Sashe 29
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Uhmm.. Ki faɗa mata ni na saka ki.. Maza je ki.." Har ranta ba ta ji daɗi ba, ta so da kan shi ze yi wa Didin magana ko babu komai sa ɗan soma magana. Se dai kuma tunda har aka zo nan ɗin ta san In Sha Allah za a zo inda suke fata.
"Toh.." ta faɗa tana juyawa zuwa ciki. A cikin ɗakin ta tarar da Didin tana kwance idanunta a buɗe, da alama tunani take yi. Da murmushi Atine ta ƙarasa tana faɗin
"Tashi ɗiyata.." Babu musu ta miƙe ɗin tana kallan Baba Atinen.
"Kin san me ya faru? Ina tunanin Allah ya karɓi addu'o'inmu.. Yanzun nan Areef ke ce min na faɗa miki ki dinga kai masa Coffee safe da dare.. Kin ga wannan ɗin ai matakin nasara ne.." Tura ɗan ƙaramin bakinta ta yi tana tuna rashin kirkin da ya yi mata, shi ne kuma yanzu ze wani aiko a faɗa mata ta dinga kai masa Coffee. Lallai ma wannan mutumin.
"Baba Atine Amma fa shi ne ya koro ni shi ya sa na dena.." ta ƙare dai cikin tura bakin. Murmushi Atine ta yi tace bayan ta riƙo hannun Didi
"Ki yi haƙuri ɗiyata.. In Sha Allah komai ze wuce, na san abun da ciwo amma ki daure wataran ze zama tarihi kin ji?" Jinjina kai kawai Didi har ranta tana jin babu daɗi, dan wukaƙancin da ya mata har yanzu ba ta manta ba. Hango angry fuskar nan tasa ta yi lokacin da yana faɗa mata magana, ta murguɗa baki a kan laɓɓanta ta furta
"Mutum se baƙin hali da son wukaƙanta wani.."
.. Kafin ya ƙarasa parking space wayarsa ta shiga ruri, be damu da hakan ba ya cigaba da takawa ya shige cikin wata hamshaƙiyar mota. Se a lokacin ya fito da wayar tasa yana shirin ajjewa wani kiran ya shigo. Ganin me kiran ne ya sanya shi jinginar da kansa jikin kujera ya kara a kunnensa.
"Ka na ina?"
"Ina gida.."
"Ka zo ina parlourna.." Daddy ya faɗa. Kamar yace fita ze yi se dai kawai ya amsa da
"Toh" yana katse wayar.
Daddy na zaune a kan kujera yayin da Mom ma ke zaune kan kujera suna ɗan taɓa hira. Ta saki murmushi lokacin da ta ga Bad Man ɗin ya shigo. Ya nemi waje ya zauna, bayan sun gaisa Daddy ya kalli Mom yace
"Za ki iya ba mu waje.."
"Haba Rankayadaɗe.. Yanzu magana ma da ɗana a ce se ba na wajen za a yita?" Ta faɗa tana buɗe idanu cike da iyayi kamar ƙaramar yarinya. Girgiza kai Daddy ya yi yana faɗin
"Kaiii.." Se kuma ya ɗora da
"Toh ba se kin saka mana baki ba"
"Ba zan saka ba." Ta faɗa tana gyara zama. Maida dubansa kan Bad Man Daddy ya yi yace
"Ya aikin? Ya kuma matar taka?" Jin tambayar ya yi kamar wani saɓo, hakan ne ya sanya shi ɗan taɓe baki yace cikin basarwa
"Aiki Alhamdulillah.."
"Wajen matar taka fa?" Daddy ya tambaya yana kallansa, jin da ya yi ya basar da tambayar. Da sauri Mom tace
"Amma ai se da soyayya ake sanin wannan koh?" Wani kallo Daddy ya watsa mata irin na gargaɗi, wanda shi ne ya tunasar da ita ɓaran ɓaramar da take shirin yi. Duk da irin gargaɗin da Aunt Makiyy ta yi mata amma tana ƙoƙarin ta basu matsala da shegen bakin nan nata.
"Tashi ka je.. Zan neme ka." Daddy ya faɗa yana kallan Bad Man.
"A huta lafiya.." ya faɗa yana maida dubansa kan Mom dake zaune kamar an dasata ta kasa kallan kowa yace
"Bye Mom.." Daga haka ya fice daga ɗakin. Miƙewa kawai Daddy ya yi ya bar parlourn ba tare da yace da ita komai ba. Duk se ta sha jinin jikinta, lallai idan ba ta yi a hankali ba za ta janyo wannan matsalar ta jima musu ba tare da sun yi maganinta ba.
... "Ki fito Abba na jiranki.." Wannan kalmar se da ta kusa tafiya da numfashinta. Ta juya da niyyar yi wa Gwanin magana se dai tuni ya fice daga ɗakin. Ta juya ta kalli gefe, ta sake kallan gefe kamar me neman wani abun. Shi kenan ita kam yau tata ta ƙare, ta shiga uku ta lalace. Mami ta gama da ita, Mami ta cuceta ta taƙaici rayuwarta. Duk soyayyar da take mata amma ta rasa da abin da za ta saka mata se wannan. Me ya sa Mamin ta mata haka? Miƙewa ta yi duk da yanda jiri ke ɗan ɗibarta, hakan be hanata miƙewa ba tana hana kanta fitowar kukan da ya tsaya mata. A hankali ta shiga takawa, dama ba wani jiki ke gareta ba, ga kuma jirin dake kwasarta, se take ji kamar iska za ta kwasheta saboda yanda take kaɗata kamar wata bishiya. A ƙofar ɗakin ta tarar da Gwani. Fitowarta da ya gani ya sanya shi yin gaba. Ganin haka ne ya sanyata bin bayansa tana sauke numfashi da sauri da sauri kamar me shirin fashewa da kuka. Da sallama ya shiga cikin ɗakin, tana biye a bayansa, ba ta san lokacin da ta zube a ƙasa ba tana runtse idanunta. Fita Gwani ya yi daga ɗakin ya rage daga Abba se Little a cikin ɗakin. Little ya kalli Abba yace
"Abba Lulu se kuka take yi.." Da mamaki Abba ya kalli Lulu, daidai lokacin da ta yi ƙarfin halin faɗin
"Abba sannu da zuwa.." ta faɗa tana jira ta ji ta inda Abban ze fara. Se dai ga mamakinta se ji ta yi yace
"Ashe har yanzu ba ki kwantar da hankalinki a kan auren nan ba Afaaf? So kike ki ɗorawa kanki damuwa koh? Ashe ban isa na yanke hukunci a kan ki ba? Har yanzu kin kasa haƙuri ki karɓi zaɓin da na miki? Shi ne kika zauna ki na ta kuka kenan har yanzu ba ki haƙura ba? Afaaf ashe ban isa dake ba.." Da mamaki ta ɗaga jajayen idanunta ta kalli Abba, se ta shiga girgiza kai, sannan ta soma faɗin
"Abba wallahi na haƙura.. na haƙura wallahi.. Abba ka isa da ni don Allah ka yi haƙuri ka min afuwa. Na haƙura wallahi Abba, ba zan sake kukan ba." Ta faɗa tana kai hannunta kan fuskarta ta shiga goge hawayen fuskar tata.
"Allah ya yi miki albarka. Allah ya ba ku zaman lafiya.. Allah ya miki albarka.." ya faɗa cikin matuƙar jin daɗin abin da ya fito daga bakin Lulun. Ita kam ba ta kuma san me za tace bayan wannan ba, ta riga ta san tsana ce a tsakaninta da Gwani, se dai daga ɗazu zuwa yanzu ta ji tsanar tasa ta ragu a cikin zuciyarta. Ta riga ta san har abada ba za ta so shi ba se dai tunda har ya iya ɓoye abin da ya faru ba tare da ya faɗawa Abba ba ita me iya cigaba da zama cikin gidan ne, ko babu komai ta bi umarnin Abbanta ta kuma cigaba da zama da Gwanin har lokacin da ze gano gaskiyar abin da ya faru. Ya gane ita ɗin ba yadda yake tunani ba ce. Da ƙyar ta iya amsawa da "Ameen" da dashashshiyar muryarta. Babu laifi sun ɗan taɓa hira, duk da hirar duk amfani da hakan Abba ya yi wajen sake yi mata faɗa sosai a kan zaman auren. Ita kuwa ba wani sosai take fahimta ba saboda har lokacin hankalinta a tashe yake, zuciyarta kuma ta kasa hutawa da tunanin yanda za ta fahimtar da Gwani gaskiyar al'amari.
"Toh bari mu tashi mu tafi.. Zan kuma tafi da Little kin san gobe za a koma makaranta.. Idan kuma aka yi hutun da za a yi nan da en kwanaki ze je wajen Didi.." Kallan Little ta yi tana jin sam babu daɗi, se dai dama ta san dole ze tafi. Don haka tace
"Toh Abba.. a gaida min da Ammina.. Sannan kuma ina so na yi waya da Didi don Allah.." ta faɗa da muryarta dake rawa.
"Babu damuwa.. ki faɗawa mijin naki idan ya amince ranar da za a kawo muku kayan ɗakin ku se a haɗo miki da wayar.. Ko kuma ma dai za mu yi magana da shi kawai, zan ba shi number da za a sameta se ku yi magana." Har ranta ta ji wani irin sanyi, ko babu komai za ta samu su tattauna da er uwarta a kan wannan abun.
... Tana takure a kan gadon dan ta kaasa sake gwada shiga ɗakin nan. Tana jin lokacin da ya shigo ɗakin, ta ɗauka ko ze sake mata maganar ne ta masa bayani amma ta ji shiru, dan shi tunda ya shigo ɗakin ya nemi waje ya zauna ba tare da ya kalli inda take ba.
"Kenan ya yadda hakan nake?" Ta tambayi kanta cikin karyewar zuciya. Hakan da ta raya a cikin zuciyarta shi ne ya sanya zuciyarta saurin karyewa, se ta shiga sauke ajiyar zuciya alamar kuka take shirin yi. Kukan da yanzu ba ya yi mata wuya.
Daga inda yake zaune yana jin yanda take jan sheshsheƙa a hankali, kamar ya share se kuma ya ga rashin dacewar hakan. Bayan kusan minti 1 ya miƙe a nutse ya soma takawa. Hannu ya saka ya yaye labulen idanunsa a kan gadon, jin motsinsa ne ya sanyata saurin tashi zaune a kan gadon ta kalle shi da fuskarta da ta zama kalar tausayi. Ita burinta ɗaya kawai ya fuskanceta, ya fahimci abin da take nufi, ya fahimci abin da ya gani ba shi ne gaskiya ba, wani ne yake son ɓata masa suna, wanda ba ta san waye shi ba. Kuma saboda tsabar ruɗewa ma ba ta taɓa kawowa kanta idan aka nemo Mami za a ji daga ainahin inda komai ya fito ba. Ƙarasawa ya yi cikin nutsuwar dai ya nemi gefen gadon ya zauna yana kallanta yace
"Kukan fa?" Ya faɗa a nutse kamar babu abin da ke faruwa. Kai ta girgiza lokacin da wasu sabbin hawayen suka zubo a kan kuncinta tace
"Toh.." ta faɗa tana juyawa zuwa ciki. A cikin ɗakin ta tarar da Didin tana kwance idanunta a buɗe, da alama tunani take yi. Da murmushi Atine ta ƙarasa tana faɗin
"Tashi ɗiyata.." Babu musu ta miƙe ɗin tana kallan Baba Atinen.
"Kin san me ya faru? Ina tunanin Allah ya karɓi addu'o'inmu.. Yanzun nan Areef ke ce min na faɗa miki ki dinga kai masa Coffee safe da dare.. Kin ga wannan ɗin ai matakin nasara ne.." Tura ɗan ƙaramin bakinta ta yi tana tuna rashin kirkin da ya yi mata, shi ne kuma yanzu ze wani aiko a faɗa mata ta dinga kai masa Coffee. Lallai ma wannan mutumin.
"Baba Atine Amma fa shi ne ya koro ni shi ya sa na dena.." ta ƙare dai cikin tura bakin. Murmushi Atine ta yi tace bayan ta riƙo hannun Didi
"Ki yi haƙuri ɗiyata.. In Sha Allah komai ze wuce, na san abun da ciwo amma ki daure wataran ze zama tarihi kin ji?" Jinjina kai kawai Didi har ranta tana jin babu daɗi, dan wukaƙancin da ya mata har yanzu ba ta manta ba. Hango angry fuskar nan tasa ta yi lokacin da yana faɗa mata magana, ta murguɗa baki a kan laɓɓanta ta furta
"Mutum se baƙin hali da son wukaƙanta wani.."
.. Kafin ya ƙarasa parking space wayarsa ta shiga ruri, be damu da hakan ba ya cigaba da takawa ya shige cikin wata hamshaƙiyar mota. Se a lokacin ya fito da wayar tasa yana shirin ajjewa wani kiran ya shigo. Ganin me kiran ne ya sanya shi jinginar da kansa jikin kujera ya kara a kunnensa.
"Ka na ina?"
"Ina gida.."
"Ka zo ina parlourna.." Daddy ya faɗa. Kamar yace fita ze yi se dai kawai ya amsa da
"Toh" yana katse wayar.
Daddy na zaune a kan kujera yayin da Mom ma ke zaune kan kujera suna ɗan taɓa hira. Ta saki murmushi lokacin da ta ga Bad Man ɗin ya shigo. Ya nemi waje ya zauna, bayan sun gaisa Daddy ya kalli Mom yace
"Za ki iya ba mu waje.."
"Haba Rankayadaɗe.. Yanzu magana ma da ɗana a ce se ba na wajen za a yita?" Ta faɗa tana buɗe idanu cike da iyayi kamar ƙaramar yarinya. Girgiza kai Daddy ya yi yana faɗin
"Kaiii.." Se kuma ya ɗora da
"Toh ba se kin saka mana baki ba"
"Ba zan saka ba." Ta faɗa tana gyara zama. Maida dubansa kan Bad Man Daddy ya yi yace
"Ya aikin? Ya kuma matar taka?" Jin tambayar ya yi kamar wani saɓo, hakan ne ya sanya shi ɗan taɓe baki yace cikin basarwa
"Aiki Alhamdulillah.."
"Wajen matar taka fa?" Daddy ya tambaya yana kallansa, jin da ya yi ya basar da tambayar. Da sauri Mom tace
"Amma ai se da soyayya ake sanin wannan koh?" Wani kallo Daddy ya watsa mata irin na gargaɗi, wanda shi ne ya tunasar da ita ɓaran ɓaramar da take shirin yi. Duk da irin gargaɗin da Aunt Makiyy ta yi mata amma tana ƙoƙarin ta basu matsala da shegen bakin nan nata.
"Tashi ka je.. Zan neme ka." Daddy ya faɗa yana kallan Bad Man.
"A huta lafiya.." ya faɗa yana maida dubansa kan Mom dake zaune kamar an dasata ta kasa kallan kowa yace
"Bye Mom.." Daga haka ya fice daga ɗakin. Miƙewa kawai Daddy ya yi ya bar parlourn ba tare da yace da ita komai ba. Duk se ta sha jinin jikinta, lallai idan ba ta yi a hankali ba za ta janyo wannan matsalar ta jima musu ba tare da sun yi maganinta ba.
... "Ki fito Abba na jiranki.." Wannan kalmar se da ta kusa tafiya da numfashinta. Ta juya da niyyar yi wa Gwanin magana se dai tuni ya fice daga ɗakin. Ta juya ta kalli gefe, ta sake kallan gefe kamar me neman wani abun. Shi kenan ita kam yau tata ta ƙare, ta shiga uku ta lalace. Mami ta gama da ita, Mami ta cuceta ta taƙaici rayuwarta. Duk soyayyar da take mata amma ta rasa da abin da za ta saka mata se wannan. Me ya sa Mamin ta mata haka? Miƙewa ta yi duk da yanda jiri ke ɗan ɗibarta, hakan be hanata miƙewa ba tana hana kanta fitowar kukan da ya tsaya mata. A hankali ta shiga takawa, dama ba wani jiki ke gareta ba, ga kuma jirin dake kwasarta, se take ji kamar iska za ta kwasheta saboda yanda take kaɗata kamar wata bishiya. A ƙofar ɗakin ta tarar da Gwani. Fitowarta da ya gani ya sanya shi yin gaba. Ganin haka ne ya sanyata bin bayansa tana sauke numfashi da sauri da sauri kamar me shirin fashewa da kuka. Da sallama ya shiga cikin ɗakin, tana biye a bayansa, ba ta san lokacin da ta zube a ƙasa ba tana runtse idanunta. Fita Gwani ya yi daga ɗakin ya rage daga Abba se Little a cikin ɗakin. Little ya kalli Abba yace
"Abba Lulu se kuka take yi.." Da mamaki Abba ya kalli Lulu, daidai lokacin da ta yi ƙarfin halin faɗin
"Abba sannu da zuwa.." ta faɗa tana jira ta ji ta inda Abban ze fara. Se dai ga mamakinta se ji ta yi yace
"Ashe har yanzu ba ki kwantar da hankalinki a kan auren nan ba Afaaf? So kike ki ɗorawa kanki damuwa koh? Ashe ban isa na yanke hukunci a kan ki ba? Har yanzu kin kasa haƙuri ki karɓi zaɓin da na miki? Shi ne kika zauna ki na ta kuka kenan har yanzu ba ki haƙura ba? Afaaf ashe ban isa dake ba.." Da mamaki ta ɗaga jajayen idanunta ta kalli Abba, se ta shiga girgiza kai, sannan ta soma faɗin
"Abba wallahi na haƙura.. na haƙura wallahi.. Abba ka isa da ni don Allah ka yi haƙuri ka min afuwa. Na haƙura wallahi Abba, ba zan sake kukan ba." Ta faɗa tana kai hannunta kan fuskarta ta shiga goge hawayen fuskar tata.
"Allah ya yi miki albarka. Allah ya ba ku zaman lafiya.. Allah ya miki albarka.." ya faɗa cikin matuƙar jin daɗin abin da ya fito daga bakin Lulun. Ita kam ba ta kuma san me za tace bayan wannan ba, ta riga ta san tsana ce a tsakaninta da Gwani, se dai daga ɗazu zuwa yanzu ta ji tsanar tasa ta ragu a cikin zuciyarta. Ta riga ta san har abada ba za ta so shi ba se dai tunda har ya iya ɓoye abin da ya faru ba tare da ya faɗawa Abba ba ita me iya cigaba da zama cikin gidan ne, ko babu komai ta bi umarnin Abbanta ta kuma cigaba da zama da Gwanin har lokacin da ze gano gaskiyar abin da ya faru. Ya gane ita ɗin ba yadda yake tunani ba ce. Da ƙyar ta iya amsawa da "Ameen" da dashashshiyar muryarta. Babu laifi sun ɗan taɓa hira, duk da hirar duk amfani da hakan Abba ya yi wajen sake yi mata faɗa sosai a kan zaman auren. Ita kuwa ba wani sosai take fahimta ba saboda har lokacin hankalinta a tashe yake, zuciyarta kuma ta kasa hutawa da tunanin yanda za ta fahimtar da Gwani gaskiyar al'amari.
"Toh bari mu tashi mu tafi.. Zan kuma tafi da Little kin san gobe za a koma makaranta.. Idan kuma aka yi hutun da za a yi nan da en kwanaki ze je wajen Didi.." Kallan Little ta yi tana jin sam babu daɗi, se dai dama ta san dole ze tafi. Don haka tace
"Toh Abba.. a gaida min da Ammina.. Sannan kuma ina so na yi waya da Didi don Allah.." ta faɗa da muryarta dake rawa.
"Babu damuwa.. ki faɗawa mijin naki idan ya amince ranar da za a kawo muku kayan ɗakin ku se a haɗo miki da wayar.. Ko kuma ma dai za mu yi magana da shi kawai, zan ba shi number da za a sameta se ku yi magana." Har ranta ta ji wani irin sanyi, ko babu komai za ta samu su tattauna da er uwarta a kan wannan abun.
... Tana takure a kan gadon dan ta kaasa sake gwada shiga ɗakin nan. Tana jin lokacin da ya shigo ɗakin, ta ɗauka ko ze sake mata maganar ne ta masa bayani amma ta ji shiru, dan shi tunda ya shigo ɗakin ya nemi waje ya zauna ba tare da ya kalli inda take ba.
"Kenan ya yadda hakan nake?" Ta tambayi kanta cikin karyewar zuciya. Hakan da ta raya a cikin zuciyarta shi ne ya sanya zuciyarta saurin karyewa, se ta shiga sauke ajiyar zuciya alamar kuka take shirin yi. Kukan da yanzu ba ya yi mata wuya.
Daga inda yake zaune yana jin yanda take jan sheshsheƙa a hankali, kamar ya share se kuma ya ga rashin dacewar hakan. Bayan kusan minti 1 ya miƙe a nutse ya soma takawa. Hannu ya saka ya yaye labulen idanunsa a kan gadon, jin motsinsa ne ya sanyata saurin tashi zaune a kan gadon ta kalle shi da fuskarta da ta zama kalar tausayi. Ita burinta ɗaya kawai ya fuskanceta, ya fahimci abin da take nufi, ya fahimci abin da ya gani ba shi ne gaskiya ba, wani ne yake son ɓata masa suna, wanda ba ta san waye shi ba. Kuma saboda tsabar ruɗewa ma ba ta taɓa kawowa kanta idan aka nemo Mami za a ji daga ainahin inda komai ya fito ba. Ƙarasawa ya yi cikin nutsuwar dai ya nemi gefen gadon ya zauna yana kallanta yace
"Kukan fa?" Ya faɗa a nutse kamar babu abin da ke faruwa. Kai ta girgiza lokacin da wasu sabbin hawayen suka zubo a kan kuncinta tace