Sashe 12
Cutarwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana gani aka zaɓi wata daban, bayan malamar ta fita, suka ɗora da yi mata dariya da tsokanar ta, har da masu ja mata hijjabi, suna ƙazama ba ta wanka ba ta wanki, waƙar da aka saba yi mata a assembly idan an zo duban tsabta, har misali ake yi da ita, na ƙazamai.
Ana tashi ta fita daga aji, ta nufi gida har da gudunta, dan kar ma ƴan ajinsu su taso, su tireta a hanya, ta ƙarasa tana ta numfarfashi.
Sai da ta É—an huta sannan ta shiga sashin su da sallama, muryar iya ta fara jiyo wa tana hayaniya, da muryar baba saminu, ba ta san dai faÉ—an me suke yi ba, ta kutsa kai ta shiga.
Wan mahaifiyarta ta gani, a zaune suna ta jayayya da su iya.
Hayaniyar da suke yi, ba ita ce ta dame ta ba, murnar ta Allah ya sa da mama suka dawo.
Bai lura da ummi ba, sai da ta riƙe hannunsa, ya waiwayo ya kalleta ta ce "Ina maman take?" Yayi ƙuri da ido yana kallon ummi, sai ka ce ba ƴar mutane ba.
Yadda mariya ke ƙalƙaleta, take kula da ita, amma ya ganta kamar an janyota daga ramin ƙasa.
Ya ce "Baki gaishe ni ba" ta tsuguna ƙasa ta ce "Ina kwana"
"Lafiya ƙalau, ya makarantar?"
Ta ce "Lafiya lau, to ina maman take?"
"Mama tana lafiya, ta ce; a gaishe ki"
Ummi ta sake kallonsa ta ce "To zaka kai ni wurinta?"
"Ke wuce ki je ki cire uniform, ki yi salla" Iya tayi mata tsawa. Yayi shiru ransa a matuƙar ɓace, bai taɓa tunanin ganin ummi a cikin wannan mummunan yanayin ba.
Ta fito kanta babu ɗan kwali, gashin nan a cukurkuɗe, sai soshe-soshe take yi, saboda yadda ya addaba mata da ƙaiƙayi.
Ya dubi iya ya ce "Shikenan, tun da kun ce cikin ba naku bane ba, baku san da shi ba, ni ba dan wani abun hannunku ya sanya muka zo muka sanar da akwai cikin ba, saboda a cika umarnin Ubangiji, amma tun da abun haka ne, Allah ya kyauta, mu mun ji mun gani, mun karɓa. Amma dan Allah ku bani ƴar ta in kai mata, mariya ta kasa zaune ta kasa tsaye, hankalinta yaƙi kwanciya, ku bata ƴar ta dan Allah"
"Ba rashin ummi ne ya hanata nutsuwa ba, mugun abun ta ne yake koma mata kanta, hakkina da na ɗa na ba zai taɓa barinta ba, ya din ga bibiyar ta kenan"
Ganin idan ya cigaba da zama, wannan jayayyar zata kai su ga maganar banza, ya sanya ya tashi tsam, ya ce "Shikenan babu laifi, Allah ya kyauta"
Jin ya ce zai tafi, ya sanya ummi fitowa da gudu daga É—aki, ta ce "Ba zaka tafi da ni, ka kai ni wurin maman ba?"
Ya durƙusa ya shafa kanta ya ce "Ki yi haƙuri, in sha Allah nan gaba kaɗan, zaki koma wurin mamanki, Allah ya yi miki albarka" ya ciro kuɗi dubu biyar, ya bawa iya ya ce "Dan Allah a canza mata uniform, a saya mata wasu ƴan kayan buƙata"
Ba kunya iya ta amshe, tana harare-harare.
Ummi ta tsaya tabi bayansa da kallo har ya fice.
Dukan da aka yi mata a kanta ne, ya sanya ta dawowa hayyacinta, ta firgita ta kalli Iya.
"Duk wanda ya sake zuwa gidan nan, ki ka ce ya kai ki wurin uwarki, sai na saka idris ya zane miki jikinki, wato salon ace ba a kula da ke, saboda ƙwarewa a munafunci kin tsotsa a nono ko?" Tayi shiru ta sunkuyar da kanta ƙasa.
"Munafuka, ga muni ga kinibibi, tashi ki wanke kwanukan nan na safe" sumi-sumi ta nufi wurin tara kwanukan wanke wanke, ta haÉ—a ta fara wankewa.
***
Bayan sallar magariba, yaya garba ya je ya samu mahaifinsu ya sanar da shi cewa iya ta ce ba su san da ciki ba, dan haka a nemi ubansa.
Malam yayi shiru, lamarin ya girmame shi ya ce "Haka suka ce?"
"Wallahi, matar nan ba ta da mutunci ba ta da imani ko kaɗan, ba ka ga Yarinyar nan a halin da na baro bata ba, kamar ƴar jari bola saboda azabar datti da ƙazanta"
"Ƙyalesu, yarinya kullum muna yi mata addu'a, in sha Allah babu wanda zai sake bi ta kansu, ita kuma Allah ya raba ta da ciki lafiya"
Ya amsa masa da "Amin"
***
Na'ima kuwa ummi na ranta, amma babarta ta ce mata ba ita ba ummi, dan kakarta ba mutunci ne da ita ba, kar ta yi mata wani sharrin.
Sai dai ta kan ƙulle abinci wasu lokutan, ta tafi da shi makaranta ta bawa ummi.
Yanzu babu mai yi wa ummi wanki balle guga, dan haka dauÉ—a kamar ka kankarota a jikinta.
Ummi na iya ƙoƙarin ta wurin kaucewa haɗuwa da idiris, ga bala'in tsoronsa da take ji, saboda dukan da yake yi mata idan tayi laifi babu tausayi babu imani.
Allah ya taimake ta, wasu lokutan magaji na taka masa burki a kan wasu abubuwan.
Tsabar rashin gyara, ya sanya kwarkwata cika wa ummi gashi, kayan ta duk suka cukurkuɗe suka yi mata kaɗan, tana zaune har sakkowa kwarkwata suke yi daga kanta, suna bin ta, sai dai ta ɓuya tayi ta kashewa, ba ta son a gani.
Ga wasu irin manyan ƙuraje da suka din ga fitowa a cikin gashin kan nata, suna ɗurar ruwa, suka ƙara bawa kwarkwatar nan damar hayayyafa babu ji babu gani.
Banda zarnin fitsari da warin datti, babu abun da take yi, dan kuwa da kanta take yi wa kanta wankin kayanta, wando sai ya fi kwana uku a jikinta, ba ruwan iya balle ta ce cire ki wanke.
Sa'adatu ce babar auwwalu, ta fara lura da wannan ƙurajen na kan ummi, ta kamata ta buɗe kan, ta ga ƙazantar da take cikin gashin.
Ta nuna wa iya, Iya ta yamutse fuska ta ce "Taɓ gaskiya ba zan iya taɓa wannan kan ba, to gashi ne ba kaɗan ba, gaba ɗaya ba irin namu ba, kalar na mutanen ƙetare, shiyasa nake cewa anya ma kuwa tamun ce, duk zuriyar mu, babu irin wannan gashin, yanzu meye abun yi kar kan ya ruɓe ace ni ce ina kallonta, na bari ya ruɓe ji yadda wani mugun ruwa yake tsatstsafowa da ƙwayayen kwarkwata a ciki".
"Aikuwa sai dai a aske kan nan, dan ban ga yadda za ayi maganin abun nan ba"
Cikin ƙyanƙyami, sa'adatu ta sauke wa ummi gashin nan tsaf, ta koma sai ka ce namiji, ga hudar kunnenta ma, tana ruwa saboda tsufan ɗan kunne a kunnenta, ba a taɓa cirewa ba.
Iya ta saka aka haɗa kanwa da gishiri, da omo aka wanke kan nan, ummi ta din ga wani irin masifaffen kuka, saboda azabar raɗaɗi, da bal'in zafi haka nan da ruwan sanyi aka tuɓe ta, aka wanketa a tsakar gidan, iya har tana cewa wannan baƙar fatar ba da dutsen goge faso za a wanketa ba kuwa?. Wata irin annakiyar dauɗa ta din ga zuba daga jikin yarinyar. Yara suka cika sashin danƙam suna kallon ummi, da tana ta ƙoƙarin rufe jikinta, amma azabar wahala da zafi ya sanya ta manta da tsiraicinta.
Ummi na ji na gani, aka ɗaure gashinta a leda kaya guda da shi aka zubar, iya ta ce a sakawa kan ummi fiya-fiya, idan ba haka ba, sauran ƙwan zai ƙyanƙyashe kansa.
Ba tare da tunanin wane hali zata shiga ba, suka shafe ƙwallon kan da suka saukewa sumarta da fiya-fiya, hakan ya sa ta din ga tari da atishawa, gaba ɗaya kanta ya juye, ta din ga jiri, kan dare zazzaɓi ya rufe ta da ciwon kai.
Ba wanda ya kula ya saya mata magani, haka ta kwana tana rawar sanyi, da ta yinƙura ta tashi, sai ta tafi luuu zata faɗi.
Da safe gwaggo ta bata, koko da ƙosai, sai dai ta kasa ci, ta cigaba da kwanciya tana burgima a ƙasa, kanta yana ciwo, ga tari da take ta faman yi.
Cikin barccin wahala, ummi ta ji wani ƙamshin turare mai daɗi, ta ji magana sama-sama kamar muryar babanta.
Da sauri ta buɗe ido, ta yi ƙuri da ido tana kallonsa, ga iya a gefe suna magana da shi.
Yayi murmushi ya ce "Uwata ta kaina, kin tashi? Ƙaraso mu gaisa" sai yanzu ta lura ba baba bane ba, mutumin nan ne mai kama da shi.
Tasowa ta yi da sauri, sai dai ta faÉ—i, saboda jirin da take ji.
Da sauri ya tashi, ya ce "Iya ba ta da lafiya ne?" Iya ta taɓe baki, mussaman jin ya kirata da uwassa ta kansa ta ce "Eh zazzaɓi take".
"Subhanallah, kuma ba a kaita asibiti ba?"
Ya zaunar da ummi, ya sinsuna kanta ya ce "Ya na ji kamar kina warin fiya-fiya? Ya cire hular kanta, sai ga kai sol ba gashi, ga dagwalon gyambo a kan, ciwon duk yayi baƙi saboda fiya-fiya.
A razane ya ce "Meye wannan? Iya meya sameta a kanta?"
"Kwarkwata ce, da wasu ƙuraje, shi ne aka aske kan aka shafa mata fiya-fiya"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, iya wannan ai ganganci ne, ina laifin a kaita asibiti, wannan ƙaramar yarinyar a saka mata fiya-fiya a ka, ai shi ya sanya mata zazzaɓi".
"To ban da kai yahaya, ana ta abun da za a ci, waye yake ta wani asibiti, wa zai bayar da kuÉ—in kai ta wani asibiti?"
Miƙewa yayi ya ce "Wannan abun kunya da yawa yake"
Cak ya saɓa ummi a kafaɗarsa, yayi waje da ita, iya ta biyo shi tana tambayar ina zai kai ta?.
"Asibiti zan kai ta, idan ta mutu ba makawa ku ne ku ka kasheta" yayi waje da ita.
A mota ya kwantar da ita, ya ja suka tafi.
Sosai likitoci suka din ga faɗa, dan ma asibitin kuɗi ne, aka sake wanke kan ummi, da magunguna, aka saka mata ruwa saboda zazzaɓin da ya rufeta, take ta rawar sanyi.
Ya fita ya sayo kayan marmari, da ta farfaɗo zazzaɓin ya sauka, ya din ga bata da kansa.
"Kana kama da baba" ta faɗa a lokacin da zaƙin kankana ya ratsa kwanyarta, wanda rabon da ta sha har ta manta.
Yayi mata murmushi ya ce "Ai nima baba ne"
Ana tashi ta fita daga aji, ta nufi gida har da gudunta, dan kar ma ƴan ajinsu su taso, su tireta a hanya, ta ƙarasa tana ta numfarfashi.
Sai da ta É—an huta sannan ta shiga sashin su da sallama, muryar iya ta fara jiyo wa tana hayaniya, da muryar baba saminu, ba ta san dai faÉ—an me suke yi ba, ta kutsa kai ta shiga.
Wan mahaifiyarta ta gani, a zaune suna ta jayayya da su iya.
Hayaniyar da suke yi, ba ita ce ta dame ta ba, murnar ta Allah ya sa da mama suka dawo.
Bai lura da ummi ba, sai da ta riƙe hannunsa, ya waiwayo ya kalleta ta ce "Ina maman take?" Yayi ƙuri da ido yana kallon ummi, sai ka ce ba ƴar mutane ba.
Yadda mariya ke ƙalƙaleta, take kula da ita, amma ya ganta kamar an janyota daga ramin ƙasa.
Ya ce "Baki gaishe ni ba" ta tsuguna ƙasa ta ce "Ina kwana"
"Lafiya ƙalau, ya makarantar?"
Ta ce "Lafiya lau, to ina maman take?"
"Mama tana lafiya, ta ce; a gaishe ki"
Ummi ta sake kallonsa ta ce "To zaka kai ni wurinta?"
"Ke wuce ki je ki cire uniform, ki yi salla" Iya tayi mata tsawa. Yayi shiru ransa a matuƙar ɓace, bai taɓa tunanin ganin ummi a cikin wannan mummunan yanayin ba.
Ta fito kanta babu ɗan kwali, gashin nan a cukurkuɗe, sai soshe-soshe take yi, saboda yadda ya addaba mata da ƙaiƙayi.
Ya dubi iya ya ce "Shikenan, tun da kun ce cikin ba naku bane ba, baku san da shi ba, ni ba dan wani abun hannunku ya sanya muka zo muka sanar da akwai cikin ba, saboda a cika umarnin Ubangiji, amma tun da abun haka ne, Allah ya kyauta, mu mun ji mun gani, mun karɓa. Amma dan Allah ku bani ƴar ta in kai mata, mariya ta kasa zaune ta kasa tsaye, hankalinta yaƙi kwanciya, ku bata ƴar ta dan Allah"
"Ba rashin ummi ne ya hanata nutsuwa ba, mugun abun ta ne yake koma mata kanta, hakkina da na ɗa na ba zai taɓa barinta ba, ya din ga bibiyar ta kenan"
Ganin idan ya cigaba da zama, wannan jayayyar zata kai su ga maganar banza, ya sanya ya tashi tsam, ya ce "Shikenan babu laifi, Allah ya kyauta"
Jin ya ce zai tafi, ya sanya ummi fitowa da gudu daga É—aki, ta ce "Ba zaka tafi da ni, ka kai ni wurin maman ba?"
Ya durƙusa ya shafa kanta ya ce "Ki yi haƙuri, in sha Allah nan gaba kaɗan, zaki koma wurin mamanki, Allah ya yi miki albarka" ya ciro kuɗi dubu biyar, ya bawa iya ya ce "Dan Allah a canza mata uniform, a saya mata wasu ƴan kayan buƙata"
Ba kunya iya ta amshe, tana harare-harare.
Ummi ta tsaya tabi bayansa da kallo har ya fice.
Dukan da aka yi mata a kanta ne, ya sanya ta dawowa hayyacinta, ta firgita ta kalli Iya.
"Duk wanda ya sake zuwa gidan nan, ki ka ce ya kai ki wurin uwarki, sai na saka idris ya zane miki jikinki, wato salon ace ba a kula da ke, saboda ƙwarewa a munafunci kin tsotsa a nono ko?" Tayi shiru ta sunkuyar da kanta ƙasa.
"Munafuka, ga muni ga kinibibi, tashi ki wanke kwanukan nan na safe" sumi-sumi ta nufi wurin tara kwanukan wanke wanke, ta haÉ—a ta fara wankewa.
***
Bayan sallar magariba, yaya garba ya je ya samu mahaifinsu ya sanar da shi cewa iya ta ce ba su san da ciki ba, dan haka a nemi ubansa.
Malam yayi shiru, lamarin ya girmame shi ya ce "Haka suka ce?"
"Wallahi, matar nan ba ta da mutunci ba ta da imani ko kaɗan, ba ka ga Yarinyar nan a halin da na baro bata ba, kamar ƴar jari bola saboda azabar datti da ƙazanta"
"Ƙyalesu, yarinya kullum muna yi mata addu'a, in sha Allah babu wanda zai sake bi ta kansu, ita kuma Allah ya raba ta da ciki lafiya"
Ya amsa masa da "Amin"
***
Na'ima kuwa ummi na ranta, amma babarta ta ce mata ba ita ba ummi, dan kakarta ba mutunci ne da ita ba, kar ta yi mata wani sharrin.
Sai dai ta kan ƙulle abinci wasu lokutan, ta tafi da shi makaranta ta bawa ummi.
Yanzu babu mai yi wa ummi wanki balle guga, dan haka dauÉ—a kamar ka kankarota a jikinta.
Ummi na iya ƙoƙarin ta wurin kaucewa haɗuwa da idiris, ga bala'in tsoronsa da take ji, saboda dukan da yake yi mata idan tayi laifi babu tausayi babu imani.
Allah ya taimake ta, wasu lokutan magaji na taka masa burki a kan wasu abubuwan.
Tsabar rashin gyara, ya sanya kwarkwata cika wa ummi gashi, kayan ta duk suka cukurkuɗe suka yi mata kaɗan, tana zaune har sakkowa kwarkwata suke yi daga kanta, suna bin ta, sai dai ta ɓuya tayi ta kashewa, ba ta son a gani.
Ga wasu irin manyan ƙuraje da suka din ga fitowa a cikin gashin kan nata, suna ɗurar ruwa, suka ƙara bawa kwarkwatar nan damar hayayyafa babu ji babu gani.
Banda zarnin fitsari da warin datti, babu abun da take yi, dan kuwa da kanta take yi wa kanta wankin kayanta, wando sai ya fi kwana uku a jikinta, ba ruwan iya balle ta ce cire ki wanke.
Sa'adatu ce babar auwwalu, ta fara lura da wannan ƙurajen na kan ummi, ta kamata ta buɗe kan, ta ga ƙazantar da take cikin gashin.
Ta nuna wa iya, Iya ta yamutse fuska ta ce "Taɓ gaskiya ba zan iya taɓa wannan kan ba, to gashi ne ba kaɗan ba, gaba ɗaya ba irin namu ba, kalar na mutanen ƙetare, shiyasa nake cewa anya ma kuwa tamun ce, duk zuriyar mu, babu irin wannan gashin, yanzu meye abun yi kar kan ya ruɓe ace ni ce ina kallonta, na bari ya ruɓe ji yadda wani mugun ruwa yake tsatstsafowa da ƙwayayen kwarkwata a ciki".
"Aikuwa sai dai a aske kan nan, dan ban ga yadda za ayi maganin abun nan ba"
Cikin ƙyanƙyami, sa'adatu ta sauke wa ummi gashin nan tsaf, ta koma sai ka ce namiji, ga hudar kunnenta ma, tana ruwa saboda tsufan ɗan kunne a kunnenta, ba a taɓa cirewa ba.
Iya ta saka aka haɗa kanwa da gishiri, da omo aka wanke kan nan, ummi ta din ga wani irin masifaffen kuka, saboda azabar raɗaɗi, da bal'in zafi haka nan da ruwan sanyi aka tuɓe ta, aka wanketa a tsakar gidan, iya har tana cewa wannan baƙar fatar ba da dutsen goge faso za a wanketa ba kuwa?. Wata irin annakiyar dauɗa ta din ga zuba daga jikin yarinyar. Yara suka cika sashin danƙam suna kallon ummi, da tana ta ƙoƙarin rufe jikinta, amma azabar wahala da zafi ya sanya ta manta da tsiraicinta.
Ummi na ji na gani, aka ɗaure gashinta a leda kaya guda da shi aka zubar, iya ta ce a sakawa kan ummi fiya-fiya, idan ba haka ba, sauran ƙwan zai ƙyanƙyashe kansa.
Ba tare da tunanin wane hali zata shiga ba, suka shafe ƙwallon kan da suka saukewa sumarta da fiya-fiya, hakan ya sa ta din ga tari da atishawa, gaba ɗaya kanta ya juye, ta din ga jiri, kan dare zazzaɓi ya rufe ta da ciwon kai.
Ba wanda ya kula ya saya mata magani, haka ta kwana tana rawar sanyi, da ta yinƙura ta tashi, sai ta tafi luuu zata faɗi.
Da safe gwaggo ta bata, koko da ƙosai, sai dai ta kasa ci, ta cigaba da kwanciya tana burgima a ƙasa, kanta yana ciwo, ga tari da take ta faman yi.
Cikin barccin wahala, ummi ta ji wani ƙamshin turare mai daɗi, ta ji magana sama-sama kamar muryar babanta.
Da sauri ta buɗe ido, ta yi ƙuri da ido tana kallonsa, ga iya a gefe suna magana da shi.
Yayi murmushi ya ce "Uwata ta kaina, kin tashi? Ƙaraso mu gaisa" sai yanzu ta lura ba baba bane ba, mutumin nan ne mai kama da shi.
Tasowa ta yi da sauri, sai dai ta faÉ—i, saboda jirin da take ji.
Da sauri ya tashi, ya ce "Iya ba ta da lafiya ne?" Iya ta taɓe baki, mussaman jin ya kirata da uwassa ta kansa ta ce "Eh zazzaɓi take".
"Subhanallah, kuma ba a kaita asibiti ba?"
Ya zaunar da ummi, ya sinsuna kanta ya ce "Ya na ji kamar kina warin fiya-fiya? Ya cire hular kanta, sai ga kai sol ba gashi, ga dagwalon gyambo a kan, ciwon duk yayi baƙi saboda fiya-fiya.
A razane ya ce "Meye wannan? Iya meya sameta a kanta?"
"Kwarkwata ce, da wasu ƙuraje, shi ne aka aske kan aka shafa mata fiya-fiya"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, iya wannan ai ganganci ne, ina laifin a kaita asibiti, wannan ƙaramar yarinyar a saka mata fiya-fiya a ka, ai shi ya sanya mata zazzaɓi".
"To ban da kai yahaya, ana ta abun da za a ci, waye yake ta wani asibiti, wa zai bayar da kuÉ—in kai ta wani asibiti?"
Miƙewa yayi ya ce "Wannan abun kunya da yawa yake"
Cak ya saɓa ummi a kafaɗarsa, yayi waje da ita, iya ta biyo shi tana tambayar ina zai kai ta?.
"Asibiti zan kai ta, idan ta mutu ba makawa ku ne ku ka kasheta" yayi waje da ita.
A mota ya kwantar da ita, ya ja suka tafi.
Sosai likitoci suka din ga faɗa, dan ma asibitin kuɗi ne, aka sake wanke kan ummi, da magunguna, aka saka mata ruwa saboda zazzaɓin da ya rufeta, take ta rawar sanyi.
Ya fita ya sayo kayan marmari, da ta farfaɗo zazzaɓin ya sauka, ya din ga bata da kansa.
"Kana kama da baba" ta faɗa a lokacin da zaƙin kankana ya ratsa kwanyarta, wanda rabon da ta sha har ta manta.
Yayi mata murmushi ya ce "Ai nima baba ne"