← Book details Gidanmu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 190

Sashe 65

Gidanmu Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Kamar yadda take Ranar Lahadi a garin kano haka take Lahadin karshen Satin agarin na Dukku.
Yau gidan na Daada yana Cike da Mutane ne kama Daga ya"ya zuwa Jikoki,Tun jiya asabar Wasu suka sauka kamar su Inna Maimunatu da Inna Bintalo su da gayyar ya"yansu da marasa auran da masu auran duka suna Gidan Daada,Tun safe kuma Baffa Kabir ya sauka shima Tare da Mami Asma"u da ya"yansu duka Uku Wato Sajida da Umaima da Khamis wanda wannan karon Dolensa ya bar Aikinsa ya Taho Saboda Kiran Daada.
Baffa Mustpha ne karshen Zuwa Misalin karfe 11am na Safiya suka iso Bashir ne ke jan motar Umma da Inteesar da Hauwa suna Baya sai su Abiden Dake jikin Umma.
Inteeesar tun da suka Dauko Hanya bata iya cewa kala ba Bakinta kuwa ta gaji da Turasa ma ta Hakura ne bata so zuwa Dukku ba har ga Allah hakan baya Cikin Adanjanta Gobe ne suke Komawa Makaranta ta Fara Shirya kayanta Zata dawo ko Laraba ko alhamis Domin har mgana sunyi da Munari Zata dawo haka Kurum taji bata Kyauta ba in ta sabama Ya Imu alkwarinsa kuma ya gayamata Baya alkawari in yasan bazai cika ba kuma Shima bayaso ayimai in har baza"a cika ba..
Bata so ta karyamai Zuciya da Saba alkawarinta shiyasa ta Fadama Daddy zata koma Ranar Alhamis ko Laraba kuma ya amince mata har yayi mata alkawarin zai maidata kano da kansa Har Umma ta fara mata Shirin komawa Tunda har Mama ta kano sun yi mgana tace mata Intee na tafe Cikin Satin nan mai shiga kawai Rana Tsaka Ranar jumma"a Sai ga Kiran Baffa Kabir yana Fadama Daddy Daada Tana chan tana kuka Baba Asabe ta Kirashi ta gayamai shine yace abama Daada Wayar yana Tambayanta me ya faru nan take fadin Tana son ganinsu dukkansu kwansu da Kwarkwatansu Bata son ace mata wani baya nan ko yana makaranta ko yana Wajen aiki Dasu da duka ya"yansu take son gani kafin gobe a Dukku Domin Tana so ta Hada kansu ne kafin Ajali ya Risketa.
Ba Lallashin da bai mata ba ta Kafe kan mganarta Dole ya Kira Daddy ya Fadamai bayan ya Kira Su Inna Bintalo ya Shaida musu Halin da ake ciki Shine nan fa Kowa ya Tarkato Iyakansa ya Yada Zango adukku Gidan Tsohon Marigayi Alkalin Alkalai Hamisu Dukku.
Baffa Kabir Daman Khamis yazo Gida a Ranar zai yi kwana Biyu ya koma sai ga Kiran Daada Sajida kuma suna Hutu Tana gida Umaimace Take makaranta ba Halin adauje ma Tafiyar Duk yadda ko suke Girmama Karatun ya"yansu wannan karon basu da Tacewa Dole suka Tarkato har su sai sun Rasa aikinsu Gobe Monday Tun ba lalle bane su koma aranar sai takai su Gobe Tunda basu san Dalilin Taruwar da Daada ta Hada Lokaci Daya ba
Tun suna Hanya Mami ke ta Fada Tana Fadama Baffa Kabir Tana san bai wuce kan malami ba,tasa sukabar Komai nasu suka taho Mutumin Daya Gujeta da kansa kuma Miye abun Damun kai,Shidai yana Jinta bai ce komai ba sai Korafi take zata Rasa aikinta Gobe kadai Sajida ma Ranta bace saboda bata son Wahala ballatana Hayaniya gidan Daada kuwa komai da kanka Zakayi ba yan aikin da zaka saka suyi maka Khamis kuwa Da Umaima Ransu Fes Suna Farincikin zasu mahaifarsu suga Daada Daman Shima yana da Niyyar Zuwa sai ya bari sai wata watan in ya samu Huti bazai ma je Abuja ba Direct Dukku zai wuce yayi Hutunsa na Karshen Wata awajen Daada tunda Har ta gama Shan jinya bai Zo ba sai da ya Tura mata sako kuma Sunyi mganata ta waya..
Chapter 65 · 0% Book details