Sashe 86
Cutarwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***
Sai da ummi tayi sati uku cif, sannan dr. Ya koma ɗaukar ta, kamar ta ce masa dan Allah ya barta a nan, amma sai ta ji nauyin hakan ta kasa, kayanta ƙwaya biyu da ta je da su, sai da aka ɗinka mata kusan kala goma a can, kuma tuni suka haɗa kayan gyaran jiki masu haɗe da turarrruka, ummi ta fara amfani da shi.
Yaya maryam sai jaddada mata take yi, kar ta yi wasa da kayan gyaran da aka ba ta ta yi, da sabulan da aka haÉ—a mata.
Mariya ta kalli dr. Ta ce "Ka yi mini alƙawarin ba wurin Iya zaka mayar da ita ba?"
Yayi murmushi ya ce "Ai aronta na ce ki bani, ba zan kai miki ita wurin Iya ba"
"To ai zaka dawo da ita ko?"
"In sha Allah"
"To dan Allah ka kula mini da ita sosai da sosai, kar ka bari ta yi kuka"
"In sha Allah zan kula da ita sosai da sosai"
Ta kalli ummi ta ce "Kar ki yi musu kuka kin ji ummi, ban da ƙyuya da kuka, ba ruwanki da yara, kar ki je su din ga dukanki kin ji ko?"
Ummi ta riƙe hannunta ta ce "To mamana, me ki ke so na taho miki da shi idan zan dawo?"
Ta É—an yi jimm sannan ta ce "Bakomai, ni dai kawai ki dawo, ba dan ina jin kunyar kawu yahaya ba, ba zan bashi ke ba"
Ummi ta cigaba da kallon mariya tana jin daÉ—i.
Da ƙyar suka rabu suka nufo hanyar Kano.
Duk rashin surutun ummi, haka ta sake ta din ga yi wa kawu hira tana bawa kawun labarin mamanta.
Bayan azahar suka sauka a kano, noor kamar ta mayar da ummi cikin ta, dan murnar ta dawo.
Ummi ta shiga har falo, ta ce wa farida sun dawo, ta amsa mata a yatsune, sai dai fuskar inteesar kawai ta kalla ta san matsala ce ta kawota gida.
Ummi ta koma É—akinta, suka din ga hira ita da noor tana bawa noor labarin mamanta.
Noor ta ce "Kuma ki ka yadda ki ka dawo, wallaahi idan ni ce ba zan dawo ba, amma na san saboda yaya raihan ki ka dawo ko?"
Ummi ta ce "Ban sani ba"
Suka din ga dariya, noor ta ce "In gaya miki, Inteesar mijinta ya É—auki amaryarsa sun tafi umara, shi ne take kuka wai ba a tafi da ita ba"
"To waye ya tambaye ki?"
Noor tayi shiru tana ƙifta idanu.
Haka nan take murna, ta san yau za ta ga raihan, ta rasa dalilin da ya sanya take murna.
Haka nan ta samu kanta da yin shirin haÉ—uwa da shi.
Ta ɗauki kayan tsaraba da ta zo da su, har da su kayan turaren wuta ta kai wa farida, ta karɓe ba tare da godiya ba.
Bayan sallar magariba ummi ta saka rigar atamfa bubu, tana ta fama ta ɗaura ɗankwali, abu ya gagara saboda ba ta saba ba, ƙarshe noor ce ta ɗaura mata da ƙyar, shima gashin ya ƙi rufuwa, sai da ta saka hula sannan aka ɗaura ɗan kwalin.
Ta yafa mayafi, tana ta rufe-rufe tana tunanin anya za ta iya fita a haka? Kiran wayarsa ta gani, ta tashi ta kalli noor ta ce "Anya in fita a haka kuwa?"
"Wallahi kin yi kyau, kin rufe ko ina kuma"
Da ƙyar ummi ta iya fita, tana ta kare jikinta, ta ƙarasa in da yake.
"Oyoyo sweetheart, long time"
Tayi murmushi ta zauna, tana kawar da kanta gefe.
"Congratulations once again, ya ki ka baro mini maman?"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Tana lafiya ƙalau"
"Kin bata labarina kuwa?"
Ummi ta ce "Idan na yi mata babu lallai ta gane ma"
Ya ce "Ba ki yi niyya ba dai, zan je da kaina mu gaisa ai"
"Ka gama yajin?"
Yayi murmushi ya ce "Ke ma haka zaki ce?"
Ummi ta ce "To ba yajin ka yi ba, ko kunya ba ka ji ba?" Yayi dariya ya ce "Na samu mafita ai, kin yi kyau sosai da sosai wallahi, Allah ya nuna mana ranar nan lafiya babyna" ummi ta yi shiru tana sunkuyar da kanta.
Kausar ce ta nufo in da suke zaune, dan haka yayi shiru yana kallon ta.
Cikin mamaki take kallon raihan, yanzu wannan ne zai auri ummi? Wannan yaron, amma kuwa tayi asara, ko kuma shi yayi asarar kyakykyawan matashi kamar wannan ya auri ummi. Ta yi maganar a zuciyarta
Cikin gadara ta ce "Ke ki zo maama tana kiranki, wa ki ka barwa yin abincin daren da haryanzu baki ɗora ba," tayi maganar cike da son wulaƙanta ummi a gaban raihan.
Raihan ya ce "Tana magana da mijinta ne, idan kun matsu ku ci, ku dafa, tana buƙatar hutu, tun da yau ta dawo daga tafiya, kuma ina buƙatar yin magana da ita"
Zare ido ummi tayi ta ce "Na shiga uku, raihan"
"Shhh" ya É—ora yatsansa a kan lips É—in sa yana zare mata ido.
Ya sake kallon kausar ya ce "Ki koma ki ce ba za ta yi ba"
Ayshercool
08081012143.
             *CUTARWA*
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
34
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
Wani irin gumi ne ya dinga gangaro wa mami, duk da yadda sanyin AC ke ratsa ko ina a falon.
Raihan ƙararta ya je ya kai wa wannan masifaffiyar yar uban nasa kenan? tuno maganar Alhaji Tahir, da tuni ya bar falon da yayi ya sanya ta jin wata muguwar gudawa, saboda yadda cikinta ya murɗa mata.
Afujajan ta fita ta nufi sashinsa, har da tuntuɓe.
"Wallahi Baka isa ka gaya mini maganar da zata hana ni sukuni ka fice ka bar ni ba, kai yanzu saboda abun kunya goÉ—ai-goÉ—ai da kai sai ka auri yarinyar da É—an ka ya ce yana so?"
Alhaji Tahir ya ce "In dai haka shi ne mafita a gareni me zai hana? Ku mata ku kuka san wani abun kunya, mu maza abu in dai mu yayi mana ba ruwanmu da abun kunya, kuma ina sake tunatar da ke, bana magana biyu, wallahi da gaske nake, sai dai idan na aureta wanda ba zai iya zama da ni ba ya ƙara gaba, shawara ta rage ga mai shiga shiga rijiya" ya ƙarasa maganar tare da ɗaukar wayarsa ya fita.
Kamar wadda ta zare, haka ta sake kwasa har da gudu, ta tafi ta kira Anty rakiya a waya.
Rakiya na É—agawa mami ta fashe da kuka, "Anty rakiya na shiga uku na lalace"
"Wane irin kin shiga uku, meyafaru ba yanzu muka gama waya lafiya ba?"
"Ashe raihan bauchi ya tafi, ya je ya haÉ—o ni da wannan masifaffiyar matar yayar babansa, kin ga yadda ta ci mini mutunci kuwa? shi kuma Alhaji wai idan ban bari an yi auren ba, wai shi zai aureta ya kawota gidan nan a matsayin matarsa"
Anty Rakiya ta ce "Kai haba, dalla rabu da shi, barazana ce kar ki fasa wallahi, kar ki yadda a kawo miki bazawara a matsayin sirika"
"Anty Rakiya waye ya gaya miki Alhaji Tahir yana barazana ne? Magana É—aya yake yi ko ta yi maka daÉ—i, ko kuma akasin haka, har rantsuwa yayi mini, na shiga uku, kuma wai raihan ya ajiye aikin nan ina na kama?"
Anty Rakiya ta ce "Taɓ, lallai raihan ba shi da hankali, to wallahi idan ki ka zuba masa ido, haka zai aurota ya fi ƙarfinki, tun da har ya san yayi miki yaji, ki kira shi ki ce lallai ya dawo dan ubansa"
Mami cikin takaici ta ce "Lamarin fa ya wuce yadda ki ke tunani, kin san taurin kan raihan kuwa? To cewa tayi wai ba zai dawo ba, ya bar aikin kenan, ya kuma ce idan aka karɓo kuɗin auren nan, shi da aure har abada, ga babansa ya ce idan aka fasa zai aureta, na shiga uku ina na kama? Kin ga suna nema su haukata ni, raihan kafiya da taurin kai kamar ubansa, idan ya ƙi aure ya lalace yaya zan yi?"
Anty Rakiya ta ce "Ai kawai ki dage ki samu ya dawo tukuna, ki kira shi a waya"
"Wayoyin da duk ya kashe su, ina zan yi?"
"To ki koma ki samu babansa ki lallaɓa shi, ya dawo da shi kar a rasa wannan damar kuma ta kasuwancin nan "
Mami tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, zan kira ki mayi magana anjima" ta katse wayar ta ajiye tana wani irin haki, ita ba mai asma ba.
***
Dr. suna tafe a mota da shi da ummi, ya ce "Mamana zaki ga zamu yi doguwar tafiya, ba sayar da ke zan yi ba abun alkhairi ne"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Idan sayar da ni É—in ma ka yi ai na saidu kawu"
Yayi murmushi ya ce "Idan na sayar da uwata ina na kama? Yakamata ace kin yi azumin farinciki kan mu yi tafiyar nan"
"To Ubangiji ya tabattar mana da dukkanin alkhairin da yake cikinta"
Ya amsa mata da "amin"
Ummi ta gaji da zaman motar nan sosai da sosai, sai dai tun da taga symbols da sunan borno, jikinta ya fara sanyi, har ta rasa tunanin me ma za ta yi ne?.
Kawu kuma ya mayar da kai sosai a kan tuƙinsa, sai lokacin salla ya tsaya suka yi salla, ya saya mata abinci.
Sai da ummi tayi sati uku cif, sannan dr. Ya koma ɗaukar ta, kamar ta ce masa dan Allah ya barta a nan, amma sai ta ji nauyin hakan ta kasa, kayanta ƙwaya biyu da ta je da su, sai da aka ɗinka mata kusan kala goma a can, kuma tuni suka haɗa kayan gyaran jiki masu haɗe da turarrruka, ummi ta fara amfani da shi.
Yaya maryam sai jaddada mata take yi, kar ta yi wasa da kayan gyaran da aka ba ta ta yi, da sabulan da aka haÉ—a mata.
Mariya ta kalli dr. Ta ce "Ka yi mini alƙawarin ba wurin Iya zaka mayar da ita ba?"
Yayi murmushi ya ce "Ai aronta na ce ki bani, ba zan kai miki ita wurin Iya ba"
"To ai zaka dawo da ita ko?"
"In sha Allah"
"To dan Allah ka kula mini da ita sosai da sosai, kar ka bari ta yi kuka"
"In sha Allah zan kula da ita sosai da sosai"
Ta kalli ummi ta ce "Kar ki yi musu kuka kin ji ummi, ban da ƙyuya da kuka, ba ruwanki da yara, kar ki je su din ga dukanki kin ji ko?"
Ummi ta riƙe hannunta ta ce "To mamana, me ki ke so na taho miki da shi idan zan dawo?"
Ta É—an yi jimm sannan ta ce "Bakomai, ni dai kawai ki dawo, ba dan ina jin kunyar kawu yahaya ba, ba zan bashi ke ba"
Ummi ta cigaba da kallon mariya tana jin daÉ—i.
Da ƙyar suka rabu suka nufo hanyar Kano.
Duk rashin surutun ummi, haka ta sake ta din ga yi wa kawu hira tana bawa kawun labarin mamanta.
Bayan azahar suka sauka a kano, noor kamar ta mayar da ummi cikin ta, dan murnar ta dawo.
Ummi ta shiga har falo, ta ce wa farida sun dawo, ta amsa mata a yatsune, sai dai fuskar inteesar kawai ta kalla ta san matsala ce ta kawota gida.
Ummi ta koma É—akinta, suka din ga hira ita da noor tana bawa noor labarin mamanta.
Noor ta ce "Kuma ki ka yadda ki ka dawo, wallaahi idan ni ce ba zan dawo ba, amma na san saboda yaya raihan ki ka dawo ko?"
Ummi ta ce "Ban sani ba"
Suka din ga dariya, noor ta ce "In gaya miki, Inteesar mijinta ya É—auki amaryarsa sun tafi umara, shi ne take kuka wai ba a tafi da ita ba"
"To waye ya tambaye ki?"
Noor tayi shiru tana ƙifta idanu.
Haka nan take murna, ta san yau za ta ga raihan, ta rasa dalilin da ya sanya take murna.
Haka nan ta samu kanta da yin shirin haÉ—uwa da shi.
Ta ɗauki kayan tsaraba da ta zo da su, har da su kayan turaren wuta ta kai wa farida, ta karɓe ba tare da godiya ba.
Bayan sallar magariba ummi ta saka rigar atamfa bubu, tana ta fama ta ɗaura ɗankwali, abu ya gagara saboda ba ta saba ba, ƙarshe noor ce ta ɗaura mata da ƙyar, shima gashin ya ƙi rufuwa, sai da ta saka hula sannan aka ɗaura ɗan kwalin.
Ta yafa mayafi, tana ta rufe-rufe tana tunanin anya za ta iya fita a haka? Kiran wayarsa ta gani, ta tashi ta kalli noor ta ce "Anya in fita a haka kuwa?"
"Wallahi kin yi kyau, kin rufe ko ina kuma"
Da ƙyar ummi ta iya fita, tana ta kare jikinta, ta ƙarasa in da yake.
"Oyoyo sweetheart, long time"
Tayi murmushi ta zauna, tana kawar da kanta gefe.
"Congratulations once again, ya ki ka baro mini maman?"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Tana lafiya ƙalau"
"Kin bata labarina kuwa?"
Ummi ta ce "Idan na yi mata babu lallai ta gane ma"
Ya ce "Ba ki yi niyya ba dai, zan je da kaina mu gaisa ai"
"Ka gama yajin?"
Yayi murmushi ya ce "Ke ma haka zaki ce?"
Ummi ta ce "To ba yajin ka yi ba, ko kunya ba ka ji ba?" Yayi dariya ya ce "Na samu mafita ai, kin yi kyau sosai da sosai wallahi, Allah ya nuna mana ranar nan lafiya babyna" ummi ta yi shiru tana sunkuyar da kanta.
Kausar ce ta nufo in da suke zaune, dan haka yayi shiru yana kallon ta.
Cikin mamaki take kallon raihan, yanzu wannan ne zai auri ummi? Wannan yaron, amma kuwa tayi asara, ko kuma shi yayi asarar kyakykyawan matashi kamar wannan ya auri ummi. Ta yi maganar a zuciyarta
Cikin gadara ta ce "Ke ki zo maama tana kiranki, wa ki ka barwa yin abincin daren da haryanzu baki ɗora ba," tayi maganar cike da son wulaƙanta ummi a gaban raihan.
Raihan ya ce "Tana magana da mijinta ne, idan kun matsu ku ci, ku dafa, tana buƙatar hutu, tun da yau ta dawo daga tafiya, kuma ina buƙatar yin magana da ita"
Zare ido ummi tayi ta ce "Na shiga uku, raihan"
"Shhh" ya É—ora yatsansa a kan lips É—in sa yana zare mata ido.
Ya sake kallon kausar ya ce "Ki koma ki ce ba za ta yi ba"
Ayshercool
08081012143.
             *CUTARWA*
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
34
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
FOLLOW AND SHARE
AYSHERCOOL
08081012143
MASU BUƘATA DAGA FARKO WANDA BA SA WATPAD, KU YI FOLLOWING CHANNEL ƊINA, ZAKU SAMU DAGA FARKO IN SHA ALLAH.
Follow the COOL HAUSA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
Follow this link, to join my what's app channel, domin samun sabbi da tsofaffin litattafaina, tare da tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi rayuwa na yau da gobe.
Wani irin gumi ne ya dinga gangaro wa mami, duk da yadda sanyin AC ke ratsa ko ina a falon.
Raihan ƙararta ya je ya kai wa wannan masifaffiyar yar uban nasa kenan? tuno maganar Alhaji Tahir, da tuni ya bar falon da yayi ya sanya ta jin wata muguwar gudawa, saboda yadda cikinta ya murɗa mata.
Afujajan ta fita ta nufi sashinsa, har da tuntuɓe.
"Wallahi Baka isa ka gaya mini maganar da zata hana ni sukuni ka fice ka bar ni ba, kai yanzu saboda abun kunya goÉ—ai-goÉ—ai da kai sai ka auri yarinyar da É—an ka ya ce yana so?"
Alhaji Tahir ya ce "In dai haka shi ne mafita a gareni me zai hana? Ku mata ku kuka san wani abun kunya, mu maza abu in dai mu yayi mana ba ruwanmu da abun kunya, kuma ina sake tunatar da ke, bana magana biyu, wallahi da gaske nake, sai dai idan na aureta wanda ba zai iya zama da ni ba ya ƙara gaba, shawara ta rage ga mai shiga shiga rijiya" ya ƙarasa maganar tare da ɗaukar wayarsa ya fita.
Kamar wadda ta zare, haka ta sake kwasa har da gudu, ta tafi ta kira Anty rakiya a waya.
Rakiya na É—agawa mami ta fashe da kuka, "Anty rakiya na shiga uku na lalace"
"Wane irin kin shiga uku, meyafaru ba yanzu muka gama waya lafiya ba?"
"Ashe raihan bauchi ya tafi, ya je ya haÉ—o ni da wannan masifaffiyar matar yayar babansa, kin ga yadda ta ci mini mutunci kuwa? shi kuma Alhaji wai idan ban bari an yi auren ba, wai shi zai aureta ya kawota gidan nan a matsayin matarsa"
Anty Rakiya ta ce "Kai haba, dalla rabu da shi, barazana ce kar ki fasa wallahi, kar ki yadda a kawo miki bazawara a matsayin sirika"
"Anty Rakiya waye ya gaya miki Alhaji Tahir yana barazana ne? Magana É—aya yake yi ko ta yi maka daÉ—i, ko kuma akasin haka, har rantsuwa yayi mini, na shiga uku, kuma wai raihan ya ajiye aikin nan ina na kama?"
Anty Rakiya ta ce "Taɓ, lallai raihan ba shi da hankali, to wallahi idan ki ka zuba masa ido, haka zai aurota ya fi ƙarfinki, tun da har ya san yayi miki yaji, ki kira shi ki ce lallai ya dawo dan ubansa"
Mami cikin takaici ta ce "Lamarin fa ya wuce yadda ki ke tunani, kin san taurin kan raihan kuwa? To cewa tayi wai ba zai dawo ba, ya bar aikin kenan, ya kuma ce idan aka karɓo kuɗin auren nan, shi da aure har abada, ga babansa ya ce idan aka fasa zai aureta, na shiga uku ina na kama? Kin ga suna nema su haukata ni, raihan kafiya da taurin kai kamar ubansa, idan ya ƙi aure ya lalace yaya zan yi?"
Anty Rakiya ta ce "Ai kawai ki dage ki samu ya dawo tukuna, ki kira shi a waya"
"Wayoyin da duk ya kashe su, ina zan yi?"
"To ki koma ki samu babansa ki lallaɓa shi, ya dawo da shi kar a rasa wannan damar kuma ta kasuwancin nan "
Mami tayi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, zan kira ki mayi magana anjima" ta katse wayar ta ajiye tana wani irin haki, ita ba mai asma ba.
***
Dr. suna tafe a mota da shi da ummi, ya ce "Mamana zaki ga zamu yi doguwar tafiya, ba sayar da ke zan yi ba abun alkhairi ne"
Ummi ta yi murmushi ta ce "Idan sayar da ni É—in ma ka yi ai na saidu kawu"
Yayi murmushi ya ce "Idan na sayar da uwata ina na kama? Yakamata ace kin yi azumin farinciki kan mu yi tafiyar nan"
"To Ubangiji ya tabattar mana da dukkanin alkhairin da yake cikinta"
Ya amsa mata da "amin"
Ummi ta gaji da zaman motar nan sosai da sosai, sai dai tun da taga symbols da sunan borno, jikinta ya fara sanyi, har ta rasa tunanin me ma za ta yi ne?.
Kawu kuma ya mayar da kai sosai a kan tuƙinsa, sai lokacin salla ya tsaya suka yi salla, ya saya mata abinci.