Sashe 3
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.." Shi ne abin da Kaseem yake maimaitawa. Zuciyarsa na masa wani irin zafi. Be taɓa tunanin abin da ze zo ya ji daga bakin Abban ba kenan. Da ya san wannan zancen kunnuwansa zasu ji masa da ya yi fatan Allah ya kawo dalilin da zesa be zo ba. Ashe ba ze taɓa samun Afrah ba? Ashe Afrah matar wani zata zama? Ashe duk saurin da yake a bashi ita a banza. Lallai kuwa kamar yanda Abban ya faɗa ne kana naka Allah na na shi. Da ƙyar ya iya buɗe baki, bayan shuɗewar wasu mintuna tun bayan da Abba ya gama magana yace
"Babu komai Abba.. Allah yasa haka ne mafi alkhairi.. Na kuma gode da wannan shedar da na samu. Ni kaina da kana da wata ɗiyar Abba da kaina zan nemi ka bani ita, se dai tunda babu, dole zan haƙura. Allah ya riga ya tsara dama ba matata bace.. Allah ya basu zaman lafiya.." ya ƙare muryarsa a raunane. Cike da tausayawa Abba yace
"Ameen.." Miƙewa Kaseem ya yi yace
"Bari na tafi Abba.." Binsa da kallo Abba ya yi yana sake jin tausayinsa na ratsa shi yace
"Toh.. Allah ya yi maka albarka.." Da ƙyar ya iya amsawa da
"Ameen.." ya fice daga ɗakin. Abba ya bi shi da kallo har ya fice ɗin. Ko da ya hau motarsa kasa taɓuka komai ya yi. Ji ya yi inama shi mace ne ya dirza kukansa har da ihu, ko da mutane zasu fahimci irin raɗaɗin da zuciyarsa take. Duk da haka kuwa se da wata ƙwalla ta tarar masa cikin idanunsa, jikinsa har wani ɗumi ya ɗauka. Wannan maganar na ɗaya daga cikin munanan maganganun da ya ya taɓa ji. Za kuma ta cigaba da zama a mummunarta har zuwa lokacin da be san ƙarshensa ba.
"Ashe ba zan taɓa samunki ba Afrah.. Wallahi ina sonki.. Ina sonki.." ya faɗa sanda ya kifa kansa a kan steering motar, zuciyarsa na cigaba da zafi. Da ƙyar ya iya tashi ya kunna motar ya tasheta. Cikin ƙarfin hali ya soma driving ɗin zuciyarsa cike fall da tunani.
... "Hero wai me kake nufi ne don Allah?" Shiru Hero ya sake yi a karo na biyu.
"Kace min wani abu mana. Ya ake ciki? Ni dama ban so ka shigo da wani cikin wannan al'amarin ba.. yanzu ga shi komai ya caɓe mana.. kai kanka ma baka san abin da ke faruwa ba.."
"Kin ga Ladi.. Ki ɗan sararamin na yi tunanin abin da ya kamata. Ina ta kiran layinsa tun tana shiga yanzu ma ta dena shiga. Me kike tunani? Kika sani ko ta rutsa da shi ne? Ni daga yanzu ma na dena kiransa kada a gane numberta, idan ma wani abun ne ya rutsa da shi daga baya a zo a binciko ni haka kurum.."
"Toh yanzu me kake nufi?" Ladi ta faɗa tana kallansa
"Mu jira nan da kwana 3 haka, idan dai ban ji daga gare shi ba, toh dole zan san abin yi.."
"Anya kuwa ba zan tura Abida ta je gidansu yarinyar nan ta duba min abin da ke faruwa ba?" Dariya Hero ya yi yana girgiza kai. Ya saki tsaki kafin yace
"Toh maza aikata tunda man kanki ya tsotse.." ya faɗa yana watsa mata wani kallo. Ajiyar zuciya ta sauke dan ta fahimci gatse Heron yake mata, tace
"Shi kenan.. Bari na jiraka.."
"Ya dai fi miki.."
... Kai tsaye ɗakin Daddy suka wuce gaba ɗayansu. A babban parlournsa suka zauna.
"Za ka zauna anan har ka samu ka gama warwarewa gaba ɗaya.." Daddy ya faɗa yana kallan Bad.
"Bana jin komai yanzun.." ya faɗa bayan ya ɗan lumshe idanunsa ya kuma buɗe su a lokaci ɗaya.
"Duk da haka.. Amm zaka iya tuna dalilinka na zuwa gidansu yarinyar nan?" Daddy ya faɗa yana kallansa
"Yarinya?" Ya tambaya sanda fuskarsa ke a tsuke.
"Gidansu yarinyar da ka je ka faɗi a can.. Mene ne ainahin dalilinka na zuwa." Shiru Bad Man ya yi na tsawon sakanni be ce komai ba. Shi sam ya ma manta da abin da abin da ya faru, idan ba yanzun da Daddy ya yi maganar ba.
"I don't know who is she.. ban san waye ya aikota ba. She slapped me! Dats why na bita har gidansu dan na san wanda ya aikota. Na kuma mareta a gaban en gidan nasu, saboda su san babu abin da zasu iya min.."
"Mari kuma Boy? Wace ce ita? Waye ubanta a ƙasar nan? Me take taƙama da shi da har ta mareka? Wa take taƙama ze tsaya mata?" Mom ta faɗa a fusace. Shi kuwa Daddy kallansa kawai yake yi, tunda ya fara maganar har ya ƙare. Cikin takaici yace
"Kafin ka je gidan ina ka fara zuwa? Da wa kuma haɗu?"
"Hero!" Numfashi Daddy ya ja ya ajje. So yake ya ji duk abin da ya faru, hakan ne ya sanya shi faɗin
"Tare kuka je gidansu yarinyar da shi?"
"Yeap.. but a waje ya tsaya.." Ya faɗa yana ƙoƙarin miƙewa.
"Koma ka zauna.. bamu gama maganar ba.."
"Amma na gaji Dad.." Be bi ta kan abin da ya faɗa ba yace
"Kafin ku tafi.. ba ka sha wani abu ba?"
"Wani abu? Lyk how?" Ya faɗa yana kallan Daddyn. Se kuma yace
"Ohh.. yes.. but juice ne kawai.."
"Waye ya baka?" Daddy ya katse shi da faɗin hakan.
"Dad.." ya faɗa cike da ƙosawa.
"Ka bani amsa.."
"Hero.." ya faɗa a taƙaice. Runtse idanunsa Daddy ya yi, ashe ba a banza ba ya raba Areef ɗin da Hero. Dama tun farko be masa ba, so be ɗauka ma suna tare ba tun bayan barinsa Nigeria.
"Yallaɓai wai tambayoyin nan duka na mene?" Mom ta faɗa tana kallan Daddy.
"Idan zaki iya saurara u're welcome. Idan kuma ba zaki iya ba za ki iya bamu waje.." Jin abin da Daddyn ya faɗa ne ya sanya ta yin shiru kawai. Dan ta ga alama a fusace Daddyn yake.
"Ka san me yasa na rabaka da yaron? Baya sonka da alkhairi.. ya zuba maka wani abu cikin lemon, domin idan ka je gidansu yarinyar ka aikata mata abin da be kamata ba.."
"What?" Bad Man ya faɗa yana kallan Daddy ransa a mugun ɓace. Angry face ɗinsa a haɗe kamar hadari.
"Me na aikata Dad? Pls tell me.." ya yi maganar ɓacin ransa na daɗuwa cike da ƙosawa da son jin amsar da Daddyn ze ba shi. Se da Daddy ya sauke numfashi sannan yace
"Allah ya tsare.. babu abin da ya faru.." Wata ƙatuwar ajiyar zuciya Mom dake gefe ta sauke, yayin da Bad ya dafe kansa yana tunanin dalilin da ya saka Hero ɗin ze yi masa haka.
"Se dai dalilin zuwanka gidan da kuma faɗuwar da ka yi zuwa kaika asibiti yasa mutane sun ganka.. sun kuma ganni, sun kuma ga Mahaifiyarka.. Idan dai zaka iya tunawa ko da zamu fito daga cikin asibitin nan, idanun mutane a kanmu suke.. Ita kanta yarinyar kuma tare aka kawoku asibiti saboda bugewar da ta yi a kanta, wanda hakan ya janyo mata ta suma. Mutane kuma duk sun ga sanda hakan ta faru. Sanin kanka ne bana son duk wani nau'i na zargi, ba kuma na san kai kanka ka shiga cikin waɗanda ake zargi, dan kuwa zargi mugun ƙulli ne.. Wannan dalilin ne ya sanya ni aura maka yarinyar." Cikin matuƙar mamaki, tashin hankali Mom tace bayan ta miƙe tsaye
"Aure kuma Abubakar? Ka aurar min da ɗa ba tare da izinina ba? Ko kuwa dai ka faɗa ne kawai dan nishaɗi?" Mom ta faɗa a fusace, dan matuƙa ranta ya ɓaci da maganar Daddyn. In dai kuma har da gaske abin da ya faɗa gaskiya ne akwai babban tashin hankali a cikin gidan. Yanda ta kira sunan shi kai tsaye, da yanda take iƙirarin ya aurar mata da ɗa ba tare da izininta ba ya sanya shi yi mata shiru idan ta gama ya kulata. Jin tana neman ɗorawa ne ya sanya shi katseta da faɗin
"Ki nemi waje ki zauna.. Wannan abun da kike babu abin da ze sauya, dan kuwa kamar yanda kika ji ne na ɗaurawa Areef aure da yarinyar nan.." Se a lokacin Bad ya fahimci ma abin da Daddyn ke faɗa. Ya fahimci me Daddyn ke ƙoƙarin faɗa. Se dai ya san Daddyn nasa ƙalau yake, ya kuma san mutumin arziƙi ne. Se dai a yau yana da yaƙinin wani abokin nasa shi ma ya zuba masa wani abun cikin lemo ya sha, shi yasa yake irin wannan maganar da har abada ma baya tunanin zata taɓa faruwa. Se da ya ɗan sake lumshe idanunsa sannan ya soma miƙewa a kan ƙafafunsa.
"Ina zaka je? Dawo ka zauna, ka kuma sake tabbatar da abin da kunnuwanka suka jiye maka.." Daddy ya faɗa yana kallan Bad Man dake ƙoƙarin barin ɗakin. Juyowa ya yi, kawai se ya tsaya yana kallan Daddyn kamar wanda ya ga sabuwar halitta. Jira kawai yake Daddyn ya sake maimaita abin da ya faɗa ɗazun sannan ya san abin yi.
... "Kama gidan haya ba mafita bace.. Saboda tsaro gwara a yi abin da ze yiwu.." Abeey ya bawa Ummeey amsa.
"Toh kai Affan.. ya kake ganin za a yi?" Ummeeyn ta faɗa tana kallansa. Shiru ya yi na ɗan wani lokaci. Duk da baya jin daɗin maganar, amma ya zama dole ya tsaya a yi maganar, ko dan farin cikin iyayen nasa.
"Abeey ina ganin kawai a gyara mata ɗakin can se ta zauna a ciki.."
"Ja'iri.. ce maka aka yi er aiki ce aka kawo? Da za a bata ɗaki ita ɗaya? Malam me ze hana kamar yadda ya faɗa ɗin a gyara ɗakin nan, duk da dai ba girma gare shi ba, amma ko yaya ne dai za a samu abin da ake so. Idan yaso se a shigar da shi cikin ɗakin Affan.. A samu ko ɗan fenti ne a yi, se ta zauna anan ɗin koh?" Ummeey ta ƙare maganar tana kallan Abeey..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO25*
___"Ka fahimci abin da na faɗa? Za ka iya tafiya.."
"Babu komai Abba.. Allah yasa haka ne mafi alkhairi.. Na kuma gode da wannan shedar da na samu. Ni kaina da kana da wata ɗiyar Abba da kaina zan nemi ka bani ita, se dai tunda babu, dole zan haƙura. Allah ya riga ya tsara dama ba matata bace.. Allah ya basu zaman lafiya.." ya ƙare muryarsa a raunane. Cike da tausayawa Abba yace
"Ameen.." Miƙewa Kaseem ya yi yace
"Bari na tafi Abba.." Binsa da kallo Abba ya yi yana sake jin tausayinsa na ratsa shi yace
"Toh.. Allah ya yi maka albarka.." Da ƙyar ya iya amsawa da
"Ameen.." ya fice daga ɗakin. Abba ya bi shi da kallo har ya fice ɗin. Ko da ya hau motarsa kasa taɓuka komai ya yi. Ji ya yi inama shi mace ne ya dirza kukansa har da ihu, ko da mutane zasu fahimci irin raɗaɗin da zuciyarsa take. Duk da haka kuwa se da wata ƙwalla ta tarar masa cikin idanunsa, jikinsa har wani ɗumi ya ɗauka. Wannan maganar na ɗaya daga cikin munanan maganganun da ya ya taɓa ji. Za kuma ta cigaba da zama a mummunarta har zuwa lokacin da be san ƙarshensa ba.
"Ashe ba zan taɓa samunki ba Afrah.. Wallahi ina sonki.. Ina sonki.." ya faɗa sanda ya kifa kansa a kan steering motar, zuciyarsa na cigaba da zafi. Da ƙyar ya iya tashi ya kunna motar ya tasheta. Cikin ƙarfin hali ya soma driving ɗin zuciyarsa cike fall da tunani.
... "Hero wai me kake nufi ne don Allah?" Shiru Hero ya sake yi a karo na biyu.
"Kace min wani abu mana. Ya ake ciki? Ni dama ban so ka shigo da wani cikin wannan al'amarin ba.. yanzu ga shi komai ya caɓe mana.. kai kanka ma baka san abin da ke faruwa ba.."
"Kin ga Ladi.. Ki ɗan sararamin na yi tunanin abin da ya kamata. Ina ta kiran layinsa tun tana shiga yanzu ma ta dena shiga. Me kike tunani? Kika sani ko ta rutsa da shi ne? Ni daga yanzu ma na dena kiransa kada a gane numberta, idan ma wani abun ne ya rutsa da shi daga baya a zo a binciko ni haka kurum.."
"Toh yanzu me kake nufi?" Ladi ta faɗa tana kallansa
"Mu jira nan da kwana 3 haka, idan dai ban ji daga gare shi ba, toh dole zan san abin yi.."
"Anya kuwa ba zan tura Abida ta je gidansu yarinyar nan ta duba min abin da ke faruwa ba?" Dariya Hero ya yi yana girgiza kai. Ya saki tsaki kafin yace
"Toh maza aikata tunda man kanki ya tsotse.." ya faɗa yana watsa mata wani kallo. Ajiyar zuciya ta sauke dan ta fahimci gatse Heron yake mata, tace
"Shi kenan.. Bari na jiraka.."
"Ya dai fi miki.."
... Kai tsaye ɗakin Daddy suka wuce gaba ɗayansu. A babban parlournsa suka zauna.
"Za ka zauna anan har ka samu ka gama warwarewa gaba ɗaya.." Daddy ya faɗa yana kallan Bad.
"Bana jin komai yanzun.." ya faɗa bayan ya ɗan lumshe idanunsa ya kuma buɗe su a lokaci ɗaya.
"Duk da haka.. Amm zaka iya tuna dalilinka na zuwa gidansu yarinyar nan?" Daddy ya faɗa yana kallansa
"Yarinya?" Ya tambaya sanda fuskarsa ke a tsuke.
"Gidansu yarinyar da ka je ka faɗi a can.. Mene ne ainahin dalilinka na zuwa." Shiru Bad Man ya yi na tsawon sakanni be ce komai ba. Shi sam ya ma manta da abin da abin da ya faru, idan ba yanzun da Daddy ya yi maganar ba.
"I don't know who is she.. ban san waye ya aikota ba. She slapped me! Dats why na bita har gidansu dan na san wanda ya aikota. Na kuma mareta a gaban en gidan nasu, saboda su san babu abin da zasu iya min.."
"Mari kuma Boy? Wace ce ita? Waye ubanta a ƙasar nan? Me take taƙama da shi da har ta mareka? Wa take taƙama ze tsaya mata?" Mom ta faɗa a fusace. Shi kuwa Daddy kallansa kawai yake yi, tunda ya fara maganar har ya ƙare. Cikin takaici yace
"Kafin ka je gidan ina ka fara zuwa? Da wa kuma haɗu?"
"Hero!" Numfashi Daddy ya ja ya ajje. So yake ya ji duk abin da ya faru, hakan ne ya sanya shi faɗin
"Tare kuka je gidansu yarinyar da shi?"
"Yeap.. but a waje ya tsaya.." Ya faɗa yana ƙoƙarin miƙewa.
"Koma ka zauna.. bamu gama maganar ba.."
"Amma na gaji Dad.." Be bi ta kan abin da ya faɗa ba yace
"Kafin ku tafi.. ba ka sha wani abu ba?"
"Wani abu? Lyk how?" Ya faɗa yana kallan Daddyn. Se kuma yace
"Ohh.. yes.. but juice ne kawai.."
"Waye ya baka?" Daddy ya katse shi da faɗin hakan.
"Dad.." ya faɗa cike da ƙosawa.
"Ka bani amsa.."
"Hero.." ya faɗa a taƙaice. Runtse idanunsa Daddy ya yi, ashe ba a banza ba ya raba Areef ɗin da Hero. Dama tun farko be masa ba, so be ɗauka ma suna tare ba tun bayan barinsa Nigeria.
"Yallaɓai wai tambayoyin nan duka na mene?" Mom ta faɗa tana kallan Daddy.
"Idan zaki iya saurara u're welcome. Idan kuma ba zaki iya ba za ki iya bamu waje.." Jin abin da Daddyn ya faɗa ne ya sanya ta yin shiru kawai. Dan ta ga alama a fusace Daddyn yake.
"Ka san me yasa na rabaka da yaron? Baya sonka da alkhairi.. ya zuba maka wani abu cikin lemon, domin idan ka je gidansu yarinyar ka aikata mata abin da be kamata ba.."
"What?" Bad Man ya faɗa yana kallan Daddy ransa a mugun ɓace. Angry face ɗinsa a haɗe kamar hadari.
"Me na aikata Dad? Pls tell me.." ya yi maganar ɓacin ransa na daɗuwa cike da ƙosawa da son jin amsar da Daddyn ze ba shi. Se da Daddy ya sauke numfashi sannan yace
"Allah ya tsare.. babu abin da ya faru.." Wata ƙatuwar ajiyar zuciya Mom dake gefe ta sauke, yayin da Bad ya dafe kansa yana tunanin dalilin da ya saka Hero ɗin ze yi masa haka.
"Se dai dalilin zuwanka gidan da kuma faɗuwar da ka yi zuwa kaika asibiti yasa mutane sun ganka.. sun kuma ganni, sun kuma ga Mahaifiyarka.. Idan dai zaka iya tunawa ko da zamu fito daga cikin asibitin nan, idanun mutane a kanmu suke.. Ita kanta yarinyar kuma tare aka kawoku asibiti saboda bugewar da ta yi a kanta, wanda hakan ya janyo mata ta suma. Mutane kuma duk sun ga sanda hakan ta faru. Sanin kanka ne bana son duk wani nau'i na zargi, ba kuma na san kai kanka ka shiga cikin waɗanda ake zargi, dan kuwa zargi mugun ƙulli ne.. Wannan dalilin ne ya sanya ni aura maka yarinyar." Cikin matuƙar mamaki, tashin hankali Mom tace bayan ta miƙe tsaye
"Aure kuma Abubakar? Ka aurar min da ɗa ba tare da izinina ba? Ko kuwa dai ka faɗa ne kawai dan nishaɗi?" Mom ta faɗa a fusace, dan matuƙa ranta ya ɓaci da maganar Daddyn. In dai kuma har da gaske abin da ya faɗa gaskiya ne akwai babban tashin hankali a cikin gidan. Yanda ta kira sunan shi kai tsaye, da yanda take iƙirarin ya aurar mata da ɗa ba tare da izininta ba ya sanya shi yi mata shiru idan ta gama ya kulata. Jin tana neman ɗorawa ne ya sanya shi katseta da faɗin
"Ki nemi waje ki zauna.. Wannan abun da kike babu abin da ze sauya, dan kuwa kamar yanda kika ji ne na ɗaurawa Areef aure da yarinyar nan.." Se a lokacin Bad ya fahimci ma abin da Daddyn ke faɗa. Ya fahimci me Daddyn ke ƙoƙarin faɗa. Se dai ya san Daddyn nasa ƙalau yake, ya kuma san mutumin arziƙi ne. Se dai a yau yana da yaƙinin wani abokin nasa shi ma ya zuba masa wani abun cikin lemo ya sha, shi yasa yake irin wannan maganar da har abada ma baya tunanin zata taɓa faruwa. Se da ya ɗan sake lumshe idanunsa sannan ya soma miƙewa a kan ƙafafunsa.
"Ina zaka je? Dawo ka zauna, ka kuma sake tabbatar da abin da kunnuwanka suka jiye maka.." Daddy ya faɗa yana kallan Bad Man dake ƙoƙarin barin ɗakin. Juyowa ya yi, kawai se ya tsaya yana kallan Daddyn kamar wanda ya ga sabuwar halitta. Jira kawai yake Daddyn ya sake maimaita abin da ya faɗa ɗazun sannan ya san abin yi.
... "Kama gidan haya ba mafita bace.. Saboda tsaro gwara a yi abin da ze yiwu.." Abeey ya bawa Ummeey amsa.
"Toh kai Affan.. ya kake ganin za a yi?" Ummeeyn ta faɗa tana kallansa. Shiru ya yi na ɗan wani lokaci. Duk da baya jin daɗin maganar, amma ya zama dole ya tsaya a yi maganar, ko dan farin cikin iyayen nasa.
"Abeey ina ganin kawai a gyara mata ɗakin can se ta zauna a ciki.."
"Ja'iri.. ce maka aka yi er aiki ce aka kawo? Da za a bata ɗaki ita ɗaya? Malam me ze hana kamar yadda ya faɗa ɗin a gyara ɗakin nan, duk da dai ba girma gare shi ba, amma ko yaya ne dai za a samu abin da ake so. Idan yaso se a shigar da shi cikin ɗakin Affan.. A samu ko ɗan fenti ne a yi, se ta zauna anan ɗin koh?" Ummeey ta ƙare maganar tana kallan Abeey..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO25*
___"Ka fahimci abin da na faɗa? Za ka iya tafiya.."