Sashe 64
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki ɗan ba ni waje." Ya faɗawa Talatuwa da ta yi kane kane ta kasa matsawa ko ina daga jikin Maimunan. Ban da kuka babu abin da take yi tamkar ƙaramar yarinyar goye. Se a lokacin ta iya miƙewa ta matsa gefe tana share hawayen fuskar tata. Ya yin da shi kuma likitan kai tsaye ya shiga dubata cikin ƙwarewa.
.. "Ki yi haƙuri In Sha Allah komai ze daidaita. Za kuma ta samu sauƙi da yaddar me sama." Gwaggo ta faɗa tana kallan Talatuwa. Jinjina kai Ammi ta yi kafin a nutse ta ɗora da
"In Sha Allah.." Hannu Talatuwa ta kai ta goge fuskarta kafin tace
"Ina fatan haka ni ma. Amma yanda suka fita da ita ne ya ba ni tsoro."
"Babu damuwa hakan ma. Ke dai kawai ki fawwalawa Allah." Ba ta iya amsawa ba se ɗaga kai da ta yi. Shiru ne ya wanzu a wajen na en mintuna kowa da abin da yake tunani. Kafin daga bisani Gwaggo ta kalli Ammi tace
"Goben za ki wuce Fatima?" Kallan Gwaggo Ammi ta yi tana ji kamar tace a'ah, dan duk da Gwaggon ba ita ta haifeta ba amma tana ganinta ne kamar tata mahaifiyar da ba ta raye. Se dai kuma ta riga ta faɗawa Abba adadin kwanakin da za ta yi. Ba kuma ta so ta saɓa hakan. Don haka tace
"Ehh.. mun yi magana da Maryam tana nan tahowa a goben."
"Toh shi kenan babu matsala. Allah Ya kai mu." Tun da suka soma magana Talatuwa ke kallansu, har zuwa lokacin da suka gama. Se ta sauka daga kan kujerar da take ta ƙarasa zuwa wadda Ammi take. Hannu ta saka ta kamo hannun Ammin daidai lokacin da hawaye suka cika idanunta tace
"Don Allah.. ba don halinmu ba, ki taimaka ki bari kar ki tafi har se Maimuna ta farka. Duk wasu alamomi sun nuna tana son magana da ke ne. Ban sani ba ko ta sanki ne ko ke kin santa tuntuni. Don Allah ki mana wannan alfarmar Hajiya." Shiru Ammi ta yi tana kallanta dan ba ta san me za tace ba.
"Ki na ganin kin san fuskarta ne?" Gwaggo ta yi maganar tana kallan Ammi. Girgiza kai Ammi ta yi, tana tunanin ko ta santa ɗin ne. Se dai kuma duk wani tunaninta ita dai ba ta san Maimunan ba. Hasalima ba ta taɓa ganinta ba se zuwansu asibitin.
"Ikon Allah! Toh kuma ba ta taɓa faɗa miki wata magana da za ta saka yanzu ki kawo ko tana da alaƙa da abin da ya faru ɗazun." Gwaggo ta faɗa tana kallan Talatuwa.
"Wallahi ba ta taɓa ba. Abin da kawai zan ce cikin shekarun baya gaskiya ta haɗu da ciwon damuwa. Don haka kawai za ta zauna ta yi ta tunani kamar me iskokai. Komai tunani komai tunani. Shi ne dai daga ƙarshe aka ce mana ciwon damuwa ne. Kuma na yi na yi ta faɗa min abin da ke damunta ta ƙi. Wallahi daga haka dai ciwo ya din ga tafiya. Daga wannan lalurar se wannan. Har dai aka zo kan wannan na shanyewar jikin." Talatuwa ta ƙare a sanyaye. Ita dai Ammi har lokacin ba ta sake cewa komai ba tun bayan amsar da ta baiwa Gwaggo. Har zuwa lokacin da Gwaggon ta sake faɗin
"Ki yi haƙuri Fatima. Ki ba ni wayar da kaina zan masa bayanin abin da ya faru, wanda ze hanaki komawa. Duk da na san halin Muhammadu mutumin kirki ne." Murmushi Ammi ta yi kafin tace
"Toh Gwaggo."
.. A nutse ya tura ƙofar ɗakin da sallama ɗauke a bakinsa. Sanye yake cikin wata tattausar farar jallabiyya. Kansa babu komai yanzu haka. Se gyarararriyar sumar kan nan nasa da kuka sani a waje. Hakan ba ƙaramin kyau ya yi ba. A nutse ya ƙarasa ya nemi kan gadon ya zauna. Tana ganin haka ta ɗauke kai ta juya wani ɓangaren tana wasa da gefen hijab ɗinta. A nutse ya ɗaga idanunsa ya kalleta na tsawon second 10 kafin ya ɗauke idanunsa daga kanta.
"Afaaf.." Ya kira sunanta kai tsaye yana maida dubansa kanta. Idan da ita wata ce a yanda ya yi magana kaɗai ya isa ya nuna mata magana me muhimmanci yake son yi da ita. Amma ita ba ma ta fahimci hakan ba. Se kawar da kai da ta sake yi tana turo baki gefe guda kuma zuciyarta na neman karyewa. Dan ita yanzu sam ba ta so ta gansu waje ɗaya. Da da dama ma tashi za ta yi ta bar masa wajen, se dai kuma yanzu ta san halinsa ƙaramin aikinsa ne ya kamota. Jin da ya yi ta yi shiru ne ya sanya shi lumshe idanunsa a kan laɓɓansa ya furta
"Se yaushe ne..?" A fili kuma se ya yi amfani da hannunsa wajen lalubo inda nata hannun yake ya sanya shi cikin nasa ya riƙe da duka biyun. Da sauri ta juyo da niyyar ƙwacewa. Se dai a yanda ya zuba mata narkakkun idanunsa, se ta ga kallan da yake mata a kwanakin nan ba irin wannan ba ne. Dan yanzun se ta ga yana neman rikiɗe mata ya koma Gwani na can baya. Gwani Affan Ya mu'allim ɗin Islamiyyarsu. Dalilin kenan da ya sanya ta yi maza ta janye idanunta da ke wani girgiɗi.
"Ki nutsu.. ki kalle ni da kyau.. ki kuma faɗa min gaskiya." Ya faɗa sanda ya lura ba ta haƙura ba tana cigaba da neman ƙwace hannayenta ne.
"Gaskiya?" Ta maimaita a kan laɓɓanta har ba ta san lokacin da ta kalle shi ba. Lura da maganar da ya faɗa ɗin ta sakata mamaki ne ya sanya shi sakin hannun nata a hankali kafin yace
"Mene ne haɗinku da wadda kika kira da ƙanwar Abba?" Ya tambaya yana kafeta da idanunsa. Shiru ta yi, kamar yanda ya kafeta da idanu haka ita ma ta kafe shi da su. A karo na farko da ko da da second ɗaya ne ba ta ji tsoron haɗa idanu da shi ba. Se dai wannan kwarjinin na nan. Amma duk da haka ba ta janye ba.
"Ki ba ni amsa." Ya sake faɗa. Kawai se ta sauke ajiyar zuciya. A yanda take ta uban fushin nan be yi tunanin da wuri haka za ta sakko har ta masa magana ba. Se kuwa ta fara faɗin
"Ƙanwar Abba ce wallahi.. Babansu ɗaya." Jinjina kai Gwani ya shiga yi yana sake yin mamakin Mamin.
"Kin san ta san da zaman hoton nan? Kar ki faɗa min ba gaskiya ba.." Ya yi tambayar da kuma maganar duka a haɗe. Shiru ta yi a ranta tana tunanin idan dai har ta faɗa masa to ta tonawa Mamin asiri. Idan kuma ba ta faɗa ba wani abu ya zo ya faru tabbas za ta zama me laifi. Kamar ba za tace komai ba se kuma tace
"Ita...." Se ta dakata a nan kamar wadda aka riƙe. Ya fesar da iska daga bakinsa kafin ya kai hannunsa ya sake riƙo hannunta ya sanya shi cikin nasa. Cikin nutsuwa kamar me raɗa yace
"Kar ki damu. Kar ki ji komai.. ki faɗa min abin da kika sani. Kar ki ɓoye min komai Uhmm?" Ya ƙare yana kallanta. Se ta zame hannun da sauri tana ɓata fuska. Babu musu ya sakar mata hannun. Se da ta sake ɗaukar wasu sakannin kafin ta cigaba da faɗin
"Ita ce ta nuna min hoton a wayarta.." Ta dakata a nan. Se kuma tace
"Don Allah kar ka faɗawa su Abba. Idan dai ka faɗa musu se sun ji abin da ya faru. Don Allah ka min alƙawari." Ta faɗa a sanyaye.
"Na yi miki." Ya ba ta amsar a taƙaice yana lumshe ido, saboda yanda ta yi maganar ba ƙaramin dukan zuciyarsa hakan ya yi ba. Kasancewarsa Malami ya sanyata amincewa, dan ta san ba ze faɗi abu kuma ya zo ya ƙi yi ba musamman ma dai a yanda ta san Gwanin.
"Me ya saka ta samo hoton toh? Ko ita ce ta saka a ɗauka?" Girgiza kai Lulu ta yi tace
"A'ah ba ta faɗa min ba. Ce min ta yi wai.. ze taimaka idan ka gani hakan ya sa ka..." Se kuma ta ƙi ƙarasawa. Ta saci kallansa ta ƙasan idanunta. Murmushi ya yi yana girgiza kai
"In sake ki ba..?" Se yanzu ya fahimci kan labarin. Wato ashe ita ta nemi Hero ya ba ta hoto ne dan ta ba wa Abbati. Shi kuma Abbati ya nuna masa daga haka ya saketa. Saboda ga lusarin namiji, wanda be san abin da yake yi ba. Ko da yake ko babu komai hakan ya yi sanadiyyar gyaruwar abubuwa da dama a zamantakewarsu. Daga ƙarshe kuma ga shi ta rufta da su Mami a ciki.
"Ba zan sanar da Abba abin da ya faru ba, ko dan ka da zumuncinsu ya lalace. Se dai ki sani daga yau na datse duk wata alaƙa da ke tsakaninku. Ba na so na sake ganin ku na alaƙa kamar ta da. Se dai kasancewarki musulma ita ma haka, kuma er uwar mahaifinki ya sa na sahalce miki gaisuwa da kuma sallama. Daga nan babu wani abu.. Kin fahimta?" Kawai se ta samu kanta da gyaɗa kai kamar wata ƙadangaruwa. Ya yi murmushi har cikin ransa yana jin daɗin hakan.
.. Daga cikin ɗakin ta fito hannunta ɗauke da wayar. Ta nemi waje ta zauna tana kara wayar a kunnenta.
"Ashe ki na kusa.."
"Ehh Abbansu ina kusa.." Ta amsa tana murmushi. Kafin yace komai ta ɗora da faɗin
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai.. Ki na lafiya?" Shi ma ya amsa mata da murmushin kan fuskarsa.
"Alhamdulillah."
"Madallah.. ya masu jikin?"
"Gwaggo kam ta warware. Toh ka san yanayin jikin nata har yanzu dai ba su sallame mu ba. Ita ma kuma waccan ɗin an ce ana samun cigaba. Su na saka ran farfaɗowarta ma nan da kwanaki kaɗan."
"Toh Ma Sha Allah.. Allah Ya ƙara lafiya. Ki samu idan ana buƙatar wani abu ne ko dan a ceto lafiyarta ki bayar. Kin san irin waɗannan ciwukan su na da cin kuɗi."
.. "Ki yi haƙuri In Sha Allah komai ze daidaita. Za kuma ta samu sauƙi da yaddar me sama." Gwaggo ta faɗa tana kallan Talatuwa. Jinjina kai Ammi ta yi kafin a nutse ta ɗora da
"In Sha Allah.." Hannu Talatuwa ta kai ta goge fuskarta kafin tace
"Ina fatan haka ni ma. Amma yanda suka fita da ita ne ya ba ni tsoro."
"Babu damuwa hakan ma. Ke dai kawai ki fawwalawa Allah." Ba ta iya amsawa ba se ɗaga kai da ta yi. Shiru ne ya wanzu a wajen na en mintuna kowa da abin da yake tunani. Kafin daga bisani Gwaggo ta kalli Ammi tace
"Goben za ki wuce Fatima?" Kallan Gwaggo Ammi ta yi tana ji kamar tace a'ah, dan duk da Gwaggon ba ita ta haifeta ba amma tana ganinta ne kamar tata mahaifiyar da ba ta raye. Se dai kuma ta riga ta faɗawa Abba adadin kwanakin da za ta yi. Ba kuma ta so ta saɓa hakan. Don haka tace
"Ehh.. mun yi magana da Maryam tana nan tahowa a goben."
"Toh shi kenan babu matsala. Allah Ya kai mu." Tun da suka soma magana Talatuwa ke kallansu, har zuwa lokacin da suka gama. Se ta sauka daga kan kujerar da take ta ƙarasa zuwa wadda Ammi take. Hannu ta saka ta kamo hannun Ammin daidai lokacin da hawaye suka cika idanunta tace
"Don Allah.. ba don halinmu ba, ki taimaka ki bari kar ki tafi har se Maimuna ta farka. Duk wasu alamomi sun nuna tana son magana da ke ne. Ban sani ba ko ta sanki ne ko ke kin santa tuntuni. Don Allah ki mana wannan alfarmar Hajiya." Shiru Ammi ta yi tana kallanta dan ba ta san me za tace ba.
"Ki na ganin kin san fuskarta ne?" Gwaggo ta yi maganar tana kallan Ammi. Girgiza kai Ammi ta yi, tana tunanin ko ta santa ɗin ne. Se dai kuma duk wani tunaninta ita dai ba ta san Maimunan ba. Hasalima ba ta taɓa ganinta ba se zuwansu asibitin.
"Ikon Allah! Toh kuma ba ta taɓa faɗa miki wata magana da za ta saka yanzu ki kawo ko tana da alaƙa da abin da ya faru ɗazun." Gwaggo ta faɗa tana kallan Talatuwa.
"Wallahi ba ta taɓa ba. Abin da kawai zan ce cikin shekarun baya gaskiya ta haɗu da ciwon damuwa. Don haka kawai za ta zauna ta yi ta tunani kamar me iskokai. Komai tunani komai tunani. Shi ne dai daga ƙarshe aka ce mana ciwon damuwa ne. Kuma na yi na yi ta faɗa min abin da ke damunta ta ƙi. Wallahi daga haka dai ciwo ya din ga tafiya. Daga wannan lalurar se wannan. Har dai aka zo kan wannan na shanyewar jikin." Talatuwa ta ƙare a sanyaye. Ita dai Ammi har lokacin ba ta sake cewa komai ba tun bayan amsar da ta baiwa Gwaggo. Har zuwa lokacin da Gwaggon ta sake faɗin
"Ki yi haƙuri Fatima. Ki ba ni wayar da kaina zan masa bayanin abin da ya faru, wanda ze hanaki komawa. Duk da na san halin Muhammadu mutumin kirki ne." Murmushi Ammi ta yi kafin tace
"Toh Gwaggo."
.. A nutse ya tura ƙofar ɗakin da sallama ɗauke a bakinsa. Sanye yake cikin wata tattausar farar jallabiyya. Kansa babu komai yanzu haka. Se gyarararriyar sumar kan nan nasa da kuka sani a waje. Hakan ba ƙaramin kyau ya yi ba. A nutse ya ƙarasa ya nemi kan gadon ya zauna. Tana ganin haka ta ɗauke kai ta juya wani ɓangaren tana wasa da gefen hijab ɗinta. A nutse ya ɗaga idanunsa ya kalleta na tsawon second 10 kafin ya ɗauke idanunsa daga kanta.
"Afaaf.." Ya kira sunanta kai tsaye yana maida dubansa kanta. Idan da ita wata ce a yanda ya yi magana kaɗai ya isa ya nuna mata magana me muhimmanci yake son yi da ita. Amma ita ba ma ta fahimci hakan ba. Se kawar da kai da ta sake yi tana turo baki gefe guda kuma zuciyarta na neman karyewa. Dan ita yanzu sam ba ta so ta gansu waje ɗaya. Da da dama ma tashi za ta yi ta bar masa wajen, se dai kuma yanzu ta san halinsa ƙaramin aikinsa ne ya kamota. Jin da ya yi ta yi shiru ne ya sanya shi lumshe idanunsa a kan laɓɓansa ya furta
"Se yaushe ne..?" A fili kuma se ya yi amfani da hannunsa wajen lalubo inda nata hannun yake ya sanya shi cikin nasa ya riƙe da duka biyun. Da sauri ta juyo da niyyar ƙwacewa. Se dai a yanda ya zuba mata narkakkun idanunsa, se ta ga kallan da yake mata a kwanakin nan ba irin wannan ba ne. Dan yanzun se ta ga yana neman rikiɗe mata ya koma Gwani na can baya. Gwani Affan Ya mu'allim ɗin Islamiyyarsu. Dalilin kenan da ya sanya ta yi maza ta janye idanunta da ke wani girgiɗi.
"Ki nutsu.. ki kalle ni da kyau.. ki kuma faɗa min gaskiya." Ya faɗa sanda ya lura ba ta haƙura ba tana cigaba da neman ƙwace hannayenta ne.
"Gaskiya?" Ta maimaita a kan laɓɓanta har ba ta san lokacin da ta kalle shi ba. Lura da maganar da ya faɗa ɗin ta sakata mamaki ne ya sanya shi sakin hannun nata a hankali kafin yace
"Mene ne haɗinku da wadda kika kira da ƙanwar Abba?" Ya tambaya yana kafeta da idanunsa. Shiru ta yi, kamar yanda ya kafeta da idanu haka ita ma ta kafe shi da su. A karo na farko da ko da da second ɗaya ne ba ta ji tsoron haɗa idanu da shi ba. Se dai wannan kwarjinin na nan. Amma duk da haka ba ta janye ba.
"Ki ba ni amsa." Ya sake faɗa. Kawai se ta sauke ajiyar zuciya. A yanda take ta uban fushin nan be yi tunanin da wuri haka za ta sakko har ta masa magana ba. Se kuwa ta fara faɗin
"Ƙanwar Abba ce wallahi.. Babansu ɗaya." Jinjina kai Gwani ya shiga yi yana sake yin mamakin Mamin.
"Kin san ta san da zaman hoton nan? Kar ki faɗa min ba gaskiya ba.." Ya yi tambayar da kuma maganar duka a haɗe. Shiru ta yi a ranta tana tunanin idan dai har ta faɗa masa to ta tonawa Mamin asiri. Idan kuma ba ta faɗa ba wani abu ya zo ya faru tabbas za ta zama me laifi. Kamar ba za tace komai ba se kuma tace
"Ita...." Se ta dakata a nan kamar wadda aka riƙe. Ya fesar da iska daga bakinsa kafin ya kai hannunsa ya sake riƙo hannunta ya sanya shi cikin nasa. Cikin nutsuwa kamar me raɗa yace
"Kar ki damu. Kar ki ji komai.. ki faɗa min abin da kika sani. Kar ki ɓoye min komai Uhmm?" Ya ƙare yana kallanta. Se ta zame hannun da sauri tana ɓata fuska. Babu musu ya sakar mata hannun. Se da ta sake ɗaukar wasu sakannin kafin ta cigaba da faɗin
"Ita ce ta nuna min hoton a wayarta.." Ta dakata a nan. Se kuma tace
"Don Allah kar ka faɗawa su Abba. Idan dai ka faɗa musu se sun ji abin da ya faru. Don Allah ka min alƙawari." Ta faɗa a sanyaye.
"Na yi miki." Ya ba ta amsar a taƙaice yana lumshe ido, saboda yanda ta yi maganar ba ƙaramin dukan zuciyarsa hakan ya yi ba. Kasancewarsa Malami ya sanyata amincewa, dan ta san ba ze faɗi abu kuma ya zo ya ƙi yi ba musamman ma dai a yanda ta san Gwanin.
"Me ya saka ta samo hoton toh? Ko ita ce ta saka a ɗauka?" Girgiza kai Lulu ta yi tace
"A'ah ba ta faɗa min ba. Ce min ta yi wai.. ze taimaka idan ka gani hakan ya sa ka..." Se kuma ta ƙi ƙarasawa. Ta saci kallansa ta ƙasan idanunta. Murmushi ya yi yana girgiza kai
"In sake ki ba..?" Se yanzu ya fahimci kan labarin. Wato ashe ita ta nemi Hero ya ba ta hoto ne dan ta ba wa Abbati. Shi kuma Abbati ya nuna masa daga haka ya saketa. Saboda ga lusarin namiji, wanda be san abin da yake yi ba. Ko da yake ko babu komai hakan ya yi sanadiyyar gyaruwar abubuwa da dama a zamantakewarsu. Daga ƙarshe kuma ga shi ta rufta da su Mami a ciki.
"Ba zan sanar da Abba abin da ya faru ba, ko dan ka da zumuncinsu ya lalace. Se dai ki sani daga yau na datse duk wata alaƙa da ke tsakaninku. Ba na so na sake ganin ku na alaƙa kamar ta da. Se dai kasancewarki musulma ita ma haka, kuma er uwar mahaifinki ya sa na sahalce miki gaisuwa da kuma sallama. Daga nan babu wani abu.. Kin fahimta?" Kawai se ta samu kanta da gyaɗa kai kamar wata ƙadangaruwa. Ya yi murmushi har cikin ransa yana jin daɗin hakan.
.. Daga cikin ɗakin ta fito hannunta ɗauke da wayar. Ta nemi waje ta zauna tana kara wayar a kunnenta.
"Ashe ki na kusa.."
"Ehh Abbansu ina kusa.." Ta amsa tana murmushi. Kafin yace komai ta ɗora da faɗin
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai.. Ki na lafiya?" Shi ma ya amsa mata da murmushin kan fuskarsa.
"Alhamdulillah."
"Madallah.. ya masu jikin?"
"Gwaggo kam ta warware. Toh ka san yanayin jikin nata har yanzu dai ba su sallame mu ba. Ita ma kuma waccan ɗin an ce ana samun cigaba. Su na saka ran farfaɗowarta ma nan da kwanaki kaɗan."
"Toh Ma Sha Allah.. Allah Ya ƙara lafiya. Ki samu idan ana buƙatar wani abu ne ko dan a ceto lafiyarta ki bayar. Kin san irin waɗannan ciwukan su na da cin kuɗi."