Sashe 104
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haka ne Afrah.. Zan yanke hukunci ne a kan rayuwarku tamkar a kan rayuwar 'ya'yan da na haifa. Saboda ku ɗin 'ya'yana ne. Na kuma yanke hukuncin nan ne bayan ganin shi ne ya dace. Ina kuma fatan Allah Ya sanya albarka a ciki, Ya kaɗe fitina, Ya kuma ƙara haɗa min kanku gaba ɗaya, Ameen." Dukkansu shiru suka yi. Mommah ta yi murmushi tana ji a ranta lallai ta yi sa'ar surukai ita kam.
... Washegari da sassafe me gyaran jikin da Mommah ta kirawo ta zo cikin gidan. Ɗaki guda aka ware musu cikin ƙanƙanin lokaci ta soma aikinta. Sosai yau ɗin Mommah ta bayar da wuta, dan so take komai dare a yau ta bawa kowa matarsa. Dan haka ta saka an gyara sashen da kowannensu ze zauna kafin a ƙarasa wanda Daddy ya sa aka fara ginawa. Dan tuni har ya ba da umarni an fara gina inda 'ya'yan nasa za su zauna. Da kuma wanda Ummeey da Abeey za su zauna ciki, amma su se sun dawo daga Makkah.
... Zaune yake cikin palourn hannunsa ɗauke da wani littafin addini yana karantawa. Wajen minti 10 se ya rufe littafin ya kalli tamfatsetsen agogon da ke manne a bangon ɗakin. Ƙarfe 9 daidai ya nuna. Ya ɗan lumshe idanunsa yana jin yanda bacci ke cin idanunsa. Qur'an ɗin da ke ajje a gabansa da wasu littafan ya ɗauka da niyyar shigewa ɗaki ya samu ya watsa ruwa ya kwanta. Sallamar Mommah da ya ji ita ce ta dakatar da shi, ya juya ya kalli bakin ƙofar lokaci ɗaya yana amsa sallamar. Tun kafin ya kai ƙarshen sallamar idanunsa suka sauka a kan Lulu da ke sanye cikin wata doguwar rigar atamfa. Mayafin da ya dace da atamfar saye saman ɗankwalin da ke zaune a kanta. Ta yi wani daƙiƙin kyau kamar ka saceta ka gudu.
Lumshe idanunsa ya yi yana buɗe su a kanta. Sam mantawa ma ya yi tare da Mommah ne suke tare, har se da ya ji muryar Mommah tace
"Toh zauna koh?" Se a lokacin ya tuna a inda yake, ya yi saurin basarwa yana ƙaƙalo murmushi ya nemi waje ya zauna jiki a sanyaye. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke kafin yace
"Mommah.." Ya yi maganar yana iya ƙoƙarinsa wajen ganin be kalli Lulu ba. Lulun da ke zaune gefen Mommah kanta a ƙasa kamar munafuka.
"Na'am.." Mommah ta amsa da hakan tana murmushi. Shiru ne ya wanzu na tsawon lokaci. Shi dai Gwani jira kawai yake ya ji me ye ya kawo Mommah da Lulun cikin ɗakin? Musamman da tun ganinta da ya yi duk baccin da yake ji ya tafi. A hankali Mommah ta soma faɗin
"Areef.."
"Na'am Mommah." Ya amsa da hakan yana ɗaga kai ya kalleta. Se ta cigaba da faɗin
"Ga Afaaf nan na dawo maka da ita.. Ba na jinka in Sha Allah.. Se dai duk da haka ina me roƙonka da ka riƙeta amana. Ka kuma kula da ita gwargwadon iyawarka." Be san sanda ya lumshe idanunsa ba, yana jin wani irin farin ciki na ratsa shi. Kenan idan dai har ya fahimci zancen Mommahn tana nufin ta dawo masa da matarsa kenan?
"In Sha Allah Mommah ba za ki kuka da ni ba.. Na gode Allah Ya ƙara girma."
"Ameen.." Mommah ta faɗa tana murmushi, daidai lokacin da ta maida dubanta kan Lulu. Babu buƙatar yi mata faɗa ko wata maganar, dan duk wani abu da ya kamata ta faɗa mata ta faɗa musu tun kafin su fito. Dan haka kawai hannunta ta kamo tace a hankali
"Bari na wuce Daughter.." Se a lokacin sannan Lulu ta ɗaga kai ta kalli Mommah cikin sanyin murya kamar Didi tace
"Tohm." Daga haka ba ta sake cewa komai ba. Ita ma Mommahn ba tace komai ba se ficewa daga ɗakin da ta yi. A hankali ya ɗaga kansa ya kalli Lulu da ta cigaba da zama a kan kujerar tana wasa da yatsun hannunta. Miƙewa ya yi a nutse ya koma ya zauna a kan kujerar da take kai. Yanda ta yi ƙasa da kai hakan ba ƙaramin ba shi damar kallanta ya yi ba. Ya ƙura mata ido kamar wanda ya soma ganinta yau. Se ya ga yau ɗin ta sake wani irin kyau, ta sake murjewa, farar fatar jikinta ta yi fresh ban da sheƙi babu abin da take yi. Be san sanda ya sake lumshe idanunsa a karo na barkatai ba saboda wani irin ƙamshi da ya daki cikin hancinsa. Ya buɗe idanun a hankali yana kokawa da zuciyarsa. Hannunsa ya saka ya kamo hannunta cikin nasa. Se a lokacin sannan ta ɗaga kai a hankali ta kalle shi. Tana shirin janyewa ya girgiza kai yana faɗin
"A'ah.. kar ki janye don Allah.." Se ta ɗan runtse idanunta kawai tana buɗewa a kan fuskar tasa. Murmushi me ƙayatarwa ya sakar mata wanda ta ji shi har cikin zuciyarta. Se dai ta basar, daidai lokacin da ya soma faɗin
"Kin yi kyau.." Ya ƙare yana sake aza mata idanunsa. Yanzu kam ba ta san lokacin da ta janye idanun nata ba. Se ya yi murmushi yana faɗin
"Tashi mu je." Ya faɗa har lokacin be saki hannunta ba. Miƙewa ta yi har lokacin ba ta sake kuskuren kallansa ba. A haka har suka ƙarasa cikin ɗakin. Gefen gado ya ƙarasa ya zaunar da ita, yana cigaba da mamakin sauyawar Lulun gaba ɗaya. Kwata kwata ta sauya, ta zama kamar ba ita ba. Duk ta yi wani irin sanyi. Hannunta ya saki a nutse ya furta
"Ki na buƙatar wani abu ne?" Girgiza kai ta yi ba tare da tace komai ba.
"Bari na shiga wanka." Ya faɗa yana kallanta. Ba ta ɗauka yana buƙatar amsa ba ne. Se dai jin idanunsa a kanta ya sanyata ɗaga kai ta kalle shi. Se ya langaɓar da kai kamar wani maraya. Ba ta san lokacin da murmushi ya ɗan suɓuce a kan laɓɓanta ba. Da sauri ta jinjina kai.
Se a lokacin ya miƙe sosai kai tsaye toilet ya faɗa yana murmushi. Se ta samu kanta da binsa da kallo har ya shige toilet ɗin. Ta dawo da kanta cikin ɗakin tana sauke numfashi. Bayan shuɗewar wasu mintuna se ga shi ya fito. Kai tsaye wata tattausar jallabiyya mara nauyi ya ɗauka ya sanya. Se ya sake fitowa kamar balarabe ya yi kyau sosai. Musamman kuma da ya kasance kwantacciyar sumar kansa a buɗe take. A inda ya barta a nan ya sameta. Ya ƙarasa ya ɗan rusuna kaɗan yace
"Na haɗa miki ruwa.." A hankali ta miƙe tana gyara zaman mayafin jikinta. Ya kalleta yana jira ya ga me za ta yi next. Se ya ga tana ƙoƙarin yin hanyar toilet ɗin da duk kayan jikinta. Da sauri ya riƙo hannunta, wanda hakan ya sanyata juyowa.
"Ba dai da dukka kayan nan za ki shiga ba?" Ya tambaya yana bin duk jikinta da kallo. Duk se ta ji wani iri saboda kallan da ta ga yana binta da shi. Se ta yi saurin jinjina kai tace
"A'ah zan cire."
"Na sani.. Amma ya kamata ki rage daga nan." Girgiza kai ta yi bayan ta kalle shi. Ya bi narkakkiyar fuskarta da kallo, se ya yi murmushi dan tabbas ta ba shi dariya saboda yanda ta marairaice fuska kamar wadda za a yanka. Se kawai ya jinjina kai yana faɗin
"Toh je ki." Ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke tana wucewa toilet ɗin. Komawa ya yi ya nemi waje ya zauna. Gaba ɗaya baccin nan da yake ji tuni ya nemi nasa wajen. Ban da tsananin farin ciki babu abin da yake ji. Ta kwashe mintuna da yawa kafin ta fito daga ciki. Sanye da madaidaicin towel ta yafa mayafin jikinta. Tun da ta fito ta soma jin wani irin ƙamshi na tashi cikin ɗakin. A haka dai ƙamshin abinci ne me ɗan karen daɗi, se dai cikin lokaci ƙanƙani ƙamshin ya soma ɗaga mata hankali. Mazewa ta yi ta shiga takowa zuwa cikin ɗakin. Se dai duk taku ɗaya se ta ji ƙamshin na sake cika mata cikin hanci. Daidai lokacin da ta isa inda kayan da Mommah ta saka aka ɗinka musu haɗi da abayas da duk sauran kayan buƙata dai na mata ya shigo cikin ɗakin. Da sauri ta ɗaga kai ta kalle shi. Se kawai ta dakata ba tare da ta ɗauka ɗin ba. Daidai lokacin da ya ƙaraso. Hannu ya saka ya buɗe akwatin da ke kusa da shi ya ɗauko wata doguwar riga yana ɗagowa se ya ganta daf da toilet kamar za ta shige. Ya ɗauka ko ganinsa da ta yi ne ya sanya za ta koma cikin. Hakan ne ya sanya shi yin gaba ya yi saurin riƙota. Jan hannunta ta yi tana ƙoƙarin ƙwace jikinta saboda aman da ya taho mata saboda ƙamshin da kwata kwata be yi mata ba. Abin da shi kuma sam be fahimta ba. Dan kuwa riƙota ya sake yi da niyyar juyo da ita. Se kuwa ta shiga yi a jikinsa, duk yanda take ƙoƙarin riƙewa dan kar ta yi.
"Ya salaam.." Ya faɗa yana riƙe hannunta sosai. Ganin tana cigaba da yunƙuri ne ya sanya shi janta zuwa toilet ɗin. Hannu ya saka ya zame mayafin jikinta ya ajje shi gefe guda. Se kuwa ta cigaba da abinta a wahalce. Cike da tausayawa yake kallanta. Sosai ta wahala duk da yunƙurin ya fi aman da ta yi yawa. Taimaka mata ya yi yana riƙe da ita ta wanke bakinta. Kafin ya fito, kai tsaye kaya ya chanja. Babu jimawa se gata ta fito daga cikin toilet ɗin gaba ɗaya jikinta a sanyaye kamar mara lafiya. Da sauri ya miƙe ya ƙarasa ya riƙo hannunta.
"Sannu.." ya faɗa cike da tausayawa. Kawai jinjina kai ta yi dan da gaske wannan yunƙurin da ta yi duk ya wahalar da ita. Ashe haka Ammi ta sha wahala kafin ta haife su? Ta tambayi kanta idanunta na kawo ruwan hawaye. Ita mantawa ma ta yi towel ne kawai a jikinta. Haka ya kamata zuwa kan gadon ya zaunar.
... Washegari da sassafe me gyaran jikin da Mommah ta kirawo ta zo cikin gidan. Ɗaki guda aka ware musu cikin ƙanƙanin lokaci ta soma aikinta. Sosai yau ɗin Mommah ta bayar da wuta, dan so take komai dare a yau ta bawa kowa matarsa. Dan haka ta saka an gyara sashen da kowannensu ze zauna kafin a ƙarasa wanda Daddy ya sa aka fara ginawa. Dan tuni har ya ba da umarni an fara gina inda 'ya'yan nasa za su zauna. Da kuma wanda Ummeey da Abeey za su zauna ciki, amma su se sun dawo daga Makkah.
... Zaune yake cikin palourn hannunsa ɗauke da wani littafin addini yana karantawa. Wajen minti 10 se ya rufe littafin ya kalli tamfatsetsen agogon da ke manne a bangon ɗakin. Ƙarfe 9 daidai ya nuna. Ya ɗan lumshe idanunsa yana jin yanda bacci ke cin idanunsa. Qur'an ɗin da ke ajje a gabansa da wasu littafan ya ɗauka da niyyar shigewa ɗaki ya samu ya watsa ruwa ya kwanta. Sallamar Mommah da ya ji ita ce ta dakatar da shi, ya juya ya kalli bakin ƙofar lokaci ɗaya yana amsa sallamar. Tun kafin ya kai ƙarshen sallamar idanunsa suka sauka a kan Lulu da ke sanye cikin wata doguwar rigar atamfa. Mayafin da ya dace da atamfar saye saman ɗankwalin da ke zaune a kanta. Ta yi wani daƙiƙin kyau kamar ka saceta ka gudu.
Lumshe idanunsa ya yi yana buɗe su a kanta. Sam mantawa ma ya yi tare da Mommah ne suke tare, har se da ya ji muryar Mommah tace
"Toh zauna koh?" Se a lokacin ya tuna a inda yake, ya yi saurin basarwa yana ƙaƙalo murmushi ya nemi waje ya zauna jiki a sanyaye. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke kafin yace
"Mommah.." Ya yi maganar yana iya ƙoƙarinsa wajen ganin be kalli Lulu ba. Lulun da ke zaune gefen Mommah kanta a ƙasa kamar munafuka.
"Na'am.." Mommah ta amsa da hakan tana murmushi. Shiru ne ya wanzu na tsawon lokaci. Shi dai Gwani jira kawai yake ya ji me ye ya kawo Mommah da Lulun cikin ɗakin? Musamman da tun ganinta da ya yi duk baccin da yake ji ya tafi. A hankali Mommah ta soma faɗin
"Areef.."
"Na'am Mommah." Ya amsa da hakan yana ɗaga kai ya kalleta. Se ta cigaba da faɗin
"Ga Afaaf nan na dawo maka da ita.. Ba na jinka in Sha Allah.. Se dai duk da haka ina me roƙonka da ka riƙeta amana. Ka kuma kula da ita gwargwadon iyawarka." Be san sanda ya lumshe idanunsa ba, yana jin wani irin farin ciki na ratsa shi. Kenan idan dai har ya fahimci zancen Mommahn tana nufin ta dawo masa da matarsa kenan?
"In Sha Allah Mommah ba za ki kuka da ni ba.. Na gode Allah Ya ƙara girma."
"Ameen.." Mommah ta faɗa tana murmushi, daidai lokacin da ta maida dubanta kan Lulu. Babu buƙatar yi mata faɗa ko wata maganar, dan duk wani abu da ya kamata ta faɗa mata ta faɗa musu tun kafin su fito. Dan haka kawai hannunta ta kamo tace a hankali
"Bari na wuce Daughter.." Se a lokacin sannan Lulu ta ɗaga kai ta kalli Mommah cikin sanyin murya kamar Didi tace
"Tohm." Daga haka ba ta sake cewa komai ba. Ita ma Mommahn ba tace komai ba se ficewa daga ɗakin da ta yi. A hankali ya ɗaga kansa ya kalli Lulu da ta cigaba da zama a kan kujerar tana wasa da yatsun hannunta. Miƙewa ya yi a nutse ya koma ya zauna a kan kujerar da take kai. Yanda ta yi ƙasa da kai hakan ba ƙaramin ba shi damar kallanta ya yi ba. Ya ƙura mata ido kamar wanda ya soma ganinta yau. Se ya ga yau ɗin ta sake wani irin kyau, ta sake murjewa, farar fatar jikinta ta yi fresh ban da sheƙi babu abin da take yi. Be san sanda ya sake lumshe idanunsa a karo na barkatai ba saboda wani irin ƙamshi da ya daki cikin hancinsa. Ya buɗe idanun a hankali yana kokawa da zuciyarsa. Hannunsa ya saka ya kamo hannunta cikin nasa. Se a lokacin sannan ta ɗaga kai a hankali ta kalle shi. Tana shirin janyewa ya girgiza kai yana faɗin
"A'ah.. kar ki janye don Allah.." Se ta ɗan runtse idanunta kawai tana buɗewa a kan fuskar tasa. Murmushi me ƙayatarwa ya sakar mata wanda ta ji shi har cikin zuciyarta. Se dai ta basar, daidai lokacin da ya soma faɗin
"Kin yi kyau.." Ya ƙare yana sake aza mata idanunsa. Yanzu kam ba ta san lokacin da ta janye idanun nata ba. Se ya yi murmushi yana faɗin
"Tashi mu je." Ya faɗa har lokacin be saki hannunta ba. Miƙewa ta yi har lokacin ba ta sake kuskuren kallansa ba. A haka har suka ƙarasa cikin ɗakin. Gefen gado ya ƙarasa ya zaunar da ita, yana cigaba da mamakin sauyawar Lulun gaba ɗaya. Kwata kwata ta sauya, ta zama kamar ba ita ba. Duk ta yi wani irin sanyi. Hannunta ya saki a nutse ya furta
"Ki na buƙatar wani abu ne?" Girgiza kai ta yi ba tare da tace komai ba.
"Bari na shiga wanka." Ya faɗa yana kallanta. Ba ta ɗauka yana buƙatar amsa ba ne. Se dai jin idanunsa a kanta ya sanyata ɗaga kai ta kalle shi. Se ya langaɓar da kai kamar wani maraya. Ba ta san lokacin da murmushi ya ɗan suɓuce a kan laɓɓanta ba. Da sauri ta jinjina kai.
Se a lokacin ya miƙe sosai kai tsaye toilet ya faɗa yana murmushi. Se ta samu kanta da binsa da kallo har ya shige toilet ɗin. Ta dawo da kanta cikin ɗakin tana sauke numfashi. Bayan shuɗewar wasu mintuna se ga shi ya fito. Kai tsaye wata tattausar jallabiyya mara nauyi ya ɗauka ya sanya. Se ya sake fitowa kamar balarabe ya yi kyau sosai. Musamman kuma da ya kasance kwantacciyar sumar kansa a buɗe take. A inda ya barta a nan ya sameta. Ya ƙarasa ya ɗan rusuna kaɗan yace
"Na haɗa miki ruwa.." A hankali ta miƙe tana gyara zaman mayafin jikinta. Ya kalleta yana jira ya ga me za ta yi next. Se ya ga tana ƙoƙarin yin hanyar toilet ɗin da duk kayan jikinta. Da sauri ya riƙo hannunta, wanda hakan ya sanyata juyowa.
"Ba dai da dukka kayan nan za ki shiga ba?" Ya tambaya yana bin duk jikinta da kallo. Duk se ta ji wani iri saboda kallan da ta ga yana binta da shi. Se ta yi saurin jinjina kai tace
"A'ah zan cire."
"Na sani.. Amma ya kamata ki rage daga nan." Girgiza kai ta yi bayan ta kalle shi. Ya bi narkakkiyar fuskarta da kallo, se ya yi murmushi dan tabbas ta ba shi dariya saboda yanda ta marairaice fuska kamar wadda za a yanka. Se kawai ya jinjina kai yana faɗin
"Toh je ki." Ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke tana wucewa toilet ɗin. Komawa ya yi ya nemi waje ya zauna. Gaba ɗaya baccin nan da yake ji tuni ya nemi nasa wajen. Ban da tsananin farin ciki babu abin da yake ji. Ta kwashe mintuna da yawa kafin ta fito daga ciki. Sanye da madaidaicin towel ta yafa mayafin jikinta. Tun da ta fito ta soma jin wani irin ƙamshi na tashi cikin ɗakin. A haka dai ƙamshin abinci ne me ɗan karen daɗi, se dai cikin lokaci ƙanƙani ƙamshin ya soma ɗaga mata hankali. Mazewa ta yi ta shiga takowa zuwa cikin ɗakin. Se dai duk taku ɗaya se ta ji ƙamshin na sake cika mata cikin hanci. Daidai lokacin da ta isa inda kayan da Mommah ta saka aka ɗinka musu haɗi da abayas da duk sauran kayan buƙata dai na mata ya shigo cikin ɗakin. Da sauri ta ɗaga kai ta kalle shi. Se kawai ta dakata ba tare da ta ɗauka ɗin ba. Daidai lokacin da ya ƙaraso. Hannu ya saka ya buɗe akwatin da ke kusa da shi ya ɗauko wata doguwar riga yana ɗagowa se ya ganta daf da toilet kamar za ta shige. Ya ɗauka ko ganinsa da ta yi ne ya sanya za ta koma cikin. Hakan ne ya sanya shi yin gaba ya yi saurin riƙota. Jan hannunta ta yi tana ƙoƙarin ƙwace jikinta saboda aman da ya taho mata saboda ƙamshin da kwata kwata be yi mata ba. Abin da shi kuma sam be fahimta ba. Dan kuwa riƙota ya sake yi da niyyar juyo da ita. Se kuwa ta shiga yi a jikinsa, duk yanda take ƙoƙarin riƙewa dan kar ta yi.
"Ya salaam.." Ya faɗa yana riƙe hannunta sosai. Ganin tana cigaba da yunƙuri ne ya sanya shi janta zuwa toilet ɗin. Hannu ya saka ya zame mayafin jikinta ya ajje shi gefe guda. Se kuwa ta cigaba da abinta a wahalce. Cike da tausayawa yake kallanta. Sosai ta wahala duk da yunƙurin ya fi aman da ta yi yawa. Taimaka mata ya yi yana riƙe da ita ta wanke bakinta. Kafin ya fito, kai tsaye kaya ya chanja. Babu jimawa se gata ta fito daga cikin toilet ɗin gaba ɗaya jikinta a sanyaye kamar mara lafiya. Da sauri ya miƙe ya ƙarasa ya riƙo hannunta.
"Sannu.." ya faɗa cike da tausayawa. Kawai jinjina kai ta yi dan da gaske wannan yunƙurin da ta yi duk ya wahalar da ita. Ashe haka Ammi ta sha wahala kafin ta haife su? Ta tambayi kanta idanunta na kawo ruwan hawaye. Ita mantawa ma ta yi towel ne kawai a jikinta. Haka ya kamata zuwa kan gadon ya zaunar.