Sashe 116
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ameen Ameen.." Gwani ya faɗa, cikin ransa yana sake yi wa ɗan uwan nasa addu'a.
Yau ma kamar jiya, yini suka yi a asibitin, se dare sannan suka koma masaukinsu.
A kwanakin da suka biyo baya sosai Abeey ya soma samun sauƙi. Musamman da ya kasance kuɗi sosai Daddy ya zube wanda za a kula da Abeeyn sosai. Ta ɓangaren ma'auratan kuwa se ya zamana shaƙuwa ce sosai take sake shiga tsakanin kowannensu. I zuwa lokacin kowacce ta zage dantse wajen kula da mijinta, da kuma ƙoƙarin ganin ta farantawa mijinta. Sun kwashe sati biyu a asibitin kafin suka soma gabatar da ibada har da Abeey da jikinsa ya yi kyau sosai. Shi kansa ya ji daɗin jikinsa, ya kuma tabbatar yanzun da gaske yana samun sauƙi.
Ba su suka baro ƙasar ba se da jikin Abeey ya yi sauƙi sosai. Ya kasance an gama masa komai, an kuma ɗora shi a kan magani. Ta gefe guda kuma sun gama ibadarsu kafin suka baro ƙasar cike da kewa. Wadda ta gina musu tarihi masu wuyar mantawa. Lokacin da suka dawo kai tsaye tamfatsetsen haɗaɗɗen gidan da Daddy ya saka aka gina musu suka nufa. Haka su ma Abeey da Ummeey, na su haɗaɗɗen gidan suka nufa. Mommah da Daddy da kansu suka zo yi musu sannu da zuwa. Ganin jikin Abeey kuma ba ƙaramin faranta musu ya yi ba. Duk da da ma shi Daddy lokaci zuwa lokaci su kan yi waya ya ji jikin Abeeyn. Ta ɓangarensu Didi da Lulu kam shau shau da mai abinsu. Domin kuwa kowaccensu se da ta tarar da akwatinan da za a iya kiransu na lefe jibge a cikin ɗakinta. Akwatina haɗaɗɗu masu ɗauke da danƙara danƙaran kaya na gani na faɗa. Haka zalika hatta furniture sabbi aka zuba musu a sashe daban. Waɗancan ɗin nasu su ma nasu sashen daban. Takanas suka ɗauki jiki zuwa gidan Mommah dan yi musu godiya. Suna zaune a ƙasan carpet ɗin da ke shimfiɗe a tsakiyar ɗakin Daddyn. Murmushi Daddy ya yi kafin yace
"Ashe ma ku ba 'ya'yana ba ne.." Ya yi maganar kamar me tambaya ko kuma faɗa kawai ya yi. Dalilin da ya sa dukkansu suka ɗaga kai suka kalle shi kenan. Se kawai suka girgiza kai kusan a tare.
"Toh idan dai har haka ne mu cigaba da hirarmu.." Ya ƙare yana murmushi.
"Ni ma dai ta wajena haka ɗin ne." Mommah da tun ɗazu ba tace komai ba, yanzu ta faɗi hakan ita ma tana murmushin. Su ma murmushin suka yi dukkansu kowacce na ƙara yabawa da halin kirki irin na Daddy da Mommahn.
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. Kullum zaman lafiya da ƙaunar junansu ƙaruwa yake yi. Kowa ba shi da burin da ya wuce ya farantawa ɗan uwansa. I zuwa lokacin soyayyarsu suke sha babu kama hannun yaro. Ta gefe guda kuma lokaci ɗaya kowa na taya matarsa rainon ciki, cike da so, ƙauna da kuma tarairaya. Kwanaki na tafiya, satika na tafiya, suka haɗu suka bayar da watanni..
Daga haka se na ce mu haɗe a LAST PAGE 🎉😩😭💃
Ina yi wa kowa barka da sallah. Fatan an yi sallah cikin ƙoshin lafiya. Allah Ya mamaita mana.
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO84_85*
Last page 😩😭💃
____ Fitowarta kenan daga cikin kitchen ɗin Baba Atine ta yi sallama cikin ɗakin, hannunta ɗauke da abincin da kullum se Mommah ta saka ta kawo. Saboda Didin da jikinta ya ƙi ƙwari har yanzun. Aiki kaɗan za ta yi ta dinga haki da jiri kenan. Shi ya sa Mommah tace ta huta ta dena girkin, kullum daga gida ake kai na safe, rana da kuma dare. Didi ta amsa fuskarta ɗauke da murmushi.
"'Yata kar dai ki ce min girki kika yi?" Girgiza kai Didi ta yi tana ɗan lumshe idanunta, dan duk da ba wata daɗewa ta yi a tsaye ba amma jiri take ji. Girgiza kai ta yi tana sake ƙaƙalo murmushi ta wanzar a kan fuskarta kafin tace
"A'ah fa Baba Atine.."
"Toh zauna don Allah.." Ƙarasawa Didi ta yi ta nemi waje ta zauna tana ɗan sake lumshe idanunta. Ajiye abin da ta shigo da su Baba Atine ta yi. Kafin ta koma ta zauna kusa da Didi da ta sake yin wani kyau kamar me. Fuskarta ta yi wani irin luwai-luwai ta yi kyau abinta.
"Ba kya buƙatar komai?" Baba Atine ta tambaya tana kallan Didin. Girgiza kai Didi ta yi kana ta amsa da
"A'ah fa Baba ba na buƙatar komai." Daidai lokacin Bad Man ya sauko daga haɗaɗɗiyar matattakalar da ke cikin ɗakin, hannunsa ɗauke da waya kare a kunnensa, da alama waya yake yi. Miƙewa Baba Atine ta yi yana ƙarasowa suka gaisa cikin sakin fuska kamar koyaushe. Sallama ta yi da shi kafin ta wuce. Ya ƙarasa takowa zuwa cikin ɗakin. Be ankara ba Didi ta miƙe da niyyar kwashe abincin ta haura da su sama. Wani jiri da ya kwasheta ya tilasta mata komawa ta zauna a inda ta tashi.
"Ya salaam!." Ya faɗa yana ƙarasa zama kusa da ita hannunsa a kan nata hannun. Riƙe kanta ta yi idanunta a lumshe.
"Me ya sauko da ke ƙasa Uhmmm? Ba na hana ki sauka idan dai har ba na kusa ba?" Ya tambaya yana kallanta. Buɗe idanunta ta yi ta kalle shi kafin ta buɗe baki tace
"Ka yi haƙuri Babe, na yi laifi." Ɗaya daga cikin abin da ke sakawa ya sake jin Didin kane-kane cikin zuciyarsa shi ne taushin zuciya, da kuma saurin bayar da haƙuri ko da kuwa abu be kai ya kawo ba. Ya yi murmushi yana lumshe idanunsa. Komawa ya yi ya zauna kusa da ita sosai. Be ce komai ba se danna wayarsa da ya yi na tsawon wasu sakanni, kafin ya kafa a kunnensa.
"Mommah ko dai er aiki zan nemar mata?" Ya faɗa bayan sun gaisa da Mommahn. Murmushi Mommah ta yi kafin ta girgiza kai.
"Ba da ni ba Areef. Er aiki kam ba a gidan nan ba.. Idan dai kuna so zan iya ba ku Atine aro na wani lokaci.. Amma ka dena zancen er aikin nan." Shi ma da ma ya faɗa ne kawai be sani ba ko Mommahn ta sauya ra'ayi. Se dai be sani ba ashe har yanzu tana nan a kan bakarta.
"Toh shi kenan, hakan na mun gode sosai Mommah.. Allah Ya ƙara girma da lafiya."
"Ameen Areef." Daga haka ya ajje wayar gefensa. Ya maida dubansa kan Didi da ke kallansa. Ya yi dariya dan idan tana masa wannan kallan dariya take ba shi.
"Ki shirya dawowar Baba Atine sashen nan.."
"Kai Babe.." Hannunsa ya saka ya riƙe laɓɓanta guda biyu kafin yace
"Ba na son jin komai.. Babyn nan namu ba ya son wahala, ga yadda yake wahalar min da ke ko me kika yi. So gwara ki zauna ki huta ba se kin yi komai ba har ki haihu." Se da ta tura baki kafin tace
"Toh idan kuma garin hakan na zama ƙatuwa fa?" Ta ƙare yarintarta na bayyana. Dariya ya yi, kafin ya saka hannunsa ya juyo da fuskarta ta koma kallansa sosai
"Ko a ya ya kike ina son aba ta a haka.. Ni ke nake so." Ya yi maganar sounding seriously. Ta lumshe idanunta tana jin daɗin maganarsa. Yana shirin miƙewa daga zaman da ya yi wanda sam be masa daɗi ba tace
"Ka min wata alfarma." Ta faɗa tana riƙo hannunsa. Dawowa baya ya yi ya kafe ta da idanunsa, ya lumshe idanunsa cikin nata alamar yana ji.
"Ba na son sunan da wasu ke kiranka da shi." Buɗe idanunsa ya yi kafin yace
"Wanne?" Turo baki ta yi tana kallansa. Ya rausayar da kai gefe yana faɗin
"Da gaske fa.." Ya ƙare kamar wani maraya. Se da ta ɗan sake tura bakin kafin tace
"Bad Man!!" Murmushi ya yi kafin ya sauke ajiyar zuciya yana maida fuskarsa ta bar murmushin.
"In Allah Ya yarda daga yau an dena shi.." Ya faɗa cike da tabbatarwa. Dan ya san daga zarar ya nunawa duk masu kiransa da sunan ba ya so za su dena ko dan sanin halinsa.
"Don Allah da gaske?" Ta tambaya tana jin wani irin daɗi. Jinjina kai ya yi yana murmushi. Kawai se ta rungume shi sosai tana faɗin
"Na gode sosai Mijina.." haɗa ta ya yi da ƙaramin cikin nata da yanzun ya fito ya rungume, ya yi shiru abubuwa da dama na bijiro masa. Ya yi watsi da su yace
"Kin fi ƙarfin hakan Matata.."
Aikuwa washegari se ga Baba Atine da kayanta. Ɗaki ɗaya aka ware mata cikin ɗakunan da suke ƙasa. Nan ta sauka, aikuwa ranar Didi yini suka yi suna hira da Baba Atinen, saboda da ma da ƙyar yake fita wai yana tsoron kar ya barta ita ɗaya. Duk da Lulu na kusa, amma gani yake kowaccensu tana buƙatar kulawa ne ba ta kula da wata ba. Yau ɗin da Baba Atinen ta zo se ya samu nutsuwar fita daga gidan.
... A ɗaya ɓangaren kuwa da mamaki Gwani yake kallan cikin ɗakin. Be yi tsammanin ze ga ba ta cikin ɗakin ba kasancewar ya barta kwance kamar me shirin yin bacci. Da sauri ya fice daga ɗakin, kai tsaye kitchen ɗin saman ya nufa. Aikuwa kamar yadda ya tsammata tana ciki, tsaye take, ba ya iya hangen abin da yake yi se bayanta da yake hange. Tana sanye cikin ƙaramar riga mara hannu, se buɗaɗɗen skirt da ya ɗan tsuke daga sama kaɗan, kana ya buɗe sosai ta ƙasa. Kanta sanye cikin wata hula me taushi, wadda ta zame ta kusan rabin kanta a buɗe yake. Kan nata da ke a tsefe, a gyare kuma a kwance tsaff. Da sauri ya ƙarasa yana faɗin
"Ƙalb.." Dakatawa ta yi daga abin da take, ta juyo ta kalle shi. Ya girgiza kai yana faɗin
"Ba dai girki za ki ɗora ba?" Ɓata fuska ta yi tace kamar za ta yi kuka.
"Yunwa nake ji." Bin ta ya yi da kallo yanda take wani kwaɓe fuska kamar wadda ta ga tutu.
"Wancan ɗin ne ba kya ci ina koh?" Ya tambaya yana kallanta. Ta jinjina kai ita ma tana kallan nasa.
Yau ma kamar jiya, yini suka yi a asibitin, se dare sannan suka koma masaukinsu.
A kwanakin da suka biyo baya sosai Abeey ya soma samun sauƙi. Musamman da ya kasance kuɗi sosai Daddy ya zube wanda za a kula da Abeeyn sosai. Ta ɓangaren ma'auratan kuwa se ya zamana shaƙuwa ce sosai take sake shiga tsakanin kowannensu. I zuwa lokacin kowacce ta zage dantse wajen kula da mijinta, da kuma ƙoƙarin ganin ta farantawa mijinta. Sun kwashe sati biyu a asibitin kafin suka soma gabatar da ibada har da Abeey da jikinsa ya yi kyau sosai. Shi kansa ya ji daɗin jikinsa, ya kuma tabbatar yanzun da gaske yana samun sauƙi.
Ba su suka baro ƙasar ba se da jikin Abeey ya yi sauƙi sosai. Ya kasance an gama masa komai, an kuma ɗora shi a kan magani. Ta gefe guda kuma sun gama ibadarsu kafin suka baro ƙasar cike da kewa. Wadda ta gina musu tarihi masu wuyar mantawa. Lokacin da suka dawo kai tsaye tamfatsetsen haɗaɗɗen gidan da Daddy ya saka aka gina musu suka nufa. Haka su ma Abeey da Ummeey, na su haɗaɗɗen gidan suka nufa. Mommah da Daddy da kansu suka zo yi musu sannu da zuwa. Ganin jikin Abeey kuma ba ƙaramin faranta musu ya yi ba. Duk da da ma shi Daddy lokaci zuwa lokaci su kan yi waya ya ji jikin Abeeyn. Ta ɓangarensu Didi da Lulu kam shau shau da mai abinsu. Domin kuwa kowaccensu se da ta tarar da akwatinan da za a iya kiransu na lefe jibge a cikin ɗakinta. Akwatina haɗaɗɗu masu ɗauke da danƙara danƙaran kaya na gani na faɗa. Haka zalika hatta furniture sabbi aka zuba musu a sashe daban. Waɗancan ɗin nasu su ma nasu sashen daban. Takanas suka ɗauki jiki zuwa gidan Mommah dan yi musu godiya. Suna zaune a ƙasan carpet ɗin da ke shimfiɗe a tsakiyar ɗakin Daddyn. Murmushi Daddy ya yi kafin yace
"Ashe ma ku ba 'ya'yana ba ne.." Ya yi maganar kamar me tambaya ko kuma faɗa kawai ya yi. Dalilin da ya sa dukkansu suka ɗaga kai suka kalle shi kenan. Se kawai suka girgiza kai kusan a tare.
"Toh idan dai har haka ne mu cigaba da hirarmu.." Ya ƙare yana murmushi.
"Ni ma dai ta wajena haka ɗin ne." Mommah da tun ɗazu ba tace komai ba, yanzu ta faɗi hakan ita ma tana murmushin. Su ma murmushin suka yi dukkansu kowacce na ƙara yabawa da halin kirki irin na Daddy da Mommahn.
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. Kullum zaman lafiya da ƙaunar junansu ƙaruwa yake yi. Kowa ba shi da burin da ya wuce ya farantawa ɗan uwansa. I zuwa lokacin soyayyarsu suke sha babu kama hannun yaro. Ta gefe guda kuma lokaci ɗaya kowa na taya matarsa rainon ciki, cike da so, ƙauna da kuma tarairaya. Kwanaki na tafiya, satika na tafiya, suka haɗu suka bayar da watanni..
Daga haka se na ce mu haɗe a LAST PAGE 🎉😩😭💃
Ina yi wa kowa barka da sallah. Fatan an yi sallah cikin ƙoshin lafiya. Allah Ya mamaita mana.
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO84_85*
Last page 😩😭💃
____ Fitowarta kenan daga cikin kitchen ɗin Baba Atine ta yi sallama cikin ɗakin, hannunta ɗauke da abincin da kullum se Mommah ta saka ta kawo. Saboda Didin da jikinta ya ƙi ƙwari har yanzun. Aiki kaɗan za ta yi ta dinga haki da jiri kenan. Shi ya sa Mommah tace ta huta ta dena girkin, kullum daga gida ake kai na safe, rana da kuma dare. Didi ta amsa fuskarta ɗauke da murmushi.
"'Yata kar dai ki ce min girki kika yi?" Girgiza kai Didi ta yi tana ɗan lumshe idanunta, dan duk da ba wata daɗewa ta yi a tsaye ba amma jiri take ji. Girgiza kai ta yi tana sake ƙaƙalo murmushi ta wanzar a kan fuskarta kafin tace
"A'ah fa Baba Atine.."
"Toh zauna don Allah.." Ƙarasawa Didi ta yi ta nemi waje ta zauna tana ɗan sake lumshe idanunta. Ajiye abin da ta shigo da su Baba Atine ta yi. Kafin ta koma ta zauna kusa da Didi da ta sake yin wani kyau kamar me. Fuskarta ta yi wani irin luwai-luwai ta yi kyau abinta.
"Ba kya buƙatar komai?" Baba Atine ta tambaya tana kallan Didin. Girgiza kai Didi ta yi kana ta amsa da
"A'ah fa Baba ba na buƙatar komai." Daidai lokacin Bad Man ya sauko daga haɗaɗɗiyar matattakalar da ke cikin ɗakin, hannunsa ɗauke da waya kare a kunnensa, da alama waya yake yi. Miƙewa Baba Atine ta yi yana ƙarasowa suka gaisa cikin sakin fuska kamar koyaushe. Sallama ta yi da shi kafin ta wuce. Ya ƙarasa takowa zuwa cikin ɗakin. Be ankara ba Didi ta miƙe da niyyar kwashe abincin ta haura da su sama. Wani jiri da ya kwasheta ya tilasta mata komawa ta zauna a inda ta tashi.
"Ya salaam!." Ya faɗa yana ƙarasa zama kusa da ita hannunsa a kan nata hannun. Riƙe kanta ta yi idanunta a lumshe.
"Me ya sauko da ke ƙasa Uhmmm? Ba na hana ki sauka idan dai har ba na kusa ba?" Ya tambaya yana kallanta. Buɗe idanunta ta yi ta kalle shi kafin ta buɗe baki tace
"Ka yi haƙuri Babe, na yi laifi." Ɗaya daga cikin abin da ke sakawa ya sake jin Didin kane-kane cikin zuciyarsa shi ne taushin zuciya, da kuma saurin bayar da haƙuri ko da kuwa abu be kai ya kawo ba. Ya yi murmushi yana lumshe idanunsa. Komawa ya yi ya zauna kusa da ita sosai. Be ce komai ba se danna wayarsa da ya yi na tsawon wasu sakanni, kafin ya kafa a kunnensa.
"Mommah ko dai er aiki zan nemar mata?" Ya faɗa bayan sun gaisa da Mommahn. Murmushi Mommah ta yi kafin ta girgiza kai.
"Ba da ni ba Areef. Er aiki kam ba a gidan nan ba.. Idan dai kuna so zan iya ba ku Atine aro na wani lokaci.. Amma ka dena zancen er aikin nan." Shi ma da ma ya faɗa ne kawai be sani ba ko Mommahn ta sauya ra'ayi. Se dai be sani ba ashe har yanzu tana nan a kan bakarta.
"Toh shi kenan, hakan na mun gode sosai Mommah.. Allah Ya ƙara girma da lafiya."
"Ameen Areef." Daga haka ya ajje wayar gefensa. Ya maida dubansa kan Didi da ke kallansa. Ya yi dariya dan idan tana masa wannan kallan dariya take ba shi.
"Ki shirya dawowar Baba Atine sashen nan.."
"Kai Babe.." Hannunsa ya saka ya riƙe laɓɓanta guda biyu kafin yace
"Ba na son jin komai.. Babyn nan namu ba ya son wahala, ga yadda yake wahalar min da ke ko me kika yi. So gwara ki zauna ki huta ba se kin yi komai ba har ki haihu." Se da ta tura baki kafin tace
"Toh idan kuma garin hakan na zama ƙatuwa fa?" Ta ƙare yarintarta na bayyana. Dariya ya yi, kafin ya saka hannunsa ya juyo da fuskarta ta koma kallansa sosai
"Ko a ya ya kike ina son aba ta a haka.. Ni ke nake so." Ya yi maganar sounding seriously. Ta lumshe idanunta tana jin daɗin maganarsa. Yana shirin miƙewa daga zaman da ya yi wanda sam be masa daɗi ba tace
"Ka min wata alfarma." Ta faɗa tana riƙo hannunsa. Dawowa baya ya yi ya kafe ta da idanunsa, ya lumshe idanunsa cikin nata alamar yana ji.
"Ba na son sunan da wasu ke kiranka da shi." Buɗe idanunsa ya yi kafin yace
"Wanne?" Turo baki ta yi tana kallansa. Ya rausayar da kai gefe yana faɗin
"Da gaske fa.." Ya ƙare kamar wani maraya. Se da ta ɗan sake tura bakin kafin tace
"Bad Man!!" Murmushi ya yi kafin ya sauke ajiyar zuciya yana maida fuskarsa ta bar murmushin.
"In Allah Ya yarda daga yau an dena shi.." Ya faɗa cike da tabbatarwa. Dan ya san daga zarar ya nunawa duk masu kiransa da sunan ba ya so za su dena ko dan sanin halinsa.
"Don Allah da gaske?" Ta tambaya tana jin wani irin daɗi. Jinjina kai ya yi yana murmushi. Kawai se ta rungume shi sosai tana faɗin
"Na gode sosai Mijina.." haɗa ta ya yi da ƙaramin cikin nata da yanzun ya fito ya rungume, ya yi shiru abubuwa da dama na bijiro masa. Ya yi watsi da su yace
"Kin fi ƙarfin hakan Matata.."
Aikuwa washegari se ga Baba Atine da kayanta. Ɗaki ɗaya aka ware mata cikin ɗakunan da suke ƙasa. Nan ta sauka, aikuwa ranar Didi yini suka yi suna hira da Baba Atinen, saboda da ma da ƙyar yake fita wai yana tsoron kar ya barta ita ɗaya. Duk da Lulu na kusa, amma gani yake kowaccensu tana buƙatar kulawa ne ba ta kula da wata ba. Yau ɗin da Baba Atinen ta zo se ya samu nutsuwar fita daga gidan.
... A ɗaya ɓangaren kuwa da mamaki Gwani yake kallan cikin ɗakin. Be yi tsammanin ze ga ba ta cikin ɗakin ba kasancewar ya barta kwance kamar me shirin yin bacci. Da sauri ya fice daga ɗakin, kai tsaye kitchen ɗin saman ya nufa. Aikuwa kamar yadda ya tsammata tana ciki, tsaye take, ba ya iya hangen abin da yake yi se bayanta da yake hange. Tana sanye cikin ƙaramar riga mara hannu, se buɗaɗɗen skirt da ya ɗan tsuke daga sama kaɗan, kana ya buɗe sosai ta ƙasa. Kanta sanye cikin wata hula me taushi, wadda ta zame ta kusan rabin kanta a buɗe yake. Kan nata da ke a tsefe, a gyare kuma a kwance tsaff. Da sauri ya ƙarasa yana faɗin
"Ƙalb.." Dakatawa ta yi daga abin da take, ta juyo ta kalle shi. Ya girgiza kai yana faɗin
"Ba dai girki za ki ɗora ba?" Ɓata fuska ta yi tace kamar za ta yi kuka.
"Yunwa nake ji." Bin ta ya yi da kallo yanda take wani kwaɓe fuska kamar wadda ta ga tutu.
"Wancan ɗin ne ba kya ci ina koh?" Ya tambaya yana kallanta. Ta jinjina kai ita ma tana kallan nasa.