Sashe 74
Cutarwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai ƙasan zuciyarsa yana tunanin, ummi za ta amince ko kuwa za ta cigaba da gardama ne? Dan ya ga kamar ta raina shi ne a matsayin mijin aure, yayi mata ƙanƙanta.
Yana zuwa ya tafi sashin Alhaji, dan kwanakin nan kusan kullum Alhajin yana gida, ya daki sa'a shikaÉ—ai ya tarar a sashin nasa.
Alhaji Tahir ya gyara zaman tabaran sa, ya ce "Ya aka yi ne? Yanayin farinciki haÉ—e da damuwa a fuskar babban mutum"
Raihan ya je ya zauna a kusa da shi, ya ce "Kowanne akwai Alhaji"
"Bani labari"
Ya ciro wayarsa, ya nemo hoton ummi da yayi mata, lokacin da suka sayo dogwayen riguna, ya ce "Alhaji ka ga wannan"
Alhaji ya karɓi wayar, ya ƙare wa hoton kallo ya ce "Na gani, meyafaru?"
"Alhaji tana da kyau?"
Ya ce "Masha Allah, very beautiful kuwa, da gani kuma tana da kunya"
"Ita nake son aura Alhaji, zaka nema mini aurenta?"
Alhaji Tahir ya kalli raihan yayi murmushi ya ce "Babban mutum wannan ai matar manyan ce, anya ba ka yi tsaurin ido ba kuwa?"
"A'a Alhaji, ai nima babban mutum ne, dan Allah tayi? Wallahi mutuniyar kirki ce"
Alhaji ya yi shiru ya ce "Ai ni kallon sani nake yi mata ma"
Raihan ya ce "Eh, ƙawar maryam ce, amma ita ba ta girme ni ba, shekrunmu ɗaya da ita, kuma mutuniyar kirki ce ka tambayi Hajiya ma ka ji"
Alhaji Tahir ya dafa kafaÉ—ar raihan ya ce "Easy my dear, in dai kana son ta tayi mini, za a nemi aurenta in dai za a bamu"
Raihan ya washe baki ya ce "Babanta ya ce ranar Sunday wai ka je ku yi magana, gani yake yi kamar ba aurenta zan yi ba, Alhaji tana bani shawarari masu kyau, tana da kirki sosai"
"Allah ya kaimu lahadin, zan je in sha Allah, ko a lokacin suka ce sai a É—aura, Ubangiji Allah ya sa abokiyar zama ta gari ce"
Raihan ya sosa kai ya ce "Alhaji saura abu É—aya"
"Ok to ina jinka"
Raihan ya ce "Dan Allah kar ka gaya wa mami sai maganar ta faɗa, ban san yadda za ta karɓi maganar ba.
I really have to marry her, Alhaji rayuwar ummi akwai ƙalubale da ban tausayi, dan Allah ka tsaya mini"
Alhaji Tahir ya jinjina kai ya ce "In dai ni ne ka san baka da matsala da ni, ko tsohuwa ka ce kana so, zan wuce maka gaba in dai tana da tarbiyya, kuma ko a hoto, ni yarinyar ban ga aibunta ba, ko ta girmeka in dai kana son ta shikenan, ai soyayya ba ƙarya ba ce raihan, mune muke barin al'ada na rage mana jin daɗin abun da addini ya halatta mana. Allah ya sanya alkhairi ango"
Raihan ya sunkuyar da kai yana murmushi, wani irin farinciki na ratsa zuciyarsa.
Dr. Ya manta da batun haɗuwarsa da raihan, dan ko ummi ma bai nema da maganar ba, sai dai ya rage ganin gilmawarta ko a gidan, ya bar hakan a wataƙila takurar farida ce ta saka ta ƙara takura kanta.
Washegari raihan ya tafi wurin aikin Ummi, amma manager ya ce "Ai ummi yau kusan kwana uku ba ta zo ba, ni ban sani ba, ba ta da lafiya ne ko ya aka yi ban sani ba, kawai ta ce mini za ta je screening, tun ranar ba ta sake zuwa ba, na zata ma ko ba ta gama ba ne ba".
Raihan ya yi shiru ya ce "kira ta a waya ka ce ko ta dawo aiki, ko zaka koreta".
Manager ya zare ido ya ce "Yayarta ka za a kora? Idan ban koreta ba ni ai yayana ya kore ni, ka san yadda yake yabawa ƙoƙarin ta, da yabawa amanarta"
Raihan ya ce "Dan Allah ka bar wannan maganar, kawai ni dai taimakon da zaka yi mini kenan, ka ce lallai ta dawo aiki.
"Ba zan yi ba, ba kun fi kusa ba"
Raihan ya sassauta murya ya ce "Haba manager, dan Allah ka taimaka Please"
"Da ka ce ba ka ji? Zan yi mata magana, amma ba dan halinka ba, kuma ba zan ce zan wani koreta ba, zan dai yi ƙoƙarin ta dawo ɗin"
Raihan yayi dariya ya ce "Allah ya bar mini manager"
Manager kawai yayi murmushi, ya cigaba da aikin da yakamata ace ummi ce ta yi.
Sai dai manager bai kai ga yin hakan ba, washegari sai ga ummin ta zo aiki, sai dai ta rame sosai, kallo É—aya zaka yi mata ka san akwai tashin hankali a fuskar ta.
Manager ya kira raihan a waya, ya gaya masa ummi ta zo.
Bai ja dogon lokaci ba, ya daidaici lokacin tashin ta ya kusa, sannan ya tafi.
Ta fito daga wurin aikin, yana nesa kaÉ—an da ita yana kallonta, tana tafe a hankali kamar mara lafiya.
Zuwa yayi ya sha gabanta da motar, ta tsaya tana kallon motar, ya sauke glass É—in motar suka haÉ—a ido, sai da ta É—an razana, ya buÉ—e mata motar ba tare da ya ce mata uffan ba.
Jikin ummi ya yi sanyi sosai da ganin raihan, dan ba ta taɓa tsammani ba, kamar mai jin tsoro haka ta ɗosana ta shiga motar.
"Ta tabatta dai ba kya so na ko ummi? Kina iya rabuwa da ni, baki damu da halin da zan shiga ba, kin ce mu rabu, ko nema na baki sake yi ba, rashin muhimmancina har ya kai haka kenan ko Salma?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"Shikenan, ni gashi na sake biyo ki ai, ranar lahadi Alhaji zai zo wurin dr."
A razane ta kalleshi, tana ƙifta ido.
"Eh, mun haɗu da dr. Shekaranjiya, na zo wurinki kin ƙi ɗaga wayata, mun yi magana ya ce Alhaji ya zo su yi magana"
"Wai da gaske aurata zaka yi?" Tayi maganar cikin matuƙar rauni.
"Gashi ina gaya miki, kin zata da wasa nake yi? Na san wataƙila ba ni ne irin mijin da ki ke so ba, na san zaki ga na yi miki yarinta da yawa, amma har cikin raina nake jin zan iya aurenki na riƙe ki da kulawa da girmamawa".
"Raihan zaka aureni ina bazawara"
"Kar ki sake kawo mini maganar kin taɓa aure, zuciyata zata fashe, ummi kina wasa da son da nake yi miki kina ganin kamar wasa ko? Hubban shadidan na kira shi, ban taɓa jin damuwa da takura a kan son wani abu ba kamar ke, kawai in ganki a kusa da ni, shi zai kawo mini cikakkiyar nutsuwa"
Tayi shiru tana wasa da zoben hannunta.
"Meya rabaku da tsohon mijinki?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Kakarmu ce ta haÉ—a auren, ba ya so na, an kai kuÉ—in aurensa aka fasa, shi ne ya aure ni"
Ya ce "Ya yi wa kansa, ni ina so. Ki saka aurenmu a addu'a salma, in sha Allah zai yi albarka, wata nawa ki ke so a saka na ji kin ce a matse ki ke ko?"
"Ai wannan maganar dr. Ba tawa ba"
Ya ce "Haka ne, nima na matsun ne, in ga kin zama tawa" ummi dai ta yi shiru tana tunanin ko dai ba da gaske raihan yake ba.
"Na ga gidan tv nan sun kira screening, manager ya ce mini kin je, ya ku ka yi da su?"
Ta É—an rausayar da kai ta ce "Kyawawa suke so, ba wanda sai an ta saka musu filter ba"
"Kamar yaya kenan?"
"Haka mai wurin ya ce"
Kawai ta ga yayi parking É—in motar, ya kalli ummi ya ce "Ke kuma ki ka ce masa me?"
Tayi shiru tana kallon sa.
"Magana nake yi miki?"
"Ni ban ce komai ba"
Raihan ya ce "Sai ki ka tsaya kina kuka ko? Gwanar kuka"
Ta ce "A'a ai ban yi kukan ba"
Ya danƙo kunnenta ya ce "Wallahi ummi, duk wanda ya kuma kushe mini ke, ki ka tsaya kina kallonsa, baki ɗau wani mataki ba, sai na huce a kan ki, kamar na fi ki jin takaici idan aka kushe mini ke. Ke kina da baki, amma ba zaki iya magana ba? Tun da ba aikin zai ɗauke ki ba, sai ki wanke shi tas ki bar wurin, atleast ai kya ce masa Allah ya sa kyawawan su durƙusar da tashar, ko ki ce masa ya koma islamiyya a karanta masa Allah ne mahalicci"
Sosai ya riƙe mata kunne, ta kai hannu ta riƙe hannunsa da ya riƙe mata kunnen cikin muryarta mai cike da iyayi da shagwaɓa ta ce "Babba ne fa"
Ya sakar mata kunnen ya ce "Babban banza ba, tun da ba shi da hankali"
Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "My wife"
Ta ce 'Na shiga uku"
"A'a ko ɗaya baki shiga ba, ko ba ni ki ke so ba, dan Allah ki yi haƙuri mu karɓi ƙaddara a yadda ta zo mana, bamu san dalilin da Allah ya sa ya haɗa mu ba, kar taurin kanki yayi delaying zuwan wasu bayin Allah duniya" tayi burus kamar ba da ita yake magana ba.
"A haka kamar saliha, nan kuwa taurin kai a cikin ki kamar me".
Ranar lahadi gaba ɗaya dr. Ya manta da batun zai yi baƙi, dan ya faɗi maganar ne dan ya kori raihan, ummi ma ta kasa zaune ta kasa tsaye, dan raihan ya tabattar mata da ranar lahadin Alhajinsu zai zo.
Ƙarfe sha ɗaya na safe, Abdul ya je ya sanarwa dr. Yayi baƙi.
Ya fita ya ga manyan mutane a manyan motoci, suka gaisa, Alhaji Tahir ya ce "Ka manta zaka yi baƙi ne? Kodayake ƴan boko sai kun bawa mutum lokaci yake zuwa, Tahir ne baban sirikinka Muhammad da ka ce kana son ganina".
Dr. Ya ce "Subhanallah, Allah sarki bisimillah ku shigo"Â suka bi bayan dr. Zuwa cikin gida.
Har cikin falo, ya fita da sauri ya samu Abdul ya bashi kuÉ—i, ya ce ya sayo musu ruwa da lemuka.
Sun daɗe suna hira da Alhaji Tahir, da wasu mutane su biyu ɗaya ƙaninsa ɗaya abokinsa.
Dr. Ya sha mamakin jin waye raihan, tare da yi wa ummi fatan, Allah ya sa ƙarshen wahalarta ne ya zo.
Yana zuwa ya tafi sashin Alhaji, dan kwanakin nan kusan kullum Alhajin yana gida, ya daki sa'a shikaÉ—ai ya tarar a sashin nasa.
Alhaji Tahir ya gyara zaman tabaran sa, ya ce "Ya aka yi ne? Yanayin farinciki haÉ—e da damuwa a fuskar babban mutum"
Raihan ya je ya zauna a kusa da shi, ya ce "Kowanne akwai Alhaji"
"Bani labari"
Ya ciro wayarsa, ya nemo hoton ummi da yayi mata, lokacin da suka sayo dogwayen riguna, ya ce "Alhaji ka ga wannan"
Alhaji ya karɓi wayar, ya ƙare wa hoton kallo ya ce "Na gani, meyafaru?"
"Alhaji tana da kyau?"
Ya ce "Masha Allah, very beautiful kuwa, da gani kuma tana da kunya"
"Ita nake son aura Alhaji, zaka nema mini aurenta?"
Alhaji Tahir ya kalli raihan yayi murmushi ya ce "Babban mutum wannan ai matar manyan ce, anya ba ka yi tsaurin ido ba kuwa?"
"A'a Alhaji, ai nima babban mutum ne, dan Allah tayi? Wallahi mutuniyar kirki ce"
Alhaji ya yi shiru ya ce "Ai ni kallon sani nake yi mata ma"
Raihan ya ce "Eh, ƙawar maryam ce, amma ita ba ta girme ni ba, shekrunmu ɗaya da ita, kuma mutuniyar kirki ce ka tambayi Hajiya ma ka ji"
Alhaji Tahir ya dafa kafaÉ—ar raihan ya ce "Easy my dear, in dai kana son ta tayi mini, za a nemi aurenta in dai za a bamu"
Raihan ya washe baki ya ce "Babanta ya ce ranar Sunday wai ka je ku yi magana, gani yake yi kamar ba aurenta zan yi ba, Alhaji tana bani shawarari masu kyau, tana da kirki sosai"
"Allah ya kaimu lahadin, zan je in sha Allah, ko a lokacin suka ce sai a É—aura, Ubangiji Allah ya sa abokiyar zama ta gari ce"
Raihan ya sosa kai ya ce "Alhaji saura abu É—aya"
"Ok to ina jinka"
Raihan ya ce "Dan Allah kar ka gaya wa mami sai maganar ta faɗa, ban san yadda za ta karɓi maganar ba.
I really have to marry her, Alhaji rayuwar ummi akwai ƙalubale da ban tausayi, dan Allah ka tsaya mini"
Alhaji Tahir ya jinjina kai ya ce "In dai ni ne ka san baka da matsala da ni, ko tsohuwa ka ce kana so, zan wuce maka gaba in dai tana da tarbiyya, kuma ko a hoto, ni yarinyar ban ga aibunta ba, ko ta girmeka in dai kana son ta shikenan, ai soyayya ba ƙarya ba ce raihan, mune muke barin al'ada na rage mana jin daɗin abun da addini ya halatta mana. Allah ya sanya alkhairi ango"
Raihan ya sunkuyar da kai yana murmushi, wani irin farinciki na ratsa zuciyarsa.
Dr. Ya manta da batun haɗuwarsa da raihan, dan ko ummi ma bai nema da maganar ba, sai dai ya rage ganin gilmawarta ko a gidan, ya bar hakan a wataƙila takurar farida ce ta saka ta ƙara takura kanta.
Washegari raihan ya tafi wurin aikin Ummi, amma manager ya ce "Ai ummi yau kusan kwana uku ba ta zo ba, ni ban sani ba, ba ta da lafiya ne ko ya aka yi ban sani ba, kawai ta ce mini za ta je screening, tun ranar ba ta sake zuwa ba, na zata ma ko ba ta gama ba ne ba".
Raihan ya yi shiru ya ce "kira ta a waya ka ce ko ta dawo aiki, ko zaka koreta".
Manager ya zare ido ya ce "Yayarta ka za a kora? Idan ban koreta ba ni ai yayana ya kore ni, ka san yadda yake yabawa ƙoƙarin ta, da yabawa amanarta"
Raihan ya ce "Dan Allah ka bar wannan maganar, kawai ni dai taimakon da zaka yi mini kenan, ka ce lallai ta dawo aiki.
"Ba zan yi ba, ba kun fi kusa ba"
Raihan ya sassauta murya ya ce "Haba manager, dan Allah ka taimaka Please"
"Da ka ce ba ka ji? Zan yi mata magana, amma ba dan halinka ba, kuma ba zan ce zan wani koreta ba, zan dai yi ƙoƙarin ta dawo ɗin"
Raihan yayi dariya ya ce "Allah ya bar mini manager"
Manager kawai yayi murmushi, ya cigaba da aikin da yakamata ace ummi ce ta yi.
Sai dai manager bai kai ga yin hakan ba, washegari sai ga ummin ta zo aiki, sai dai ta rame sosai, kallo É—aya zaka yi mata ka san akwai tashin hankali a fuskar ta.
Manager ya kira raihan a waya, ya gaya masa ummi ta zo.
Bai ja dogon lokaci ba, ya daidaici lokacin tashin ta ya kusa, sannan ya tafi.
Ta fito daga wurin aikin, yana nesa kaÉ—an da ita yana kallonta, tana tafe a hankali kamar mara lafiya.
Zuwa yayi ya sha gabanta da motar, ta tsaya tana kallon motar, ya sauke glass É—in motar suka haÉ—a ido, sai da ta É—an razana, ya buÉ—e mata motar ba tare da ya ce mata uffan ba.
Jikin ummi ya yi sanyi sosai da ganin raihan, dan ba ta taɓa tsammani ba, kamar mai jin tsoro haka ta ɗosana ta shiga motar.
"Ta tabatta dai ba kya so na ko ummi? Kina iya rabuwa da ni, baki damu da halin da zan shiga ba, kin ce mu rabu, ko nema na baki sake yi ba, rashin muhimmancina har ya kai haka kenan ko Salma?" Ta girgiza masa kai alamar a'a.
"Shikenan, ni gashi na sake biyo ki ai, ranar lahadi Alhaji zai zo wurin dr."
A razane ta kalleshi, tana ƙifta ido.
"Eh, mun haɗu da dr. Shekaranjiya, na zo wurinki kin ƙi ɗaga wayata, mun yi magana ya ce Alhaji ya zo su yi magana"
"Wai da gaske aurata zaka yi?" Tayi maganar cikin matuƙar rauni.
"Gashi ina gaya miki, kin zata da wasa nake yi? Na san wataƙila ba ni ne irin mijin da ki ke so ba, na san zaki ga na yi miki yarinta da yawa, amma har cikin raina nake jin zan iya aurenki na riƙe ki da kulawa da girmamawa".
"Raihan zaka aureni ina bazawara"
"Kar ki sake kawo mini maganar kin taɓa aure, zuciyata zata fashe, ummi kina wasa da son da nake yi miki kina ganin kamar wasa ko? Hubban shadidan na kira shi, ban taɓa jin damuwa da takura a kan son wani abu ba kamar ke, kawai in ganki a kusa da ni, shi zai kawo mini cikakkiyar nutsuwa"
Tayi shiru tana wasa da zoben hannunta.
"Meya rabaku da tsohon mijinki?"
Tayi ajiyar zuciya ta ce "Kakarmu ce ta haÉ—a auren, ba ya so na, an kai kuÉ—in aurensa aka fasa, shi ne ya aure ni"
Ya ce "Ya yi wa kansa, ni ina so. Ki saka aurenmu a addu'a salma, in sha Allah zai yi albarka, wata nawa ki ke so a saka na ji kin ce a matse ki ke ko?"
"Ai wannan maganar dr. Ba tawa ba"
Ya ce "Haka ne, nima na matsun ne, in ga kin zama tawa" ummi dai ta yi shiru tana tunanin ko dai ba da gaske raihan yake ba.
"Na ga gidan tv nan sun kira screening, manager ya ce mini kin je, ya ku ka yi da su?"
Ta É—an rausayar da kai ta ce "Kyawawa suke so, ba wanda sai an ta saka musu filter ba"
"Kamar yaya kenan?"
"Haka mai wurin ya ce"
Kawai ta ga yayi parking É—in motar, ya kalli ummi ya ce "Ke kuma ki ka ce masa me?"
Tayi shiru tana kallon sa.
"Magana nake yi miki?"
"Ni ban ce komai ba"
Raihan ya ce "Sai ki ka tsaya kina kuka ko? Gwanar kuka"
Ta ce "A'a ai ban yi kukan ba"
Ya danƙo kunnenta ya ce "Wallahi ummi, duk wanda ya kuma kushe mini ke, ki ka tsaya kina kallonsa, baki ɗau wani mataki ba, sai na huce a kan ki, kamar na fi ki jin takaici idan aka kushe mini ke. Ke kina da baki, amma ba zaki iya magana ba? Tun da ba aikin zai ɗauke ki ba, sai ki wanke shi tas ki bar wurin, atleast ai kya ce masa Allah ya sa kyawawan su durƙusar da tashar, ko ki ce masa ya koma islamiyya a karanta masa Allah ne mahalicci"
Sosai ya riƙe mata kunne, ta kai hannu ta riƙe hannunsa da ya riƙe mata kunnen cikin muryarta mai cike da iyayi da shagwaɓa ta ce "Babba ne fa"
Ya sakar mata kunnen ya ce "Babban banza ba, tun da ba shi da hankali"
Sai kuma ya kwantar da murya ya ce "My wife"
Ta ce 'Na shiga uku"
"A'a ko ɗaya baki shiga ba, ko ba ni ki ke so ba, dan Allah ki yi haƙuri mu karɓi ƙaddara a yadda ta zo mana, bamu san dalilin da Allah ya sa ya haɗa mu ba, kar taurin kanki yayi delaying zuwan wasu bayin Allah duniya" tayi burus kamar ba da ita yake magana ba.
"A haka kamar saliha, nan kuwa taurin kai a cikin ki kamar me".
Ranar lahadi gaba ɗaya dr. Ya manta da batun zai yi baƙi, dan ya faɗi maganar ne dan ya kori raihan, ummi ma ta kasa zaune ta kasa tsaye, dan raihan ya tabattar mata da ranar lahadin Alhajinsu zai zo.
Ƙarfe sha ɗaya na safe, Abdul ya je ya sanarwa dr. Yayi baƙi.
Ya fita ya ga manyan mutane a manyan motoci, suka gaisa, Alhaji Tahir ya ce "Ka manta zaka yi baƙi ne? Kodayake ƴan boko sai kun bawa mutum lokaci yake zuwa, Tahir ne baban sirikinka Muhammad da ka ce kana son ganina".
Dr. Ya ce "Subhanallah, Allah sarki bisimillah ku shigo"Â suka bi bayan dr. Zuwa cikin gida.
Har cikin falo, ya fita da sauri ya samu Abdul ya bashi kuÉ—i, ya ce ya sayo musu ruwa da lemuka.
Sun daɗe suna hira da Alhaji Tahir, da wasu mutane su biyu ɗaya ƙaninsa ɗaya abokinsa.
Dr. Ya sha mamakin jin waye raihan, tare da yi wa ummi fatan, Allah ya sa ƙarshen wahalarta ne ya zo.