Sashe 113
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Didi.. Lulu.. Didi.. Lulu." Shi ne abin da yake ta faɗa cikin tsananin farin cikin ganinsu. Rungume shi suka yi a tare cike da kewarsa. Ita kanta Ammi murmushi ya ƙi barin fuskarta. Kallan 'ya'yan nata kawai take yi. Allah ne kaɗai ya san irin farin cikin da ta ji na ganinsu da ta yi. Sanda suka ƙaraso inda Ammi take, basu ɓata lokaci ba suka rungumeta. Tuni ƙwalla har ta cika idanun Ammi. Ta dai saurin maidata dan kar su ma ta karya musu zuciya.
"Ammi mun yi kewarki sosai." Didi ta faɗa. Lulu ta jinjina kai fuska a narke.
"Ni kaina yarana. Kun zo lafiya?" Ta tambaya cikin kulawa. Gaisawa sosai suka yi, shi dai Little ya yi shiru daga ya je jikin wannan, se ya koma jikin waccan. Ji yake kamar mafarki yake yau ma en uwansa ya sake ganinsu. Ga shi ma har sun dawo gida. Sosai yau ɗin ta kasance rana ta musamman a wajensu. Sun yi hira da Ammi sosai. Ta basu shawara, ta musu faɗa, ta kuma fahimci abubuwa da dama. Ciki kuwa har da cikin da Lulu ke ɗauke da shi. Ba su suka buɗi baki suka sanar da ita ba, amma duk wata alama ta me ciki ta gama bayyana a tattare da Lulun. Ga shi kuma ba ta iya cin dambun da Ammin da kanta ta tashi ta shirya musu ba, se da aka dafa mata wani abincin daban kafin ta iya ci. Ammi ta lumshe idanunta har cikin ranta tana jin farin ciki, musamman da ta ga alamar komai ya daidaitu tsakanin 'ya'yan nata da mazajensu. Se dai fatan Allah Ya ƙara musu zaman lafiya, ƙaunar juna da kwanciyar hankali me ɗorewa. Se da yamma sannan Lulu ta je gidansu Fatima Kabeer (Masoyiya). Kamar sa haɗiye juna saboda farin cikin ganin junansu. Haka suka zauna suna ta hira ta yaushe gamo. Se magribh sannan Masoyiyar ta rakota har gida kafin ta koma gida jiki duk ba daɗi. Ita kanta Lulu ji ta yi kamar kar su rabu, dan babu ƙarya sun yi kewar junansu.
Kasancewar Gwani ba ya nan, tun safe yana asibitin da Abeey yake, ya sa Bad Man ne ya wuce ɗauko su Didin. A harabar gidan ya tsaya yana jiran fitowarsu bayan ya shiga sun gaisa da Ammin. Ko a jikinsa, ganin Lulu da ya yi sun fito tare da Didi hakan be hana shi ƙarasawa inda take ba, ya yi azamar jawota jikinsa yana rungumewa.
"Sweetheart.." Ya faɗa yana lumshe idanunsa. Ita kam ji ta yi kamar ƙasa ta tsage ta shige dan kunya. Wanzuwar Lulu a wajen ita ce ta sanyata ji kamar ta fasa ihu. Shi kam da alama ko a jikinsa. Dan kuwa tana jikin nasa ya kalli Lulu da ke ƙoƙarin wuce su kamar ba ta gansu ba.
"Tweenienmu.." Ya yi maganar da ɗan murmushi a kan fuskarsa da yanzun lokuta da dama da wuya ka ganta a yanda ka san shi a da, musamman idan yana tare da Didi. Se a lokacin ta dakata ta ɗan yi murmushi cikin basarwa tace
"Barka da wannan lokaci Ya Areef."
"Barka dai.." Ya yi maganar yana sakin Didi.
"Thank God! Wannan mutumin!" Lulu ta faɗa a kan laɓɓanta, kafin ta fesar da iska daga cikin bakinta. Tura baki Didi ta yi dan ita kam ya gama bata kunya a gaban Lulu. Sarai ya lura da yanayinta, se dai ya basar kawai. Ya lura har yanzu ba ta gane yanda yake jinta a can ƙasan zuciyarsa ba ne. Kwata kwata ba ya ji ze iya ɓoye ƙaunarta da yake, musamman ma kuma da ya kasance a gaban er uwarta ne ba gaban wani can daban ba.
"Uncle.!" Ya jiyo muryar Little da ke tahowa wajen. Yana ƙarasowa ya rungume shi yana dariya. Hannu Bad Man ya saka ya ɗaga shi yana faɗin
"Areef!" Ya ƙare yana murmushi dan ba ƙarya ya yi kewar yaron shi kansa.
"Uncle kai ma ka dawo gidan nan?" Ya tambaya cike da farin ciki, dan shi a tunaninsa har su Didin ma sun dawo ne. Girgiza kai Bad Man ya yi kana yace
"A'ah na zo ne in ganka.. Amma zan dawo."
"Su Didi fa?" Ya tambaya yana buɗa baki kamar wani babba me wayo
"Su ma za su dawo."
"Kai!!" Ya faɗa yanayin fuskarsa na sauyawa. Se ma ya soma taɓe baki kamar ze yi kuka. Da sauri Bad Man yace
"Kar ka damu.. Za su dawo Uhmm?" Ya ƙare yana kallansa. Se ya jinjina kai a sanyaye. Bad Man ya ja kumatunsa yana faɗin
"That's my boy.. Oh yah, give me five!" Ya faɗa yana miƙa masa hannunsa. Se ya ba shi hannunsa suka tafa yana dariya. Se a lokacin sannan ya sauke shi yana faɗin
"Maza shiga gida.." Se da ya juya ya kalli Lulu da Didi da suke kallansa kamar za su yi kuka kafin ya tafi da gudu zuwa cikin gidan. Ajiyar zuciya ya sauke yana tashi tsaye sosai. Ya so ya samu ya gaisa da Abba, se dai har yanzun Abban be dawo ba. Dalili kenan da ya sanya ya haƙura kawai, da niyyar wani lokacin ya zo takanas ya gaishe da Abban.
Ita kam Lulu tamkar er kallo ta zama, dan ba ta taɓa tunanin Bad Man ɗin haka yake ba. Domin kuwa yanzun ma hannu ya saka ya buɗewa Didi ƙofar gidan gaba, ta juya da niyyar kallansa, ya marairaice fuska yana kauda kai ba tare da ya bari sun haɗa ido ba. Se ta juya da niyyar kallan Lulu, ita ma ta yi saurin janye idanunta tana basarwa. Bad Man da ke lura da duk abin da take ya yi murmushi har fararen haƙoransa na bayyana. Kawai se ta shiga ciki, ya kulle ƙofar kafin ya zagaya. Se a lokacin ya juya ya kalli Lulu yace
"Matar ɗan uwa mu wuce koh?" Se ta jinjina kai tana ƙarasowa ta shiga cikin motar. Babu ɓata lokaci ya ja motar suka fice daga cikin gidan. Ko a cikin motar ma duk da driving yake, hakan be hana shi kamo hannun Didi cikin nasa ba. Duk da yanda take ɗan ta babbasarwa saboda wanzuwar Lulu a wajen amma shi ko a jikinsa. Da dai ta ga babu sarki se Allah kawai se ta yi shiru, ta saki hannun nata, ya kuwa riƙe gam idanunsa na kan titi. Sosai Lulu ta ji daɗin hakan, ko babu komai ta san Didin tata ta samu mijin da ke ƙaunarta. Ba ma ita kaɗai ba dukkansu sun samu masu ƙaunarsu. Kawai se ta ji tana kewar nata mijin, ta lumshe idanunta tana jin wani murmushi na ƙwace mata. Yana ida parking na motarsa driver ma na parking motar da ya ɗauki Gwani ciki. Don haka kusan a tare suka sauka. Idanun Gwani na kan inda ze hango tauraruwar tasa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa ya hangota ta yi kyau, tamkar wadda ta gama shiri yanzun. Ya saki murmushi yana jin wani sanyi na ratsa shi. Yau ɗin da ya wuni be ganta ba duk se yake jinsa tamkar mara lafiya, yanzun kam da ya ganta se yake jinsa zam-zam.
"Ina fata dai ba ka wujijjiga min mata da ɗa ba da wannan driving ɗin naka." Gwani ya faɗa lokacin da ya ƙaraso inda suke idanunsa a kan Bad Man. Buɗe ido ya yi kafin yace
"Umm lallai ka ga me mata da ɗa.. Toh tambayeta mana." Ya ƙare yana rungume hannunsa a ƙirji yana maida dubansa kan Lulu. Jinjina kai Gwani ya yi kafin ya shiga takawa zuwa inda Lulu take. Se ta soma ɗaga kai tana kallan Bad Man da Didi da ke kallansu. Fatanta da addu'arta kawai Allah Ya sa kar yace ze riƙota ko wani abun. Cikin ikon Allah kuwa addu'arta ta karɓu, dan kuwa ƙarasowa ya yi se dai dab da ita. Ya zuba mata idanunsa, ita ma kuma shi take kalla. A hankali kamar me raɗa yace
"Ina fata dai be wahalar min da ku ba?" Har ta buɗe baki cike da mamaki da niyyar tambayar ita da wa? Se kuma murmushi ya ƙwace a kan fuskarta. Ta jinjina kai a hankali tana faɗin
"Ehh.." Juyawa Gwani ya yi yana murmushi, idanunsa a kan Bad Man yace
"Allah Ya taimake ka." Dariya Bad Man har ma da Didi suka yi, dan babu ƙarya abun ya burgesu. Musamman irin kallan da suke bin junansu da shi ɗazun, wanda kallan farko za ka karanto irin soyayyar da kowannensu ke wa ɗan uwansa.
.. Ba a ɗauki lokaci me tsayi ba, shirye-shiryen tafiyarsu Saudiyya komai ya kankama. Dan haka suka sake yin sallama da dangi na kusa kafin suka kama hanya se ƙasa me tsarki. Kowa na yi musu fatan alkhairi, da fatan a yi ibada lafiya, a kuma samu nasara a rashin lafiyar Abeey. A ranar da suka sauka kai tsaye asibitin suka fara wucewa. A kusa da asibitin kuma akwai hotel, a nan suka kama ɗakuna biyu da za su zauna. Kama ɗakin kawai suka yi, suka bar Didi da Lulu. Ya yin da su kuma suka koma asibitin dan ƙarasa duk wasu abubuwa da suka kamata saboda kasancewar yau ɗin shi ne zuwansu na farko. A can asibitin da ma suka bar Ummeey. Dan haka inda suka barta a nan suka zo suka sameta.
"Ina kuka bar 'ya'yan nawa?" Ummeey ta tambaya tana kallansu su duka.
"Yanzu haka suna cikin ɗakin hotel ɗin da ke kusa da asibitin nan Ummeey.. Idan ki na buƙatar wani abu se mu je a raka ki." Bad Man ne ya ba wa Ummeey wannan amsar. Ta yi murmushi kafin ta amsa da
"Toh madallah.." Suna nan zaune suna jiran shigowar wanda Daddy ya haɗa su da shi Abeey da ke kishingiɗe a kan gadon ɗakin ya kalli Gwani yace
"Kun dai dage se na samu lafiya." Ya ƙare yana kallan Gwani da ya san ya fi kowa shiga damuwa idan ba shi da lafiya.
"Abeey bayan lafiyar ma kuma, ai ka ga babban abun da ya kawo mu shi ne ziyartar ɗakin Allah." Murmushi Abeey ya yi kafin ya amsa da
"Ammi mun yi kewarki sosai." Didi ta faɗa. Lulu ta jinjina kai fuska a narke.
"Ni kaina yarana. Kun zo lafiya?" Ta tambaya cikin kulawa. Gaisawa sosai suka yi, shi dai Little ya yi shiru daga ya je jikin wannan, se ya koma jikin waccan. Ji yake kamar mafarki yake yau ma en uwansa ya sake ganinsu. Ga shi ma har sun dawo gida. Sosai yau ɗin ta kasance rana ta musamman a wajensu. Sun yi hira da Ammi sosai. Ta basu shawara, ta musu faɗa, ta kuma fahimci abubuwa da dama. Ciki kuwa har da cikin da Lulu ke ɗauke da shi. Ba su suka buɗi baki suka sanar da ita ba, amma duk wata alama ta me ciki ta gama bayyana a tattare da Lulun. Ga shi kuma ba ta iya cin dambun da Ammin da kanta ta tashi ta shirya musu ba, se da aka dafa mata wani abincin daban kafin ta iya ci. Ammi ta lumshe idanunta har cikin ranta tana jin farin ciki, musamman da ta ga alamar komai ya daidaitu tsakanin 'ya'yan nata da mazajensu. Se dai fatan Allah Ya ƙara musu zaman lafiya, ƙaunar juna da kwanciyar hankali me ɗorewa. Se da yamma sannan Lulu ta je gidansu Fatima Kabeer (Masoyiya). Kamar sa haɗiye juna saboda farin cikin ganin junansu. Haka suka zauna suna ta hira ta yaushe gamo. Se magribh sannan Masoyiyar ta rakota har gida kafin ta koma gida jiki duk ba daɗi. Ita kanta Lulu ji ta yi kamar kar su rabu, dan babu ƙarya sun yi kewar junansu.
Kasancewar Gwani ba ya nan, tun safe yana asibitin da Abeey yake, ya sa Bad Man ne ya wuce ɗauko su Didin. A harabar gidan ya tsaya yana jiran fitowarsu bayan ya shiga sun gaisa da Ammin. Ko a jikinsa, ganin Lulu da ya yi sun fito tare da Didi hakan be hana shi ƙarasawa inda take ba, ya yi azamar jawota jikinsa yana rungumewa.
"Sweetheart.." Ya faɗa yana lumshe idanunsa. Ita kam ji ta yi kamar ƙasa ta tsage ta shige dan kunya. Wanzuwar Lulu a wajen ita ce ta sanyata ji kamar ta fasa ihu. Shi kam da alama ko a jikinsa. Dan kuwa tana jikin nasa ya kalli Lulu da ke ƙoƙarin wuce su kamar ba ta gansu ba.
"Tweenienmu.." Ya yi maganar da ɗan murmushi a kan fuskarsa da yanzun lokuta da dama da wuya ka ganta a yanda ka san shi a da, musamman idan yana tare da Didi. Se a lokacin ta dakata ta ɗan yi murmushi cikin basarwa tace
"Barka da wannan lokaci Ya Areef."
"Barka dai.." Ya yi maganar yana sakin Didi.
"Thank God! Wannan mutumin!" Lulu ta faɗa a kan laɓɓanta, kafin ta fesar da iska daga cikin bakinta. Tura baki Didi ta yi dan ita kam ya gama bata kunya a gaban Lulu. Sarai ya lura da yanayinta, se dai ya basar kawai. Ya lura har yanzu ba ta gane yanda yake jinta a can ƙasan zuciyarsa ba ne. Kwata kwata ba ya ji ze iya ɓoye ƙaunarta da yake, musamman ma kuma da ya kasance a gaban er uwarta ne ba gaban wani can daban ba.
"Uncle.!" Ya jiyo muryar Little da ke tahowa wajen. Yana ƙarasowa ya rungume shi yana dariya. Hannu Bad Man ya saka ya ɗaga shi yana faɗin
"Areef!" Ya ƙare yana murmushi dan ba ƙarya ya yi kewar yaron shi kansa.
"Uncle kai ma ka dawo gidan nan?" Ya tambaya cike da farin ciki, dan shi a tunaninsa har su Didin ma sun dawo ne. Girgiza kai Bad Man ya yi kana yace
"A'ah na zo ne in ganka.. Amma zan dawo."
"Su Didi fa?" Ya tambaya yana buɗa baki kamar wani babba me wayo
"Su ma za su dawo."
"Kai!!" Ya faɗa yanayin fuskarsa na sauyawa. Se ma ya soma taɓe baki kamar ze yi kuka. Da sauri Bad Man yace
"Kar ka damu.. Za su dawo Uhmm?" Ya ƙare yana kallansa. Se ya jinjina kai a sanyaye. Bad Man ya ja kumatunsa yana faɗin
"That's my boy.. Oh yah, give me five!" Ya faɗa yana miƙa masa hannunsa. Se ya ba shi hannunsa suka tafa yana dariya. Se a lokacin sannan ya sauke shi yana faɗin
"Maza shiga gida.." Se da ya juya ya kalli Lulu da Didi da suke kallansa kamar za su yi kuka kafin ya tafi da gudu zuwa cikin gidan. Ajiyar zuciya ya sauke yana tashi tsaye sosai. Ya so ya samu ya gaisa da Abba, se dai har yanzun Abban be dawo ba. Dalili kenan da ya sanya ya haƙura kawai, da niyyar wani lokacin ya zo takanas ya gaishe da Abban.
Ita kam Lulu tamkar er kallo ta zama, dan ba ta taɓa tunanin Bad Man ɗin haka yake ba. Domin kuwa yanzun ma hannu ya saka ya buɗewa Didi ƙofar gidan gaba, ta juya da niyyar kallansa, ya marairaice fuska yana kauda kai ba tare da ya bari sun haɗa ido ba. Se ta juya da niyyar kallan Lulu, ita ma ta yi saurin janye idanunta tana basarwa. Bad Man da ke lura da duk abin da take ya yi murmushi har fararen haƙoransa na bayyana. Kawai se ta shiga ciki, ya kulle ƙofar kafin ya zagaya. Se a lokacin ya juya ya kalli Lulu yace
"Matar ɗan uwa mu wuce koh?" Se ta jinjina kai tana ƙarasowa ta shiga cikin motar. Babu ɓata lokaci ya ja motar suka fice daga cikin gidan. Ko a cikin motar ma duk da driving yake, hakan be hana shi kamo hannun Didi cikin nasa ba. Duk da yanda take ɗan ta babbasarwa saboda wanzuwar Lulu a wajen amma shi ko a jikinsa. Da dai ta ga babu sarki se Allah kawai se ta yi shiru, ta saki hannun nata, ya kuwa riƙe gam idanunsa na kan titi. Sosai Lulu ta ji daɗin hakan, ko babu komai ta san Didin tata ta samu mijin da ke ƙaunarta. Ba ma ita kaɗai ba dukkansu sun samu masu ƙaunarsu. Kawai se ta ji tana kewar nata mijin, ta lumshe idanunta tana jin wani murmushi na ƙwace mata. Yana ida parking na motarsa driver ma na parking motar da ya ɗauki Gwani ciki. Don haka kusan a tare suka sauka. Idanun Gwani na kan inda ze hango tauraruwar tasa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa ya hangota ta yi kyau, tamkar wadda ta gama shiri yanzun. Ya saki murmushi yana jin wani sanyi na ratsa shi. Yau ɗin da ya wuni be ganta ba duk se yake jinsa tamkar mara lafiya, yanzun kam da ya ganta se yake jinsa zam-zam.
"Ina fata dai ba ka wujijjiga min mata da ɗa ba da wannan driving ɗin naka." Gwani ya faɗa lokacin da ya ƙaraso inda suke idanunsa a kan Bad Man. Buɗe ido ya yi kafin yace
"Umm lallai ka ga me mata da ɗa.. Toh tambayeta mana." Ya ƙare yana rungume hannunsa a ƙirji yana maida dubansa kan Lulu. Jinjina kai Gwani ya yi kafin ya shiga takawa zuwa inda Lulu take. Se ta soma ɗaga kai tana kallan Bad Man da Didi da ke kallansu. Fatanta da addu'arta kawai Allah Ya sa kar yace ze riƙota ko wani abun. Cikin ikon Allah kuwa addu'arta ta karɓu, dan kuwa ƙarasowa ya yi se dai dab da ita. Ya zuba mata idanunsa, ita ma kuma shi take kalla. A hankali kamar me raɗa yace
"Ina fata dai be wahalar min da ku ba?" Har ta buɗe baki cike da mamaki da niyyar tambayar ita da wa? Se kuma murmushi ya ƙwace a kan fuskarta. Ta jinjina kai a hankali tana faɗin
"Ehh.." Juyawa Gwani ya yi yana murmushi, idanunsa a kan Bad Man yace
"Allah Ya taimake ka." Dariya Bad Man har ma da Didi suka yi, dan babu ƙarya abun ya burgesu. Musamman irin kallan da suke bin junansu da shi ɗazun, wanda kallan farko za ka karanto irin soyayyar da kowannensu ke wa ɗan uwansa.
.. Ba a ɗauki lokaci me tsayi ba, shirye-shiryen tafiyarsu Saudiyya komai ya kankama. Dan haka suka sake yin sallama da dangi na kusa kafin suka kama hanya se ƙasa me tsarki. Kowa na yi musu fatan alkhairi, da fatan a yi ibada lafiya, a kuma samu nasara a rashin lafiyar Abeey. A ranar da suka sauka kai tsaye asibitin suka fara wucewa. A kusa da asibitin kuma akwai hotel, a nan suka kama ɗakuna biyu da za su zauna. Kama ɗakin kawai suka yi, suka bar Didi da Lulu. Ya yin da su kuma suka koma asibitin dan ƙarasa duk wasu abubuwa da suka kamata saboda kasancewar yau ɗin shi ne zuwansu na farko. A can asibitin da ma suka bar Ummeey. Dan haka inda suka barta a nan suka zo suka sameta.
"Ina kuka bar 'ya'yan nawa?" Ummeey ta tambaya tana kallansu su duka.
"Yanzu haka suna cikin ɗakin hotel ɗin da ke kusa da asibitin nan Ummeey.. Idan ki na buƙatar wani abu se mu je a raka ki." Bad Man ne ya ba wa Ummeey wannan amsar. Ta yi murmushi kafin ta amsa da
"Toh madallah.." Suna nan zaune suna jiran shigowar wanda Daddy ya haɗa su da shi Abeey da ke kishingiɗe a kan gadon ɗakin ya kalli Gwani yace
"Kun dai dage se na samu lafiya." Ya ƙare yana kallan Gwani da ya san ya fi kowa shiga damuwa idan ba shi da lafiya.
"Abeey bayan lafiyar ma kuma, ai ka ga babban abun da ya kawo mu shi ne ziyartar ɗakin Allah." Murmushi Abeey ya yi kafin ya amsa da