Sashe 43
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki nutsu ko na saɓa miki.." Ya ƙare yana murmushi a fili.
I zuwa lokacin kam Nurse ɗin ba ta sake cewa komai ba dan ita ta ɗauka wani abun soyayyar ya faɗa mata. Se ta ɗauke kai tana ƙarasa haɗa allurar jikinta a matuƙar sanyaye. Tana daga jikinsa ita kuma Nurse ɗin ta ƙaraso ta yi mata allurar har lokacin ba ta sake cewa komai ba. Ƙanƙame shi ta yi ba tare da ta sani ba lokacin da ta ji shigar tsinin allurar cikin jikinta. Kamar gaske ya zagayo da hannunsa ta bayanta yana faɗin
"Oh sorry babe.." Ya yi maganar irin kamar cikin tausayawar nan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO46*
___Cikin sakannin da ba su wuce 60 ba Nurse ɗin ta fice daga cikin ɗakin ba tare da tace komai ba. Ita kam Didi ko jin abin da ya faɗa ma ba ta yi ba saboda yanda hankalinta gaba ɗaya ke kan yanda za ta ƙwace jikinta daga nasa. Lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi sakin Didi da ɗan ƙarfi. Har se da hakan ya sa ta yi taga taga kamar za ta faɗi se kuma ta dawo ta tsaya a kan ƙafafunta. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana ɗan lumshe idanunsa na tsawon second 10 kafin ya buɗe. Ba tare da ya kalleta ba yace lokacin da ya fara takawa dan ficewa daga cikin ɗakin
"Kar ki ɓata min lokaci, ki fito.." Daga haka ba tare da ya jira amsar da za ta ba shi ba ba ya fice daga ɗakin. Hannu ta kai wajen allurar ta dafe tana jin yanda wajen ke mata zugi. Ta ja sheshsheƙa kamar wadda ta yi kuka sannan ta soma takawa dan bin bayansa. Se a lokacin abin da ya faru ya dawo mata. An ya kuwa lafiyarsa ƙalau? Me ye ya shiga kansa ɗazun be tashi sauka ba se yanzu? Har ta isa inda motarsa take ba ta dena jin zafin allurar ba kawai mazewa take yi. Lokacin da ta isa har ya shige cikin motar yana shirin tayarwa. Ta yi saurin buɗe murfin motar ta shige a inda ta zauna ɗazun. Shiru ya yi lokacin da ya ji zamanta a gidan bayan. Shi se yanzu ne ma ya tuna a inda ta zauna ɗazun, saboda yanda yake a fusace be ma lura ba.
"Kee!!" Ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. Kamar ba za ta ɗaga kai ba dan ita ta ƙafarta take da inda aka mata allura. Se dai ta san tabbas da ita yake tunda babu kowa cikin motar daga shi se ita. Hakan ne ya sanyata ɗaga kai kawai.
"Waye sa'anki? Waye drivernki?" Tun kafin ya kai ƙarshen maganar ta buɗe murfin motar ta fito ta shige gaba. Kamar wancan karon haka ta kame kanta waje guda in case ma ka da ta yi wani abun yace ta yi.
... "Mami don Allah ki zauna.." Jadwa ta faɗa tana kallanta.
"Rabu da ni Jadwa.. ki bar ni. Na kasa mantawa da cin mutuncin da Lulu da wancan mijin nata suka min. Har ni Sadiya za a cewa na fita na bar waje?" Ta yi maganar tana jin zafin hakan har cikin ranta.
"Ki yi haƙuri ki manta kawai. Lokaci ya yi da za ki cire hannunki a kan al'amuran Lulu. Ni da ma tun da na ga kina ta shishshigewa na janye jikina saboda gudun yarfi."
"Uhmm ai ba a taɓa ci min mutunci irin wannan ba." In ji Mami tana girgiza kai.
"Mami wai kuma wannan ɗin nan da muka gani shi ne mijin Sister Lulu? Na ji kina kwatanta shi da wani banzan mutum. Ni wallahi ba dan abin da kike faɗa ba ba zan yadda ba daga gidan arziƙi ya fito ba. Saboda kalar shigarsa da kyawunsa wallahi da farko na ɗauka wani balaraben ne fa.. se da na ji ya yi magana.."
"Dallah can.. shashashar banza shashashar wofi.. ke dai kin shiga 3 idonki idon maza. Kowa kika gani se kin yaba shi. Me ye haka ne Jadwa? An ya kuwa?" Mami ta ƙare tana kallanta sosai. Hararar gefe Jadwa ta yi tana ɗauke kai lokaci ɗaya tana huhhura hanci ita a lallai dole maganar Mamin ta ɓata mata rai. Fahimtar hakan da Mami ta yi ne ya sanya ta faɗin
"Naa ji amma dai ba ki na nufin kin dawo daga rakiyar Kaseem ba ne koh?"
"A'ah ni kam ba haka nake nufi ba. Ai ke ce ba ki tsaya kin ji ƙarshen maganar tawa ba." Ta ƙare tana tura baki.
"Toh shi kenan ya wuce.. Mu koma kan abin da ze fishshe mu."
... A ɗaya ɓangaren kuwa tana zaune a kan gadon jingine jikin bango tana tunanin yanda rayuwarsu ita da er uwatta ta sauya cikin lokaci ƙanƙani. Ba ta ji shigowarsa ba dan ko sallamarsa ma ba ta ji ba saboda yanda ta yi zurfi cikin tunani. Se gyaran murya kawai ta ji, hakan ne ya sanya ta buɗe ido da sauri. Idanunta da suka sauka cikin nasa ta yi saurin janyewa.
"Wace ce ita?" Ya tambaya still yana kallanta. Kamar ta yi shiru se kuma ta ji ba za ta iya hakan ba, dan haka ta buɗe baki a hankali tace
"Ƙanwar Abba ce.."
"Ƙanwar Abba?" Ya ƙare da alamar tambaya. Se dai be jira ta ba shi amsa ba ya ɗora da wata tambayar
"Amma me ya sa kika mata haka?"
"Ba komai.." ta faɗa tana taɓe fuska dan har lokacin ranta babu daɗi. Girgiza kai ya yi yana ɗan lumshe idanunsa kafin ya buɗe baki yace
"Ba haka ba ne.. akwai dai wani abun.."
"Babu.." ta ba shi amsa a gajarce
"Toh kuwa zan barta ta cigaba da zuwa wajenki.." Daga haka ya juya dan barin wajen. Da sauri ta kalle shi, ganin ba shi da niyyar tsayawa ya sanyata faɗin
"Da ta ga hoton nan ne fa ta nuna jin daɗinta.." Abin da ya ji ta faɗa ne ya sanya shi dakatawa cike da mamaki. An ya kuwa da gaske take yi? Ko dai ta faɗi hakan ne dan kare kanta? Ƙanwar mahaifinta fa? Toh idan kuma haka ɗin ne me ye dalilin da ze sa ta ji daɗin gani hoton? Akwai wani dalili kuwa? Toh ko dai duk dan hakan ya zama sanadiyyar rabuwar aurensu ne? Dan ya lura tun farkon ganinta ba son shi take yi ba. Shi haka nan ma kawai ya ji ba ta kwanta masa a rai ba ko kaɗan. Duk shi kaɗai yake tsara hakan cikin ransa har kuma lokacin be juyo ba. Se da ya gama saƙe saƙen sannan ya juyo ya kalleta.
"An ya kuwa?" Ya tambaya dan sake tabbatarwa. Se kawai ta jinjina kai tana sake tuna lokacin da suke magana da Mamin a kan hoton. Se ya jinjina kai yana sauke numfashi har lokacin ya kasa dena mamakin abin da ta faɗa ɗin.
A ranar aka sallami Lulu daga asibitin. Bayan dawowar Ummeey suka suka shirya komai se gida..
.. A ɗaya ɓangaren kuwa babu daɗewa suka isa gida. Yana gama parking ɗin motar ba ta jira komai ba ta fice daga ciki. Daidai lokacin da take sauka daga cikin motar idanun Mom suka sauka a kanta. Se ta buɗe idanu sosai tana kallan wanda ze fito daga cikin motar. Bayan wasu sakanni se ga Bad Man ya fito daga cikin motar hannunsa saye cikin aljihunsa da ya jefa key ɗin motar a ciki.
"Na shiga 3.." Mom ta faɗa tana maida dubanta kan Didi da ta kusa ƙarasowa inda take. Tun da Didi ta hangota ta ji faɗuwar gaba ta ziyarceta, ita ta rasa dalilin da ya sa take shakkar matar. Idan ta ganta kamar wadda ta ga sheɗan, ta dinga janyo duk wata addu'a da ta zo bakinta kenan. Haka dai ta daure ta cije lokacin da ta iso wajen Mom ɗin, ta tsugunna a nutse tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka da lokacin uwarwa? Ke.. ni za ki asircewa ɗa? Toh wuce ki je sashena ki jira ni gani nan zuwa za ki gane kurenki.." Mom ta faɗa a fusace. Sauke numfashi Didi ta yi kawai se ta miƙe cikin nutsuwar nan tata, ta shiga karanto duk addu'ar da ta zo cikin bakinta kamar kodayaushe ta yi gaba jiki a sanyaye.
Murmushi ya sakarwa Mom ɗin tasa lokacin da ya ƙaraso inda take, yana shirin yi mata magana tace
"Kar ka ce min komai Boy.. Ba na buƙatar jin komai daga bakinka.. Abin da nake son ji kawai shi ne me ya kai yarinyar can cikin motarka?" Tsayawa ya yi yana kallan Mom ɗin cike da mamakin tambayar da ta fito daga bakinta. Ya ɗauka ko wata ce ze iya ɗaukarta cikin mota ba tare da wani abun ba. Ballantana wadda Daddy da kansa ya masa umarni da ya ɗauketa dan tana matsayin matar da ya aura masa? Ko tana zarginsa ne?
"Mom.." ya faɗa muryarsa a ɗan kaurare.
"Ka ba ni amsa kawai.. ka fara biyewa waccan munafukar matar ne ka na so ka bijire min? Areef ko ka manta wace ce ni? Ka manta abin da na faɗa maka? Ba na son auren kuma ba na son matar? Ba ka tsoron Allah ya kamaka? Me ya kai ka ɗaukarta cikin motarka? An ya kuwa Areef?"
"Wai Mom hakan na da zunubi ne?" Ya katse Mom da faɗin hakan a ƙage fuskarsa na nuna hakan. Saboda yanda ya ƙagu ta kai ƙarshen maganar tata amma ta ƙi katseta se ma nunawa da take yi kamar ya aikata wani babban saɓo ne..
A yi manage da wannan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO47*
___Tsayawa Mom ta yi tana kallan Bad Man sosai kamar me nazarin abin da ya gama faɗa ɗin. Anya kuwa shi ne a gabanta? Me yake shirin faruwa ne? Se da ta ɗan ja numfashi kaɗan kamin tace
"Areef.." Kamar ba ze amsa ba, se kuma ya buɗe baki a daƙile yace
"Yes Mom.." Iska ta sake fesarwa daga bakinta sannan tace
"Shi kenan.. mu je ciki mu yi magana.." Girgiza kai ya yi dan har ga Allah be ji daɗin yanda Mom ɗin ta titsiye shi haka tana ta masa tambayoyi ba.
"Mom ina so na wuce.."
I zuwa lokacin kam Nurse ɗin ba ta sake cewa komai ba dan ita ta ɗauka wani abun soyayyar ya faɗa mata. Se ta ɗauke kai tana ƙarasa haɗa allurar jikinta a matuƙar sanyaye. Tana daga jikinsa ita kuma Nurse ɗin ta ƙaraso ta yi mata allurar har lokacin ba ta sake cewa komai ba. Ƙanƙame shi ta yi ba tare da ta sani ba lokacin da ta ji shigar tsinin allurar cikin jikinta. Kamar gaske ya zagayo da hannunsa ta bayanta yana faɗin
"Oh sorry babe.." Ya yi maganar irin kamar cikin tausayawar nan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO46*
___Cikin sakannin da ba su wuce 60 ba Nurse ɗin ta fice daga cikin ɗakin ba tare da tace komai ba. Ita kam Didi ko jin abin da ya faɗa ma ba ta yi ba saboda yanda hankalinta gaba ɗaya ke kan yanda za ta ƙwace jikinta daga nasa. Lura da hakan da ya yi ne ya sanya shi sakin Didi da ɗan ƙarfi. Har se da hakan ya sa ta yi taga taga kamar za ta faɗi se kuma ta dawo ta tsaya a kan ƙafafunta. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana ɗan lumshe idanunsa na tsawon second 10 kafin ya buɗe. Ba tare da ya kalleta ba yace lokacin da ya fara takawa dan ficewa daga cikin ɗakin
"Kar ki ɓata min lokaci, ki fito.." Daga haka ba tare da ya jira amsar da za ta ba shi ba ba ya fice daga ɗakin. Hannu ta kai wajen allurar ta dafe tana jin yanda wajen ke mata zugi. Ta ja sheshsheƙa kamar wadda ta yi kuka sannan ta soma takawa dan bin bayansa. Se a lokacin abin da ya faru ya dawo mata. An ya kuwa lafiyarsa ƙalau? Me ye ya shiga kansa ɗazun be tashi sauka ba se yanzu? Har ta isa inda motarsa take ba ta dena jin zafin allurar ba kawai mazewa take yi. Lokacin da ta isa har ya shige cikin motar yana shirin tayarwa. Ta yi saurin buɗe murfin motar ta shige a inda ta zauna ɗazun. Shiru ya yi lokacin da ya ji zamanta a gidan bayan. Shi se yanzu ne ma ya tuna a inda ta zauna ɗazun, saboda yanda yake a fusace be ma lura ba.
"Kee!!" Ya faɗa ba tare da ya kalleta ba. Kamar ba za ta ɗaga kai ba dan ita ta ƙafarta take da inda aka mata allura. Se dai ta san tabbas da ita yake tunda babu kowa cikin motar daga shi se ita. Hakan ne ya sanyata ɗaga kai kawai.
"Waye sa'anki? Waye drivernki?" Tun kafin ya kai ƙarshen maganar ta buɗe murfin motar ta fito ta shige gaba. Kamar wancan karon haka ta kame kanta waje guda in case ma ka da ta yi wani abun yace ta yi.
... "Mami don Allah ki zauna.." Jadwa ta faɗa tana kallanta.
"Rabu da ni Jadwa.. ki bar ni. Na kasa mantawa da cin mutuncin da Lulu da wancan mijin nata suka min. Har ni Sadiya za a cewa na fita na bar waje?" Ta yi maganar tana jin zafin hakan har cikin ranta.
"Ki yi haƙuri ki manta kawai. Lokaci ya yi da za ki cire hannunki a kan al'amuran Lulu. Ni da ma tun da na ga kina ta shishshigewa na janye jikina saboda gudun yarfi."
"Uhmm ai ba a taɓa ci min mutunci irin wannan ba." In ji Mami tana girgiza kai.
"Mami wai kuma wannan ɗin nan da muka gani shi ne mijin Sister Lulu? Na ji kina kwatanta shi da wani banzan mutum. Ni wallahi ba dan abin da kike faɗa ba ba zan yadda ba daga gidan arziƙi ya fito ba. Saboda kalar shigarsa da kyawunsa wallahi da farko na ɗauka wani balaraben ne fa.. se da na ji ya yi magana.."
"Dallah can.. shashashar banza shashashar wofi.. ke dai kin shiga 3 idonki idon maza. Kowa kika gani se kin yaba shi. Me ye haka ne Jadwa? An ya kuwa?" Mami ta ƙare tana kallanta sosai. Hararar gefe Jadwa ta yi tana ɗauke kai lokaci ɗaya tana huhhura hanci ita a lallai dole maganar Mamin ta ɓata mata rai. Fahimtar hakan da Mami ta yi ne ya sanya ta faɗin
"Naa ji amma dai ba ki na nufin kin dawo daga rakiyar Kaseem ba ne koh?"
"A'ah ni kam ba haka nake nufi ba. Ai ke ce ba ki tsaya kin ji ƙarshen maganar tawa ba." Ta ƙare tana tura baki.
"Toh shi kenan ya wuce.. Mu koma kan abin da ze fishshe mu."
... A ɗaya ɓangaren kuwa tana zaune a kan gadon jingine jikin bango tana tunanin yanda rayuwarsu ita da er uwatta ta sauya cikin lokaci ƙanƙani. Ba ta ji shigowarsa ba dan ko sallamarsa ma ba ta ji ba saboda yanda ta yi zurfi cikin tunani. Se gyaran murya kawai ta ji, hakan ne ya sanya ta buɗe ido da sauri. Idanunta da suka sauka cikin nasa ta yi saurin janyewa.
"Wace ce ita?" Ya tambaya still yana kallanta. Kamar ta yi shiru se kuma ta ji ba za ta iya hakan ba, dan haka ta buɗe baki a hankali tace
"Ƙanwar Abba ce.."
"Ƙanwar Abba?" Ya ƙare da alamar tambaya. Se dai be jira ta ba shi amsa ba ya ɗora da wata tambayar
"Amma me ya sa kika mata haka?"
"Ba komai.." ta faɗa tana taɓe fuska dan har lokacin ranta babu daɗi. Girgiza kai ya yi yana ɗan lumshe idanunsa kafin ya buɗe baki yace
"Ba haka ba ne.. akwai dai wani abun.."
"Babu.." ta ba shi amsa a gajarce
"Toh kuwa zan barta ta cigaba da zuwa wajenki.." Daga haka ya juya dan barin wajen. Da sauri ta kalle shi, ganin ba shi da niyyar tsayawa ya sanyata faɗin
"Da ta ga hoton nan ne fa ta nuna jin daɗinta.." Abin da ya ji ta faɗa ne ya sanya shi dakatawa cike da mamaki. An ya kuwa da gaske take yi? Ko dai ta faɗi hakan ne dan kare kanta? Ƙanwar mahaifinta fa? Toh idan kuma haka ɗin ne me ye dalilin da ze sa ta ji daɗin gani hoton? Akwai wani dalili kuwa? Toh ko dai duk dan hakan ya zama sanadiyyar rabuwar aurensu ne? Dan ya lura tun farkon ganinta ba son shi take yi ba. Shi haka nan ma kawai ya ji ba ta kwanta masa a rai ba ko kaɗan. Duk shi kaɗai yake tsara hakan cikin ransa har kuma lokacin be juyo ba. Se da ya gama saƙe saƙen sannan ya juyo ya kalleta.
"An ya kuwa?" Ya tambaya dan sake tabbatarwa. Se kawai ta jinjina kai tana sake tuna lokacin da suke magana da Mamin a kan hoton. Se ya jinjina kai yana sauke numfashi har lokacin ya kasa dena mamakin abin da ta faɗa ɗin.
A ranar aka sallami Lulu daga asibitin. Bayan dawowar Ummeey suka suka shirya komai se gida..
.. A ɗaya ɓangaren kuwa babu daɗewa suka isa gida. Yana gama parking ɗin motar ba ta jira komai ba ta fice daga ciki. Daidai lokacin da take sauka daga cikin motar idanun Mom suka sauka a kanta. Se ta buɗe idanu sosai tana kallan wanda ze fito daga cikin motar. Bayan wasu sakanni se ga Bad Man ya fito daga cikin motar hannunsa saye cikin aljihunsa da ya jefa key ɗin motar a ciki.
"Na shiga 3.." Mom ta faɗa tana maida dubanta kan Didi da ta kusa ƙarasowa inda take. Tun da Didi ta hangota ta ji faɗuwar gaba ta ziyarceta, ita ta rasa dalilin da ya sa take shakkar matar. Idan ta ganta kamar wadda ta ga sheɗan, ta dinga janyo duk wata addu'a da ta zo bakinta kenan. Haka dai ta daure ta cije lokacin da ta iso wajen Mom ɗin, ta tsugunna a nutse tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka da lokacin uwarwa? Ke.. ni za ki asircewa ɗa? Toh wuce ki je sashena ki jira ni gani nan zuwa za ki gane kurenki.." Mom ta faɗa a fusace. Sauke numfashi Didi ta yi kawai se ta miƙe cikin nutsuwar nan tata, ta shiga karanto duk addu'ar da ta zo cikin bakinta kamar kodayaushe ta yi gaba jiki a sanyaye.
Murmushi ya sakarwa Mom ɗin tasa lokacin da ya ƙaraso inda take, yana shirin yi mata magana tace
"Kar ka ce min komai Boy.. Ba na buƙatar jin komai daga bakinka.. Abin da nake son ji kawai shi ne me ya kai yarinyar can cikin motarka?" Tsayawa ya yi yana kallan Mom ɗin cike da mamakin tambayar da ta fito daga bakinta. Ya ɗauka ko wata ce ze iya ɗaukarta cikin mota ba tare da wani abun ba. Ballantana wadda Daddy da kansa ya masa umarni da ya ɗauketa dan tana matsayin matar da ya aura masa? Ko tana zarginsa ne?
"Mom.." ya faɗa muryarsa a ɗan kaurare.
"Ka ba ni amsa kawai.. ka fara biyewa waccan munafukar matar ne ka na so ka bijire min? Areef ko ka manta wace ce ni? Ka manta abin da na faɗa maka? Ba na son auren kuma ba na son matar? Ba ka tsoron Allah ya kamaka? Me ya kai ka ɗaukarta cikin motarka? An ya kuwa Areef?"
"Wai Mom hakan na da zunubi ne?" Ya katse Mom da faɗin hakan a ƙage fuskarsa na nuna hakan. Saboda yanda ya ƙagu ta kai ƙarshen maganar tata amma ta ƙi katseta se ma nunawa da take yi kamar ya aikata wani babban saɓo ne..
A yi manage da wannan..
MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO47*
___Tsayawa Mom ta yi tana kallan Bad Man sosai kamar me nazarin abin da ya gama faɗa ɗin. Anya kuwa shi ne a gabanta? Me yake shirin faruwa ne? Se da ta ɗan ja numfashi kaɗan kamin tace
"Areef.." Kamar ba ze amsa ba, se kuma ya buɗe baki a daƙile yace
"Yes Mom.." Iska ta sake fesarwa daga bakinta sannan tace
"Shi kenan.. mu je ciki mu yi magana.." Girgiza kai ya yi dan har ga Allah be ji daɗin yanda Mom ɗin ta titsiye shi haka tana ta masa tambayoyi ba.
"Mom ina so na wuce.."