Sashe 110
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ban san yanda za a yi ba ranar da Babyn nan ya tashi zuwa duniya.." Ya ƙare yana kai hannunsa kan cikinta. Hannun nasa da ke can ƙarshen cikinta ta bi da kallo. Haka nan kawai ta ji fargaba ta kamata. Se kawai ta ɗora nata hannun a kan nasa tana lumshe idanunta. Ya sake yin murmushi cike da fatan ɗorewar zaman lafiya da kuma ƙaunar juna a tsakaninsa da Lulun.
"Areef na neman ki." Ya faɗa tuna abin da ya shigo da shi. Da mamaki tace
"Ni?"
"Ehh Afrah ke son ganin ki." Murmushi ta yi kafin tace
"Ta zo nan ne?" Girgiza kai ya yi yace
"A'ah.." Se ta soma takawa za ta fice daga kitchen ɗin. Ya marairaice fuska da murya tamkar yaron goye yace
"A nan za ki bar ni?" Ya ƙare yana zabga uban tagumi. Dakatawa ta yi kafin ta juya ta kalle shi. Yanda ya yi ɗin se ya bata dariya, kawai se ta yi murmushin tana dawowa baya.
"Toh mu tafi." Ta faɗa tana kallansa. Se a lokacin ya yi murmushi kafin ya soma takawa. Tare suka fito cikin ɗakin, kafin ita kuma ta yi waje inda Bad Man yake. Gaisawa suka yi kafin yace
"Wani taimako za ki min pls.."
"Tohm." Ta amsa duk da cikin zuciyarta fall mamaki ne.
"Amm.. Ina so ne ki ɗan kular min da Afrah pls, ba ta jin daɗi ne.." Ya yi maganar cikin er basarwa, wai duk dan kar ta ga fuskar tambayarsa ko lafiya? Wani irin bugawa da zuciyarta ta yi shi ne abin da ya sa ta ma manta da wani tambayarsa ko lafiya. Muryarta har ta soma karkarwa tace
"Tohm." Daga haka ba ta jira ya sake cewa komai ba ta bar wajen. Ya sauke ajiyar zuciya, a ransa yana fatan a ce babu wani abu da ya faru.
Ko sallama kasa yi ta yi, kai tsaye cikin ɗakin ta faɗa. Ta yi tunanin za ta ganta cikin palour, se dai babu ita babu alamunta. Hakan ne ya sanyata faɗawa cikin ɗakin da take da tabbacin za ta sameta ciki. Hangota kan gado da ta yi ba ƙaramin sake tayar mata da hankali ya yi ba, cikin lokaci ƙanƙani idanunta suka tara ƙwalla. Se ta ƙarasa da sauri tana faɗin
"Didi.." Ta yi maganar tana saka hannu ta taɓo fuskarta. Buɗe idanunta Didi ta yi da sauri tana kallan Lulu cike da mamakin jin muryarta. Ba dai zuwa ya yi ya sanarwa da Lulun abin da ya faru ba? Ta tambayi kanta tana kallan Lulun.
"Me ke damun ki Didi?" Wannan tambayar da Lulun ta mata, ita ce ta sa ta jin ɗan sauƙi. Se ta ƙaƙalo murmushi kafin tace
"Ciwon jiki." Ta ƙare maganar tana sake riƙo hannun Lulun da ke taimaka mata dan ta miƙe.
"Wayyo.." Didi ta faɗa tana ɗan runtse idanunta.
"Na shiga 3 Didi me ya same ki? Duk ciwon jikin ne?" Lulu ta faɗa tana share hawayen da har sun soma zuba a kan kuncinta. Jinjina kai Didi ta yi, dan ita dai ba ta fata Lulun ta gane abin da ya faru. Haka kawai.. Kawai se ta tattaro duk wani ƙarfinta da ya rage, ta miƙe tsayen. Lulu ta taimaka mata ta zaunar da ita a kan kujera. Kallanta Lulu ta cigaba da yi, har zuwa lokacin da ta ɗan karkace ta kwantar da kanta a kan hannun kujerar.
"Didi ko dai..?" Lulu ta faɗa tana saka hannunta a kan bakinta. Babu shiri Didi ta buɗe idanunta tace
"Me?" Girgiza kai Lulu ta yi tana dariya ƙasa ƙasa, dan se yanzu ta fahimci abin da ke faruwa.
"Ba komai fa." Ta ƙare cikin basarwa, tana kuma riƙe kanta dan kar ta sheƙe da dariya. Lura da hakan da Didi ta yi ne ya sanyata yin kici kicin da fuska tace
"Toh ma me ya kawo ki ɗakin nan?"
"Toh ni fa da ma Yaya Areef ne yace na zo na kula da ke.."
"Haka yace miki?" Didi ta tambaya kamar xa ta yi kuka.
"Eh wai ba ki da lafiya." Lulu ta faɗa tana ƙunshe dariyarta. Kawai shiru Didi ta yi dan ba ta san kuma me za tace ba. Kunya dai kam ya riga ya gama bata.
"Allah zan miki rashin mutunci Lulu." Didi ta faɗa cikin ƙarfin hali, tana kuma galla mata harara.
"Toh ni me na yi?" Ta yi maganar tana tura baki. Shiru kawai Didi ta yi ba ta sake cewa komai ba. Tana kallan Lulu ta shige toilet, bayan wasu mintuna se gata ta fito. Kamar yanda Ummeey ta umarceta da yi lokacin suna gida, haka ta saka Didi ma ta yi. Haka dai Didi tana ji tana gani ta koma ita ce ƙanwar, Lulu kuma babba. Haka dai ta din ga basarwa, tana aro jarumta duk dan kar Lulun ta rainata. Ita kuwa Lulu dariyarta take sha ƙasa ƙasa dan ta riga ta san kawai mazewa take yi. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa se ga shi ta ji jikinta ya saki sosai, ta ji daɗinsa sosai.
"Kin ga Didi idan za ki saki jiki ki yi abubuwanki ki yi.. Ni ba wanda zan faɗawa." Ta faɗa lokacin da take nesa da Didi. Juyawa Didi ta yi ta rarumi pillown da ke bayanta ta jefawa Lulu. Lulu ta kauce tana sheƙewa da dariya. Ta bita da kallo, ba ta san lokacin da murmushi ya ƙwace mata ba. Soyayyar er uwatta na sake ratsata. Babu ƙarya zuwan Lulun ya mugun mata amfani, dan ƙila da tuni har yanzu tana nan a kwance. Abun kuma ya burgeta yanda yau ɗin Lulun ta zama ita ce yayar.
"Allah Ya sauke ki lafiya Habibty." Ta faɗa a kan laɓɓanta tana cigaba da kallan Lulun da kullum sake kyau da murjewa take yi.
... Murmushi ne ya wanzu a kan fuskarsa lokacin da ya ga number da ke yawo a kan wayar tasa. Ya ɗauka yana karawa a kunnensa. Se da ya nemi waje ya zauna kafin yace komai, daga can ɓangaren aka ce
"Affan.."
"Na'am Ummeey.." Ya amsa da hakan.
"Ka na ina ne?" Ta faɗa muryarta a sanyaye, tana kuma bayyana damuwar da take ciki. Haka nan kawai ya ji faɗuwar gaba ta zo masa, jin muryar Ummeeyn tasa. Ya ɗan sauke numfashi yana gyara zamansa, yace
"Ina gida."
"Ka taho gida toh.. Ka ga Abeeynka ne babu lafiya." Be san lokacin da ya miƙe tsaye ba daidai lokacin da bugun zuciyarsa ya tsananta. Abeey ba lafiya? Ba ɗazun nan ya baro gidan ya same shi ƙalau ba? Ko da ma ba shi da lafiya ne be sanar da shi ba? Me ye ke damun Abeeyn? Dukka waɗannan tambayoyin suke yawo cikin ƙwaƙwalwarsa. Ya yi ƙoƙarin saita nutsuwarsa, muryarsa har ɗan rawa take yi lokacin da ya furta
"Me ke damunsa Ummeey?" Tun lokacin da ta shigo take kallansa, kai tsaye wajensa ta nufa. Ta kalle shi yanda ta ga cikin ƙanƙanin lokaci yanayinsa ya chanja. Ita kanta se da ta ji faɗuwar gaba ta zo mata. Se kawai ta cigaba da kallansa a ranta tana fatan Allah Ya sa lafiya.
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO81*
___ A sukwane ya sauke wayar daga kunnensa. Ta sake kallansa tana jin ƙirjinta na bugawa da ɗan ƙarfi. Jira take ta ji me ze ce, se dai da alama ba shi da niyyar cewa komai. Dalili kenan da ya sanyata faɗin
"Me ya faru?" Ta tambaya cike da fargaba tana sake jin faɗuwar gaba na zo mata. Se da ya sauke numfashi kafin yace a hankali.
"Abeey ne ba lafiya."
"Subhanallahi.. me ke damunsa?" Girgiza kai ya yi lokaci ɗaya yana jefa wayarsa cikin aljihu kafin yace
"Ba na ce ba.. Bari dai kawai na tafi.." Ya ƙare yana duba gefe ko da akwai abin da ze ɗauka. A gaggauce ya miƙe kuma ba tare da ya sake cewa komai ba ya zo ze fice. Ba ta san lokacin da ta riƙo hannunsa ba. Ya dakata yana juyawa ya kalleta. Duk ta yi wani sanyi, se ka ce mara lafiya. Yanda ya gantan duk a dame, ya kuma san hakan na da nasaba da yanayin da ta gan shi ne ya tilasta masa kai hannunsa kan nata hannun ya kalmashe su waje ɗaya. Ya yi ƙoƙarin wanzar da murmushi a kan fuskarsa kafin yace
"Kar ki damu Uhmmm?" Maƙe kafaɗa ta yi tana kwaɓe fuska kamar me shirin yin kuka. Dan ita dai har ga Allah ba ta san irin wannan yanayin da ta gan shi ciki. Be san lokacin da ya lumshe idanunsa ba, lokaci ɗaya sanyi da kuma fargabar halin da ze je ya samu Abeey suka dirar masa. Lallai se yanzu ne ya san ya yi aure, se yanzu ne ya san yana da mata.
"Ɗauko hijab ɗinki mu wuce.." Ya faɗa dan yana ganin wannan ce kaɗai hanyar da ta dace. Se kuwa ta sake shi da sauri. Ta ƙarasa wardrobe ta buɗe ta ɗauki wani dogon jalbab kala me kyau ta saka. Tsayawa ya yi kawai yana kallanta gaba ɗaya hankalinsa na gida. Dan da hankalinsa na nan da kansa ze zaɓa mata, har ma ya saka mata duk da ya san ƙilan ta yi ta zillewa.
... Se da ta bari ya idar da karatun da yake yi, ya ajje Alqur'anin a inda ya dace kafin ta kalle shi ta yi murmushi a nutse tace
"Yallaɓai.."
"Yallaɓiya uwar en biyu." Ya ƙare yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi kafin tace
"Ya karatun?"
"Alhamdulillah.." Ya faɗa yana gyara zamansa ya koma yana kallanta, kamar ya san dama muhimmiyar magana ce ta kawota.
"Wato Yallaɓai da ma wata magana ce ta kawo ni."
"Toh ina jinki." Se da Mommah ta sauke ajiyar zuciya kafin tace
"Waɗanda suka zauna tare da Areef a U.S da kuma waɗanda ke kula da sauran al'amuransa na gida nake so a sallama idan babu damuwa." Da mamaki sosai Daddy ke kallan Mommahn, dan ba su taɓa ko makamanciyar wannan maganar ce da ita ba.
"Kora? Da kanki?" Ya yi tambayar still yana kallanta. Se ta jinjina kai kafin ta ɗan sauke numfashi
"Ehh.."
"Areef na neman ki." Ya faɗa tuna abin da ya shigo da shi. Da mamaki tace
"Ni?"
"Ehh Afrah ke son ganin ki." Murmushi ta yi kafin tace
"Ta zo nan ne?" Girgiza kai ya yi yace
"A'ah.." Se ta soma takawa za ta fice daga kitchen ɗin. Ya marairaice fuska da murya tamkar yaron goye yace
"A nan za ki bar ni?" Ya ƙare yana zabga uban tagumi. Dakatawa ta yi kafin ta juya ta kalle shi. Yanda ya yi ɗin se ya bata dariya, kawai se ta yi murmushin tana dawowa baya.
"Toh mu tafi." Ta faɗa tana kallansa. Se a lokacin ya yi murmushi kafin ya soma takawa. Tare suka fito cikin ɗakin, kafin ita kuma ta yi waje inda Bad Man yake. Gaisawa suka yi kafin yace
"Wani taimako za ki min pls.."
"Tohm." Ta amsa duk da cikin zuciyarta fall mamaki ne.
"Amm.. Ina so ne ki ɗan kular min da Afrah pls, ba ta jin daɗi ne.." Ya yi maganar cikin er basarwa, wai duk dan kar ta ga fuskar tambayarsa ko lafiya? Wani irin bugawa da zuciyarta ta yi shi ne abin da ya sa ta ma manta da wani tambayarsa ko lafiya. Muryarta har ta soma karkarwa tace
"Tohm." Daga haka ba ta jira ya sake cewa komai ba ta bar wajen. Ya sauke ajiyar zuciya, a ransa yana fatan a ce babu wani abu da ya faru.
Ko sallama kasa yi ta yi, kai tsaye cikin ɗakin ta faɗa. Ta yi tunanin za ta ganta cikin palour, se dai babu ita babu alamunta. Hakan ne ya sanyata faɗawa cikin ɗakin da take da tabbacin za ta sameta ciki. Hangota kan gado da ta yi ba ƙaramin sake tayar mata da hankali ya yi ba, cikin lokaci ƙanƙani idanunta suka tara ƙwalla. Se ta ƙarasa da sauri tana faɗin
"Didi.." Ta yi maganar tana saka hannu ta taɓo fuskarta. Buɗe idanunta Didi ta yi da sauri tana kallan Lulu cike da mamakin jin muryarta. Ba dai zuwa ya yi ya sanarwa da Lulun abin da ya faru ba? Ta tambayi kanta tana kallan Lulun.
"Me ke damun ki Didi?" Wannan tambayar da Lulun ta mata, ita ce ta sa ta jin ɗan sauƙi. Se ta ƙaƙalo murmushi kafin tace
"Ciwon jiki." Ta ƙare maganar tana sake riƙo hannun Lulun da ke taimaka mata dan ta miƙe.
"Wayyo.." Didi ta faɗa tana ɗan runtse idanunta.
"Na shiga 3 Didi me ya same ki? Duk ciwon jikin ne?" Lulu ta faɗa tana share hawayen da har sun soma zuba a kan kuncinta. Jinjina kai Didi ta yi, dan ita dai ba ta fata Lulun ta gane abin da ya faru. Haka kawai.. Kawai se ta tattaro duk wani ƙarfinta da ya rage, ta miƙe tsayen. Lulu ta taimaka mata ta zaunar da ita a kan kujera. Kallanta Lulu ta cigaba da yi, har zuwa lokacin da ta ɗan karkace ta kwantar da kanta a kan hannun kujerar.
"Didi ko dai..?" Lulu ta faɗa tana saka hannunta a kan bakinta. Babu shiri Didi ta buɗe idanunta tace
"Me?" Girgiza kai Lulu ta yi tana dariya ƙasa ƙasa, dan se yanzu ta fahimci abin da ke faruwa.
"Ba komai fa." Ta ƙare cikin basarwa, tana kuma riƙe kanta dan kar ta sheƙe da dariya. Lura da hakan da Didi ta yi ne ya sanyata yin kici kicin da fuska tace
"Toh ma me ya kawo ki ɗakin nan?"
"Toh ni fa da ma Yaya Areef ne yace na zo na kula da ke.."
"Haka yace miki?" Didi ta tambaya kamar xa ta yi kuka.
"Eh wai ba ki da lafiya." Lulu ta faɗa tana ƙunshe dariyarta. Kawai shiru Didi ta yi dan ba ta san kuma me za tace ba. Kunya dai kam ya riga ya gama bata.
"Allah zan miki rashin mutunci Lulu." Didi ta faɗa cikin ƙarfin hali, tana kuma galla mata harara.
"Toh ni me na yi?" Ta yi maganar tana tura baki. Shiru kawai Didi ta yi ba ta sake cewa komai ba. Tana kallan Lulu ta shige toilet, bayan wasu mintuna se gata ta fito. Kamar yanda Ummeey ta umarceta da yi lokacin suna gida, haka ta saka Didi ma ta yi. Haka dai Didi tana ji tana gani ta koma ita ce ƙanwar, Lulu kuma babba. Haka dai ta din ga basarwa, tana aro jarumta duk dan kar Lulun ta rainata. Ita kuwa Lulu dariyarta take sha ƙasa ƙasa dan ta riga ta san kawai mazewa take yi. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa se ga shi ta ji jikinta ya saki sosai, ta ji daɗinsa sosai.
"Kin ga Didi idan za ki saki jiki ki yi abubuwanki ki yi.. Ni ba wanda zan faɗawa." Ta faɗa lokacin da take nesa da Didi. Juyawa Didi ta yi ta rarumi pillown da ke bayanta ta jefawa Lulu. Lulu ta kauce tana sheƙewa da dariya. Ta bita da kallo, ba ta san lokacin da murmushi ya ƙwace mata ba. Soyayyar er uwatta na sake ratsata. Babu ƙarya zuwan Lulun ya mugun mata amfani, dan ƙila da tuni har yanzu tana nan a kwance. Abun kuma ya burgeta yanda yau ɗin Lulun ta zama ita ce yayar.
"Allah Ya sauke ki lafiya Habibty." Ta faɗa a kan laɓɓanta tana cigaba da kallan Lulun da kullum sake kyau da murjewa take yi.
... Murmushi ne ya wanzu a kan fuskarsa lokacin da ya ga number da ke yawo a kan wayar tasa. Ya ɗauka yana karawa a kunnensa. Se da ya nemi waje ya zauna kafin yace komai, daga can ɓangaren aka ce
"Affan.."
"Na'am Ummeey.." Ya amsa da hakan.
"Ka na ina ne?" Ta faɗa muryarta a sanyaye, tana kuma bayyana damuwar da take ciki. Haka nan kawai ya ji faɗuwar gaba ta zo masa, jin muryar Ummeeyn tasa. Ya ɗan sauke numfashi yana gyara zamansa, yace
"Ina gida."
"Ka taho gida toh.. Ka ga Abeeynka ne babu lafiya." Be san lokacin da ya miƙe tsaye ba daidai lokacin da bugun zuciyarsa ya tsananta. Abeey ba lafiya? Ba ɗazun nan ya baro gidan ya same shi ƙalau ba? Ko da ma ba shi da lafiya ne be sanar da shi ba? Me ye ke damun Abeeyn? Dukka waɗannan tambayoyin suke yawo cikin ƙwaƙwalwarsa. Ya yi ƙoƙarin saita nutsuwarsa, muryarsa har ɗan rawa take yi lokacin da ya furta
"Me ke damunsa Ummeey?" Tun lokacin da ta shigo take kallansa, kai tsaye wajensa ta nufa. Ta kalle shi yanda ta ga cikin ƙanƙanin lokaci yanayinsa ya chanja. Ita kanta se da ta ji faɗuwar gaba ta zo mata. Se kawai ta cigaba da kallansa a ranta tana fatan Allah Ya sa lafiya.
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO81*
___ A sukwane ya sauke wayar daga kunnensa. Ta sake kallansa tana jin ƙirjinta na bugawa da ɗan ƙarfi. Jira take ta ji me ze ce, se dai da alama ba shi da niyyar cewa komai. Dalili kenan da ya sanyata faɗin
"Me ya faru?" Ta tambaya cike da fargaba tana sake jin faɗuwar gaba na zo mata. Se da ya sauke numfashi kafin yace a hankali.
"Abeey ne ba lafiya."
"Subhanallahi.. me ke damunsa?" Girgiza kai ya yi lokaci ɗaya yana jefa wayarsa cikin aljihu kafin yace
"Ba na ce ba.. Bari dai kawai na tafi.." Ya ƙare yana duba gefe ko da akwai abin da ze ɗauka. A gaggauce ya miƙe kuma ba tare da ya sake cewa komai ba ya zo ze fice. Ba ta san lokacin da ta riƙo hannunsa ba. Ya dakata yana juyawa ya kalleta. Duk ta yi wani sanyi, se ka ce mara lafiya. Yanda ya gantan duk a dame, ya kuma san hakan na da nasaba da yanayin da ta gan shi ne ya tilasta masa kai hannunsa kan nata hannun ya kalmashe su waje ɗaya. Ya yi ƙoƙarin wanzar da murmushi a kan fuskarsa kafin yace
"Kar ki damu Uhmmm?" Maƙe kafaɗa ta yi tana kwaɓe fuska kamar me shirin yin kuka. Dan ita dai har ga Allah ba ta san irin wannan yanayin da ta gan shi ciki. Be san lokacin da ya lumshe idanunsa ba, lokaci ɗaya sanyi da kuma fargabar halin da ze je ya samu Abeey suka dirar masa. Lallai se yanzu ne ya san ya yi aure, se yanzu ne ya san yana da mata.
"Ɗauko hijab ɗinki mu wuce.." Ya faɗa dan yana ganin wannan ce kaɗai hanyar da ta dace. Se kuwa ta sake shi da sauri. Ta ƙarasa wardrobe ta buɗe ta ɗauki wani dogon jalbab kala me kyau ta saka. Tsayawa ya yi kawai yana kallanta gaba ɗaya hankalinsa na gida. Dan da hankalinsa na nan da kansa ze zaɓa mata, har ma ya saka mata duk da ya san ƙilan ta yi ta zillewa.
... Se da ta bari ya idar da karatun da yake yi, ya ajje Alqur'anin a inda ya dace kafin ta kalle shi ta yi murmushi a nutse tace
"Yallaɓai.."
"Yallaɓiya uwar en biyu." Ya ƙare yana murmushi. Ita ma murmushin ta yi kafin tace
"Ya karatun?"
"Alhamdulillah.." Ya faɗa yana gyara zamansa ya koma yana kallanta, kamar ya san dama muhimmiyar magana ce ta kawota.
"Wato Yallaɓai da ma wata magana ce ta kawo ni."
"Toh ina jinki." Se da Mommah ta sauke ajiyar zuciya kafin tace
"Waɗanda suka zauna tare da Areef a U.S da kuma waɗanda ke kula da sauran al'amuransa na gida nake so a sallama idan babu damuwa." Da mamaki sosai Daddy ke kallan Mommahn, dan ba su taɓa ko makamanciyar wannan maganar ce da ita ba.
"Kora? Da kanki?" Ya yi tambayar still yana kallanta. Se ta jinjina kai kafin ta ɗan sauke numfashi
"Ehh.."