← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 122

Sashe 82

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

... Har cikin gidan marayun Daddy da kansa ya yi parking na motarsa. Ya juya ya kalli Mommah da tun ɗazun ya lura da idanunta da suka yi ja yace

"Kukan kuma na mene ne?" Se ta girgiza kai da sauri, dan ba ta so Daddyn ya gano abin da ke faruwa. So take ta yi amfani da wasu dabarorin nata ta yi maganin Bad Man ɗin. Sam kuma ya dena shan komai gaba ɗaya da yaddar Allah.

"Babu komai Yallaɓai.." Se da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ɗauki waya ya kira wata number. Tsawon minti 1 suna magana kafin ya ajje wayar. Cikin ƙanƙanin lokaci se ga wasu mutane 2 sun zo. Ɗaya ya saka hannu ya buɗewa Daddy ƙofar motar. Babu musu ya fito. Se a lokacin Mommah, Bad Man da kuma Didi, se kuma Little da ke hannun Bad Man suka sauko daga cikin motar. Babu ɓata lokaci aka ɗauke su zuwa cikin wani ɗaki. Babu wanda ke cewa da ɗan uwansa uffan, dan kuwa kowa da abin da yake saƙawa a ransa.

"Barka da zuwa Yallaɓai.." Wani babban mutum ya faɗa yana kallan Daddy. Murmushi Daddy ya yi yana faɗin

"Barka dai." Ya yi maganar hawa kan kujera ya zauna. Se da ya zauna sannan aka baiwa su Mommah kujeru su ma suka zauna.

"Ina jinka Yallaɓai.." Wanda ke zaune kan kujera ya faɗa yana kallan Daddy. Se da Daddy ya gyara zama sannan ya soma faɗin

"Wani taimako nake so ka mana.. duk da na san an fara maka bayani.. Amma idan ka ji daga bakina se yafi.. A ranar 1 ga watan june..." Daga nan Daddy ya sanar da shi kwanan watan da su Mommah suka haihu, da kuma duk wani abu da ya kamata su ji wanda ze ba su haske a kan neman jaririn da aka yar a ranar. Jinjina kai dattijon mutumin ya shiga yi bayan da ya gama jin bayanin Daddy. Ya sauke ajiyar zuciya kafin yace

"Wato ze iya zama a ga yaron har a ɗauke shi a kawo shi cikin gidan nan.. Se dai ba ni da tabbas, amma zan saka a dubo files ɗin ranar. Dan kuwa duk yaron da aka kawo yana da file, idan da rabon an kawo shi ɗin za ku iya samunsa cikin gidan nan ko kuma wajen masu karɓar yara idan suna buƙata.."

"Toh godiya nake.."

"Babu damuwa.. Ai ka fi ƙarfin haka Alhaji.. Kawai dai se kun ɗan yi haƙuri saboda abun ne da yawa.. Ka ga shekarun suna da yawa."

"Babu damuwa.. Idan dai har za a gani za mu iya jira.." In ji Daddy. Se a lokacin Mommah ta sauke ajiyar zuciya dan ita ma abin da za ta faɗa kenan Daddy ya rigata. Se suka cigaba da zama jiran wanda ya tafi binciko files ɗin.

... Fitowarta daga wanka kenan, ta ƙarasa ta buɗe wardrobe ta ɗauki wani riga da skirt na wani material me kyau ta saka. Se da ta gama shiryawa tsaff sannan ta nufi ɗakin nan. Se ta shiga duddubawa kamar me neman wani abun. Se dai tunanin abin da za ta ɗora take yi. Dan har cikin ranta take jin rashin dacewar barin Ummeey ta cigaba da yin girki cikin gidan, duk da dai ita ke zuwa ta tayata. Amma yau ɗin haka nan ta tashi da niyyar ɗora wani abun da za su ci. Kai tsaye gas ta kunna ta ɗora girkin. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa wani irin ƙamshi me daɗi ya baɗaɗe ɗakin. Ba ta san dalilin da ya sa ta ji sam ƙamshin be mata ba. Duk se ranta ya ɓaci tana ganin ga shi ta yi girki amma kuma da alama ba ze yi daɗi ba, dan kuwa ƙamshin da girkin ke yi irin me ɗaga zuciyar nan ne. Ta ɗan ja numfashi tana sake dubawa ko dai ba ta kula ba ta saka wani abun da be kamata ba? Jin da gaske dai sam ƙamshin be mata ba ya sanyata ficewa daga ɗakin tana ɓata rai. Neman waje ta yi ta zauna a gefen gado har lokacin ji take kamar ta yi kuka. Ta cigaba da sauke ajiyar zuciya a hankali. Daidai lokacin Gwani ya yi sallama cikin ɗakin, ƙamshin da ya fara dakar masa hanci shi ne ya tilasta masa lumshe idanunsa. A hankali ya ƙarasa cikin ɗakin idanunsa a kanta. Ba ƙaramin kyau ta yi masa ba. Musamman da ya kasance yau babu wannan hijab ɗin, se ɗan kwalin material ɗin da ta sake shi ba ta ɗaura ba. Ya ɗan lumshe idanunsa yana murmushi, daidai lokacin da ta ɗago kanta ta kalle shi saboda jin alamar ido da ta yi a kanta, dan sam ba ta ji sallamarsa ba, ta faɗa can wata duniyar.

"Sannu da gida.." Ya yi maganar yana kallanta dai. Be yi tunanin amsarta ba, ko kuma dai be yi tunanin za ta amsa da

"Sannu da zuwa.." ba. Ta faɗa tana miƙewa. Se ya saka hannunsa ya riƙo hannunta ya juyo da ita tana kallansa.

"Ina za ki je?"

"Wajen Ummeey zan je fa.." Ta ba shi amsa da sauri tana yamutsa fuska.

"Yanzu duk wannan ƙamshin da nake ji haka za ki tafi ki bar ni ba tare da kin sammun ba? Toh a taimaka a sammun na ɗanɗana.." Ya yi maganar a narke kamar wani maraya, kai ba za ka ce Gwani ba ne. Ba ta san lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi ba. Ya langaɓar da kansa gefe kamar me neman taimako. Wallahi ba ta san lokacin da dariya ta suɓuce mata ba saboda da gasken gaske ya bata dariya sosai. Ya lumshe idanunsa yana jin wani irin sanyi na ratsa shi. Wannan murmushin nata kaɗai abun farin ciki ne a wajensa, ya kuma ƙawatar, ya kuma ƙarawa kyakkyawar fuskarta kyau. Se a lokacin da ya buɗe idanunsa sannan ta tuna abin da ta yi. Ta yi saurin maida fuskarta yanda take tana yin baya saboda ya cika mata hannu.

"Zan samu abincin?" Ya sake katseta da faɗin hakan. Se kawai ta kafe shi da idanu kamar ba ita ba. Ita mamaki abun ya bata, ta ya ya ma ze ce wannan ƙamshin ne ya masa daɗi? Ƙamshin da ke neman sakata kasa zama cikin ɗakin? Ko dai ya faɗa ne kawai dan ta ji daɗi? Ita dai har ga Allah ba ta so yace ba ta iya girki ba dan yau an samu tangarɗa. Yanda kuma ya yi mata maganar se ta kasa bijirewa. Kamar tace masa ta cinye se kawai ta yi shahada ta ƙarasa ɗakin. Zuwa lokacin ƙamshin ya ɗan yi ƙasa ba kamar ɗazu ba. Amma duk da haka ita tashin zuciya ma take ji. Haka dai ta daure da sauri da sauri ta zuba abincin cikin flask. Ta ɗauko plate da spoon ta fito daga ciki. A karo na barkatai wani murmushi ya ƙara suɓuce masa. A kan laɓɓansa ya furta

"Ubangiji Ya ƙara gyara tsakaninmu. Ya kuma ƙara shirya min ke." Ya faɗa dan har ga Allah yana jin daɗin chanjawar Lulun fiye da zaton me zato. Kuma da alama kamar abun kullum gaba yake yi. Har gabansa ta ƙaraso ta ajje abin da ta ɗakko ɗin sannan ta juya ta fice daga ɗakin, dan tabbas idan ta cigaba da zama wannan ƙamshin ze sanyata amayar da abin da ke cikinta. Kuma ko babu komai gwara ya faɗi ko ma meye a kan abincin ba a gabanta ba. Da dai ya kushe girkinta a gabanta, gwara a bayan idanunta. Kai tsaye ɗakin Ummeey ta wuce. Da sallama ta shiga. Amsa sallamarta Ummeey ta yi tana kallan ƙofar ɗakin. Fuskarta ɗauke da murmushi take faɗin

"'Yata ke ce?" Se da Lulu ta yi murmushi sannan tace

"Ehh Ummeey.."

"Toh maraba.." Ta yi maganar tana gyara tabarmar da take kai. Neman waje Lulu ta yi ta zauna, suka sake gaisawa da Ummeeyn. Daga haka ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba. Se Ummeey ke ɗan jefo hira kaɗan kaɗan. Zuwa can dai da Lulu ta gaji, ga yunwa da take ji ya sanyata gyara zama. Ta ɗan ja numfashi kafin tace

"Ummeey babu yaɗiya?" Ta faɗa har a cikin idanunta tana tuna yaɗiyar nan ta Ummeey me ɗan karen daɗi. Murmushi Ummeey ta yi sannan tace

"Yaɗiya kike so Afaaf?" Da sauri ta jinjina kai hadda wani haɗiye yawu kafin ta amsa da

"Ehh Ummeeey.."

"Toh yi zamanki a nan.. Yanzun nan Malam ya shigo da ita, kin san da yake gwaninta ne, bari na kwaɗa muku.." Murmushi ta yi har haƙoranta na bayyana sannan ta amsa da

"Toh Ummeey.." Daga haka Ummeey ta fice daga ɗakin.

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO69*

___ A ɗaya ɓangaren kuwa bayan shuɗewar mintuna masu yawa se ga mutumin da ya fita daga ɗakin ɗazun ya sake shigowa hannunsa ɗauke da wasu files da yawa. Kai tsaye zuwa ya yi ya ajje su a gaban dattijon mutumin nan sannan ya fita daga ɗakin.

"Toh bari na duba.. Allah Ya sa a dace.."

"Ameen.." Dukkansu suka amsa da hakan. Se a lokacin Bad Man ya nemi waje ya zauna, ya lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda. Hannunsa duka biyun ya haɗe waje ɗaya ya shiga jijjigasu. Shi kansa a yanzu haka ba shi da buri da ya wuce ya ga twin brother ɗin na shi. Ya gan shi a raye cikin ƙoshin lafiya idan ya so sa yi farin cikin gaba ɗaya. Dan kuwa har yanzu be gama komawa daidai ba. Daga zarar ya yi shiru se ya tuna abin da ya faru. Shi kaɗai ya san irin adadin tsanar Mom da duk wani da ya shafeta da yake ji a yanzu haka. A hankali ya shiga duba files ɗin. Kowanne cikinsu kallansa yake yi yana addu'a cikin zuciyarsa. Ya kai wajen minti 10 yana dubawa kafin ya ɗaga kai yana kallansu cike da tausayawa. Se da ya koma ya zauna a inda ya tashi sannan yace
Chapter 82 · 0% Book details