ba alamar kwanciyar ta ƙi mata daɗi. Daidai lokacin aka soma kiraye kiraye a masallaci. Se ya miƙe a nutse ya faɗa toilet ya ɗauro alwala kana ya fito. Ya riga ya san ko da magana ya yi mata ba lallai ne tana da ƙarfin da za ta iya tashi ita ɗaya ba tare da taimakonsa ba. Hakan ne ya sanya shi ƙyaleta kawai ya fice daga ɗakin. Kamar ko yaushe tare suka fita masallacin da Abeey wanda yanzun jikinsa ya sake yin kyau. Kai ba za ka taɓa cewa ma ba ya da lafiya ba.
Da mamaki Abeey ya kalli Gwani lokacin da ya miƙe dan barin masallacin daga idar da Sallahr Asuba, bayan hakan ba ɗabi'arsa ba ce.
"Har za ka wuce ne Affan?"
"Ehh Abeey.." ya ba shi amsar a taƙaice.
"Toh Allah ya tsare.."
Duk da ya fahimci abin da Abeeyn ke nufi, ya ɗauka ko ze wuce inda za su haɗu ne su wuce wajen musabaƙar amma hakan be hana shi amsawa da "Ameen" ba. Kawai se ya fice daga masallacin kai tsaye ya koma gida. A inda ya barta a nan ya sameta. Ya saka hannunsa a hankali ya ɗan yaye bargon. Da yake lokacin idanunta a buɗe suke se ta yi saurin warosu sosai daidai lokacin da ta sanya hannayenta duka biyun ta riƙo bargon.
"Ki tashi ki yi Sallah.." Ya faɗa cikin taushin murya dan ma ka da ta yi tunanin umarni yake bata tace za ta yi tsiwar tata, duk da dai ya ga alama babu bakin yinta. Amma duk da haka yau ɗin komai ze mata ya fi so ya yi cikin rarrashi, tun da ya san laifinsa ne.
"Ni ka fita ka ƙyale ni.." ta faɗa da dashashshiyar muryarta da har zuwa lokacin ba ta koma daidai ba har kuma lokacin ba ta buɗe idanunta ba.
"Shi kenan.. zan fita amma ki tashi ki yi Sallahr.." Ya faɗa kai ba za ka taɓa cewa Gwani ne wannan ba. Ba tace komai ba duk da ta ji abin da ya faɗa ɗin. Bayan wajen minti 10 ta soma ƙoƙarin miƙewa dan tashi ta yi sallahr. Sake runtse idanunta ta yi saboda azabar da ta ji lokacin da ta zauna ɗin daidai lokacin da sabbin hawaye suka zubo a kan kuncinta. Sabon haushin Gwanin na sake kamata. Ji take kamar ta yi ta ihu ko za ta ji sauƙin abin da take ji. Haka dai ta daure, a daddafe ta shige banɗakin ta ɗauro alwala ta fito. Ko da ta fito kaasa tsayawa ta yi ta yi sallahr a tsaye, se zaunawa ta yi ta miƙata. Ko minti 3 ba ta ƙara zaune kan daddumar ba ta miƙe ta sake komawa kan gadon ta yi kwanciyarta tana share hawaye.
... "Tun da ka faasa zuwa wajen musabaƙar kasuwar ma kuma ba za ka je ba?" Se da ya kai hannunsa kan kwantacciyar sumar kansa sannan yace
"Ummeey ba na jin zuwa ne yau ɗin.."
"Ba ka jin zuwa kuma? Ko dai ba ka jin daɗi ne?" Ta tambaya tana karantar yanayinsa.
"A'ah Ummeey.." Sake ƙura masa idanu Ummeey ta yi. Dan ta san ƙarya ba halinsa ba ne. Duk yanda aka yi lafiyarsa ƙalau amma kuma akwai dalilin da ya hana shi fita yau ɗin.
"Lafiya kuwa Affan?" Ta ƙare maganar a sare. Dan ya kwantar mata da hankali ya sanya shi yin murmushin da ya ƙawata fuskarsa sannan yace
"Ummeey.."
"Ina Afaaf..?" Ta katse shi da wannan tambayar. Duk se ya ji jikinsa ya yi sanyi. Dan har ga Allah ba ya so Ummeey ta san abin da ya faru dan be san da wane ido ze kalleta ba. Ya yin da ita kuma Ummeey tsoranta ɗaya ka da zazzaɓin da ya kwantar da Lulu a asibiti yanzu ma shi ya rufeta. Shi kuma dan gudun kar ya tayar mata da hankali ya sanya shi ƙin faɗa mata. Dan ta riga ta saba yanzun kullum Lulun kan fitowa bayan Sallahr Asuba ta gaidata, har ma ta zauna ta tayata wasu ayyukan. Se dai yau sam ba ta ganta ba. So ta ɗauka ma ko bacci ne yau ɗin ya riƙeta. Se dai kawai kuma a yanda ta ga Gwanin ya sa hankalinta ya kaasa kwanciya.
"Bacci take Ummeey.."
"Ameen in da gaske kike.." Mom ta faɗa tana sake kautar da kai.
"Salma!!" Daddy ya faɗi sunanta gatsal. Wanda ba kasafai ya saba faɗar sunan kowaccensu ba. Se dai abin da Mom ɗin ta faɗa ya sanya shi faɗin hakan. Dan ya fahimci abin da take nufi..
"Na'am.." Mom ta amsa da hakan tana kallan Daddy dan ba ta yi tunanin ya ji abin da ta faɗa ɗin ba. Se dai yanayin yanda ya kira sunan nata ne ya sanyata fahimtar ya ji abin da ta faɗa. Ita dai Mommah nunawa ma ta yi kamar ba ta ji abin da ta faɗa ba.
"Tashi kawai ki je.. Allah ya tsare.. Idan kin sauka a Abujar za mu yi magana."
"Toh. Zan kiraka kuwa Rankayadaɗe da zarar na sauka" Ta ƙare tana miƙewa gami da sakarwa Daddyn wani murmushi. Ya maida mata martanin murmushin sannan yace
"Bari na musu magana su kai ki.."
"A'ah Yallaɓai.. Ni da nake da ɗa me ye kuma zan buƙaci driver?" Ta faɗa tana satar kallan Mommah da ko kallanta ba ta yi ba.
"Ba jiya kuka yi da shi za ki je ba? Ka da kuma ki same shi busy.." Se da ta juyo sosai sannan tace
"Ni fa na haifi abuna Yallaɓai.. Da ma ban haifa ba ne se na ji wani abu.. Amma ko yanzu na ce ya min abu ai shi me min ne.. Idan ma na ce zan nemi wani bayan ga ɗana ai ma kamar na butulcewa Allah kenan bayan ya ba ni wanda zan saka ya min ba se na nema ba.." Ta tsaya a nan. Lura da ta yi Daddy ya ɗauki wayarsa da aka kira ze amsa ya sanyata ɗorawa da faɗin
"Ko ba haka ba ne Hajiya Sa'adah..?"
"Uhmm.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Dan duk wani take taken Mom ɗin ta fahimceta. Tun da ba yau ne karon farko da take mata irin haka ba. Tun tana damuwa yanzu ma har ta dena damuwa. Ta samawa kanta salama.
"Tun da na haifa dole na yi alfahari da shi, na kuma godewa Allah da be yo ni juya ba." Ta yi abin da ko yaushe da shi take amfani wajen son ganin ta ƙunsawa Mommahn baƙin cikin da ze hanata bacci. Dan ta riga ta san da wannan ɗin ne kaɗai take iya ƙuntatawa Mommahn. Yanzun ma haushi ta bata shi ya sa ta yi amfani da wannan damar wajen ƙuntata mata ita ma. Kafin Daddy yace komai ta yi saurin ficewa daga ɗakin dan ta san idan ba ta yi hakan ba dole yace wani abun. Idan ma yanzun be yi magana ba toh ta tabbatar wani lokacin ze yi. Ita dai tun da ta zubar da abin da ke ranta ai shi kenan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO53*
___Se da ta gama shiryawa tsaff cikin doguwar riga me kyau. Ta sanya baby hijab ɗin da ya kasance mahaɗin rigar. Ba ƙaramin kyau ta yi ba, kamar wadda ta tsaya ta ɓata lokaci me tsayi tana shiryawar. Neman waje ta yi ta zauna a gefen gadon. Ita dai har ga Allah ta saka a ranta ba za ta sake shiga ɗakin nan nasa ba ko mene ne kuwa. Gefe guda kuma har yanzu ba ta fidda ran tsamo shi daga wannan mummunar ɗabi'a ta shi ta shaye shaye ba da yaddar Ubangiji. Se dai kuma ba ta fatan sake shiga ɗakin nasa. Ji take tamkar ta sanarwa da Mommah abin da ke faruwa ko ta taimaka mata da shawarar yanda za su ɓillowa lamarin. Amma sam se ta ji hakan be kwanta mata ba. Da so samu ne har ta cimma burinta ma ba su sani ba. Tafi minti 10 zaune a hakan, kamar ba za ta tashi ba se kuma ta miƙe ta fice daga ɗakin. A daidai lokacin da ta kusa kitchen ɗin shi kuma ya fito daga cikin ɗakin. Shi ma ya yi matuƙar kyau kamar ko yaushe. Ji ta yi kamar ta koma kawai ta haƙura da shiga kitchen ɗin. Se dai kawai ta maaze ta ɗan runtse idanunta lokacin da take ƙoƙarin gifta shi. Ba zaka ɗauka za ta gaishe shi ba se dai cikin sanyin muryar nan tata tace
"Ina wuni?" Ba tare da ta jira amsarsa ba ta yi wuff ta faɗa kitchen. Duk da be yi niyyar amsa gaisuwar tata ba, amma kuma se ya bi bayanta da kallo yanda take ta wani sum sum da kai kamar munafuka ko kuma wadda ta ga wani dodo. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana girgiza kai sannan ya ƙarasa ficewa daga ɗakin.
... Wayarsa da ta yi ƙara ya ɗaga kai ya kalla. Ya ɗan sake buɗe idanunsa a kan wayar sannan ya miƙe. Cikin nutsuwa ya yi sallama bayan ya kara wayar a kunnensa. Daga can ɓangaren aka amsa sallamar tasa sannan aka ɗora da
"Malam Affan mu jiraka ne bayan Sallah?" A nutse ya ɗaga kansa ya kalli Lulu da ke kwance tana baccin da yanzun ba wani daɗinsa take ji ba. Hakan ne ya sanya sam ya ƙi yin nauyi. Daga zarar ta soma se ta farka a tsorace kamar wadda ake tsoratawa.
"A yi min afuwa Malam ba zan samu damar zuwa ba.."
"Toh subhanallahi.. ina fata dai lafiya." Malam Ahmad ya faɗa dan ya san tun da Gwanin yace ba ze je ba ba ƙaramin uzuri ne ya taso masa ba.
"Ehh.. In Sha Allah.." Shi ne abin da Gwani ya faɗa yana sake maida dubansa kan Lulu.
"Toh shi kenan.. Babu damuwa."
"Ina godiya.." Gwani ya faɗa ba tare da ya jira komai ba ya ajje wayar. Kai tsaye ya sake komawa inda ya tashi ɗazun. Ya sake zama yana cigaba da kallanta cike da tausayinta. Saboda duk da yanda take cikin bargo amma hakan be hana shi ganin yanda take ta mutsu mutsu ba alamar kwanciyar ta ƙi mata daɗi. Daidai lokacin aka soma kiraye kiraye a masallaci. Se ya miƙe a nutse ya faɗa toilet ya ɗauro alwala kana ya fito. Ya riga ya san ko da magana ya yi mata ba lallai ne tana da ƙarfin da za ta iya tashi ita ɗaya ba tare da taimakonsa ba. Hakan ne ya sanya shi ƙyaleta kawai ya fice daga ɗakin. Kamar ko yaushe tare suka fita masallacin da Abeey wanda yanzun jikinsa ya sake yin kyau. Kai ba za ka taɓa cewa ma ba ya da lafiya ba.
Da mamaki Abeey ya kalli Gwani lokacin da ya miƙe dan barin masallacin daga idar da Sallahr Asuba, bayan hakan ba ɗabi'arsa ba ce.
"Har za ka wuce ne Affan?"
"Ehh Abeey.." ya ba shi amsar a taƙaice.
"Toh Allah ya tsare.."
Duk da ya fahimci abin da Abeeyn ke nufi, ya ɗauka ko ze wuce inda za su haɗu ne su wuce wajen musabaƙar amma hakan be hana shi amsawa da "Ameen" ba. Kawai se ya fice daga masallacin kai tsaye ya koma gida. A inda ya barta a nan ya sameta. Ya saka hannunsa a hankali ya ɗan yaye bargon. Da yake lokacin idanunta a buɗe suke se ta yi saurin warosu sosai daidai lokacin da ta sanya hannayenta duka biyun ta riƙo bargon.
"Ki tashi ki yi Sallah.." Ya faɗa cikin taushin murya dan ma ka da ta yi tunanin umarni yake bata tace za ta yi tsiwar tata, duk da dai ya ga alama babu bakin yinta. Amma duk da haka yau ɗin komai ze mata ya fi so ya yi cikin rarrashi, tun da ya san laifinsa ne.
"Ni ka fita ka ƙyale ni.." ta faɗa da dashashshiyar muryarta da har zuwa lokacin ba ta koma daidai ba har kuma lokacin ba ta buɗe idanunta ba.
"Shi kenan.. zan fita amma ki tashi ki yi Sallahr.." Ya faɗa kai ba za ka taɓa cewa Gwani ne wannan ba. Ba tace komai ba duk da ta ji abin da ya faɗa ɗin. Bayan wajen minti 10 ta soma ƙoƙarin miƙewa dan tashi ta yi sallahr. Sake runtse idanunta ta yi saboda azabar da ta ji lokacin da ta zauna ɗin daidai lokacin da sabbin hawaye suka zubo a kan kuncinta. Sabon haushin Gwanin na sake kamata. Ji take kamar ta yi ta ihu ko za ta ji sauƙin abin da take ji. Haka dai ta daure, a daddafe ta shige banɗakin ta ɗauro alwala ta fito. Ko da ta fito kaasa tsayawa ta yi ta yi sallahr a tsaye, se zaunawa ta yi ta miƙata. Ko minti 3 ba ta ƙara zaune kan daddumar ba ta miƙe ta sake komawa kan gadon ta yi kwanciyarta tana share hawaye.
... "Tun da ka faasa zuwa wajen musabaƙar kasuwar ma kuma ba za ka je ba?" Se da ya kai hannunsa kan kwantacciyar sumar kansa sannan yace
"Ummeey ba na jin zuwa ne yau ɗin.."
"Ba ka jin zuwa kuma? Ko dai ba ka jin daɗi ne?" Ta tambaya tana karantar yanayinsa.
"A'ah Ummeey.." Sake ƙura masa idanu Ummeey ta yi. Dan ta san ƙarya ba halinsa ba ne. Duk yanda aka yi lafiyarsa ƙalau amma kuma akwai dalilin da ya hana shi fita yau ɗin.
"Lafiya kuwa Affan?" Ta ƙare maganar a sare. Dan ya kwantar mata da hankali ya sanya shi yin murmushin da ya ƙawata fuskarsa sannan yace
"Ummeey.."
"Ina Afaaf..?" Ta katse shi da wannan tambayar. Duk se ya ji jikinsa ya yi sanyi. Dan har ga Allah ba ya so Ummeey ta san abin da ya faru dan be san da wane ido ze kalleta ba. Ya yin da ita kuma Ummeey tsoranta ɗaya ka da zazzaɓin da ya kwantar da Lulu a asibiti yanzu ma shi ya rufeta. Shi kuma dan gudun kar ya tayar mata da hankali ya sanya shi ƙin faɗa mata. Dan ta riga ta saba yanzun kullum Lulun kan fitowa bayan Sallahr Asuba ta gaidata, har ma ta zauna ta tayata wasu ayyukan. Se dai yau sam ba ta ganta ba. So ta ɗauka ma ko bacci ne yau ɗin ya riƙeta. Se dai kawai kuma a yanda ta ga Gwanin ya sa hankalinta ya kaasa kwanciya.
"Bacci take Ummeey.."