Sashe 61
Triplets Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta fara magana a nutse, duk yunwa ya kwakulesu, da kyar ita ma voice nata yake fita, "A'isha ban cuce ki ba, kuma abin da ya faru a yanzu kamata ya yi ma ya zama miki darasi, kamata ya yi ma ki ɗauki haske, yanzu tsakaninki da Allah kuɗi zai kai naira nawa kika kawowa wannan tsinanniyar gidan? Na san ba zaki iya kirgawa ba, duk da wannan kuɗi da kika kawo musu, bai sa sun ji tausayinki sun san suna karuwa dake ba, bai sa sun agaza miki sun yafe miki ba, ina son ki sani A'isha, sun gama dake ne, yanzu baki da amfani a wajensu, sun san cewa yanzu ba'a yayinki, sun gama ɗebar abin da zasu ɗeba a tattare dake, yanzu kin tashi aiki, ke da bakin ki a nan kika gaya mini, idan mace ta ragwargwaɓe zuwa suke yi su jefar da ita a wani garin, hakan yana nufin kenan idan mace ta gama biya musu bukatarsu to bata da amfani a wajensu, ki godewa Allah da ya nuna miki da idanunki kika gani tun da sauran numfashinki, wlh Aisha bariki bata da wata amfani, jiya dai kinga yayinki ake yi, kowa rububinki yake yi, yau kuma fa? Kowa ya gujeki, saboda komai naki ya kare, da zama kikayi, kika hakura kika yi aure, wlh koma ya zaki koma, sai an ganki da daraja tun da a ɗakin mijinki ki ke, yanzu fa? Ina mai tabbatar miki idan kika mutu, tamkar idan dabba ya mutu haka zasu ɗauke ki su jefar, kin sani ba wai baki sani ba, ke da bakin ki kike bani labari, to yana da kyau ki sani, duk wata ƴar bariki or ɗan bariki, mutuwar walanci suke yi, a lalace suke karewa, yana da kyau ki nitsar da tunaninki waje guda, ki san abin da kike yi, baa yin kuɗi da jiki, duk wanda ya ce miki ana yi karya yake yi miki, kuɗin ba zasu yi albarka ba, ni ina son ki tuba ne, ki koma ga Allah, ina miki sha'awar samun rahmar Ubangiji, yanzu sai Allah ne kaɗai yasan me yake damunki, wata kila wani cuta wani kafurin mutun ya sanya miki, kinga kuma su ba damuwrasu bane, idan cuta ta kamaki, ki mutu dan kanki, su dai tun da kin biya kuɗin da suka saye ki, to babu ruwansu, wlh yana da kyau duk masu shirin faɗawa irin wannan rayuwa ta bariki su sani babu wata nasara a saɓon Allah, babu in da zaka je, babu kuma abin da zaka cinma matukar zaka kauce hanyar Allah Manzonsa, duk wuya duk daɗi, ka tsaya a faɗar Allah da Manzonsa, to a nan ne zaka ci riba biyu, wato duniya da lahira, wlh ko yau na mutu, ba zan taɓa danasanin zuwata duniya ba, saboda ina iya kan bakin ƙoƙarina wajen ganin na tsaya a kan koyarwar manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ban taɓa batawa iyayena rai ba, bantaɓa bari Sallah ya wuce ni ba, azumi, sadaka, dukka ina iya bakin ƙoƙari, har na rabu da iyayena albarka suke saka mini, to me yafi wannan a duniya? Ni nasan jarabawa ce Allah ya jarrabeni da shi na zuwa na wannan gidan, idan da na gaya miki ni ƴar wace ce, ke da kanki zaki ce eh tabbas jarabawa ce Allah ya jarrabeni da shi, kuma ina ƙoƙarin naga na ci wannan jarabawa, bana neman taimakon kowa sai na mahaliccina, baya barci, yana kallon duk abin da yake faruwa damu, da izininsa kuma zai kawo mana mafita, zai dafa mana, dan addu'a bata faɗuwa kasa banza, sai dai jinkirin amsawa, to ina mai........".
Bata kai karshen maganar ba ta dakata sakamon buɗe kofar da ta ji ana yi, cikin sauri suka miƙe tsaye da kyar, wani irin jiri ne ya ɗebesu saboda bala'in yunwa, cikin sauri ta dafe bango dan kada ta faɗi kasa, da kyar da kyar suke jan numfashi, idanu duk sun rena fata, dama Jehan akwai dara daran idanu, da ta rame sai suka kara fitowa kwala kwala da su.
Zinariya ce ta buɗe kofar, kamar kullun kajeren jeans fashion trouser ne a jikinta, sai riga mai hannun vest baki, tasha wannan uwar make up ɗin nata, ga uban attachment da ta zuba a kai kamar wani bukkar shaiɗanu, fuska kamar an ɗaye bayan kadangare, saboda bleaching ta cinye fatar, naman fuskar ta yi jawur, sai kuma ta rinƙa damɓara uban Foundation, abin kamar kayi ta kwara amai idan ka gani, ga wani uban hujin hanci da ta yi, sai ta wani tabka katon ɗangunne kamar na Indiyawa, to su indiyawa yana musu kyau idan suka sanya, ita kuwa, sai ya yi mata wani sundumdum a fuska kamar garman shanu, abu ba kyan gani, babban abin haushi kuma abin amai shi ne eyelashes da suke labkawa, abu kamar bindin kaza, a tsaitsaye yana zagin wadda suke kallah, harta Hajiyar daɗi irin dressing nata kena, kayan haushi, kamar ya finciko wannan uban ɗan kunnan na hancin nan nasu ka tuge har da hancin kowa ma ya huta shegu, sai uban warin man bleaching suke yi, kamshin turaren da suka sanya daban, warin man bleaching daban, dama kuma haka yake yi, shegen wari masu bleaching nan suke yi, ko sun sanya turare baya kau da warin, sune basu ganewa, na kusa da su kuma basu gaya musu gaskiya, dan tsoron kada su ɓata alakar dake tsakaninsu, hmmmm ai duk abin da Allah ya haramta ka ce zaka yi, to fa kana tsaka mai wuya, ka rinƙa faɗawa wahala da masifu kala kala, Allah dai ya karemu, yasa mu tsaya a iya in da Ubangiji ya tsai damu Amin.
Kallon banza ta watsa musu kafin ta ce "Ku wuce ku fito". Ta kai karshen maganar tare da juyawa ta nufi waje, "Ai na É—auka barinmu zaku yi mu mutu a ciki, ban yi zaton zaku buÉ—e mu ba ai". Cewar Jehan da baki baya shiru, da kyar maganar yake fita, amma sai ta yi tsiwa.
"Ke kada ki kuskura ki ce zaki gaya mini wata magana a nan, wlh yanzun nan sai mu saɓa miki kamanni, ke wato bakin ki ba zai yi shiru ba ko?, To wlh ki sani nan bariki kikazo, akwai iyayen iyayenki a rashin kunya, yanzu zamu gyara miki zama, ku yi maza ku fito min nan tun ban ci uban yarinya ba dan ubanta!". Tana magana tana hura hanci takar balo balo, dama ga hancin ba'a magana.
"Babu in da zanje, kuma da kike wannan magana dama an gaya miki ni mara tarbiya ce irinki da zaki ce kunfini rashin kunya, wlh ina mai baku shawara da kuji tsoron Allah, ku sani akwai mutuwa, dan ba zance muku akwai tsufa, saboda kun rigada kun tsufa kun tsofe, ke a yadda kike yanzun nan saboda Allah ba kamata ya yi a ce ewar haka kina saman dadduma kina addu'a Allah yasa ki cika da imani ba, duk kin tsufa kin zagwanye, kadangarun bariki sun zuke miki ruwan kai da jinin jiki, amma har yanzu sheiɗan na zugaki na cewa kina da mamora ko? To wlh ki sani babu wata mamora da ta rage a jikinki face azaba da kika tana da wa kanki da kanki, ke da kanki idan zaki gayawa kanki gaskiya ki ajiye zancen sheiɗan a gefe, kin san cewa bai wuci taku biyu ya rage miki zuwa kabari ba, shekarunki nawa a duniyar nan? Kin taɓa waigawa ki duba a waƴan nan shekarun na baya da kika yi me kika aikata na alkhari? Wai ko dai kema kina ɗaya daga cikin waƴan da suke tunanin sun zo duniya kenan babu komawa? To idan ma kina ɗaya daga ciki ki sani dai duniya kam akwai ranar barinta, mutuwa gaskiya ce, yanzu ma tana iya ɗauke ki, bata jira sai an shirya, da a shirya da kar a shirya duk sai ta ɗauka idan lokacin ya yi, babu kuma uban da ya isa ya hanata ɗauka, to tun da sauran ni'ima ta numfashi da Ubangiji ya yi muku is better for you da ki tuba, ki tuba ki koma ga Allah, Allah gafurur rahim ne, zai karɓi tubanki!!".
A fusace ta juyo ta dawo cikin toilet ɗin, ranta a matukar ɓace ta ɗaga hannu zata zabga mata mari, nan take zuciyarta ya tuna mata da Hajiyar daɗi na dawowa gobe, hakan ce kuma tasa ta buɗe su, idan Hajiyar daɗi ta dawo da sami wani tabo a jikin su ukun nan, wato JEHAN, ADIVA, MARYAM, su da aka kawo sabbin, basu biya kuɗinsu ba, to sai ta yi wa su Zinariyar mummunar hukunci, dan kuwa ita bata ɗaukar asara, bata yarda da asara ko mai kankantar sa, shiyasa suka yi sauri tun yau suka buɗe su Jehan ɗin, zasu duba lafiyarsu da sauran abin da ya dace kafin hajiya ta iso ta same su lafiya, daga nan kuma su umarce su da kada su kuskura su gayawa hajiya abin da suka yi musu, idan ba haka ba wlh sai sun bi dare sun kashe su. BARIKI KENAN, BABU MUTUNCI KO KAƊAN.
Tuna hakan yasa bata bari Jehan ɗin ba, ta juya rai a ɓace ta koma cikin ɗakin tana jiran fitowarsu, da kyar Maryam da Adiva suka iya jan kafafunsu suka fito cikin ɗakin, ita kuma A'isha ko motsin kirki bata iya yi, komawa kusa da ita Jehan ta yi ta zauna, sai jiransu Zinariya take yi, amma shiru Jehan taki fitowa, daga karshe dai ta taso ta dawo cikin toilet ɗin, cike da bada umarni ta ce "Ke Jehan ki wuce mu tafi".
A kule rai a matukar ɓace ta ce "Babu in da zanje marasa imani kawai, wlh in dai baku ɗauki A'isha kun kaita cikin bedroom kun kwantar da ita a gadonta ba, to sai dai mu mutu ni da ita a nan!". Basu da zaɓi dole su fito da Aisha ba dan sun so ba, da farko basu yi niyar ko kallon in da take ba, amma da Jehan ta kafe akan sai sun fitar da ita zata fito ita ma, dan dole suka yi hakan dan gudun su yi laifi wajen Hajiya.
Bata kai karshen maganar ba ta dakata sakamon buɗe kofar da ta ji ana yi, cikin sauri suka miƙe tsaye da kyar, wani irin jiri ne ya ɗebesu saboda bala'in yunwa, cikin sauri ta dafe bango dan kada ta faɗi kasa, da kyar da kyar suke jan numfashi, idanu duk sun rena fata, dama Jehan akwai dara daran idanu, da ta rame sai suka kara fitowa kwala kwala da su.
Zinariya ce ta buɗe kofar, kamar kullun kajeren jeans fashion trouser ne a jikinta, sai riga mai hannun vest baki, tasha wannan uwar make up ɗin nata, ga uban attachment da ta zuba a kai kamar wani bukkar shaiɗanu, fuska kamar an ɗaye bayan kadangare, saboda bleaching ta cinye fatar, naman fuskar ta yi jawur, sai kuma ta rinƙa damɓara uban Foundation, abin kamar kayi ta kwara amai idan ka gani, ga wani uban hujin hanci da ta yi, sai ta wani tabka katon ɗangunne kamar na Indiyawa, to su indiyawa yana musu kyau idan suka sanya, ita kuwa, sai ya yi mata wani sundumdum a fuska kamar garman shanu, abu ba kyan gani, babban abin haushi kuma abin amai shi ne eyelashes da suke labkawa, abu kamar bindin kaza, a tsaitsaye yana zagin wadda suke kallah, harta Hajiyar daɗi irin dressing nata kena, kayan haushi, kamar ya finciko wannan uban ɗan kunnan na hancin nan nasu ka tuge har da hancin kowa ma ya huta shegu, sai uban warin man bleaching suke yi, kamshin turaren da suka sanya daban, warin man bleaching daban, dama kuma haka yake yi, shegen wari masu bleaching nan suke yi, ko sun sanya turare baya kau da warin, sune basu ganewa, na kusa da su kuma basu gaya musu gaskiya, dan tsoron kada su ɓata alakar dake tsakaninsu, hmmmm ai duk abin da Allah ya haramta ka ce zaka yi, to fa kana tsaka mai wuya, ka rinƙa faɗawa wahala da masifu kala kala, Allah dai ya karemu, yasa mu tsaya a iya in da Ubangiji ya tsai damu Amin.
Kallon banza ta watsa musu kafin ta ce "Ku wuce ku fito". Ta kai karshen maganar tare da juyawa ta nufi waje, "Ai na É—auka barinmu zaku yi mu mutu a ciki, ban yi zaton zaku buÉ—e mu ba ai". Cewar Jehan da baki baya shiru, da kyar maganar yake fita, amma sai ta yi tsiwa.
"Ke kada ki kuskura ki ce zaki gaya mini wata magana a nan, wlh yanzun nan sai mu saɓa miki kamanni, ke wato bakin ki ba zai yi shiru ba ko?, To wlh ki sani nan bariki kikazo, akwai iyayen iyayenki a rashin kunya, yanzu zamu gyara miki zama, ku yi maza ku fito min nan tun ban ci uban yarinya ba dan ubanta!". Tana magana tana hura hanci takar balo balo, dama ga hancin ba'a magana.
"Babu in da zanje, kuma da kike wannan magana dama an gaya miki ni mara tarbiya ce irinki da zaki ce kunfini rashin kunya, wlh ina mai baku shawara da kuji tsoron Allah, ku sani akwai mutuwa, dan ba zance muku akwai tsufa, saboda kun rigada kun tsufa kun tsofe, ke a yadda kike yanzun nan saboda Allah ba kamata ya yi a ce ewar haka kina saman dadduma kina addu'a Allah yasa ki cika da imani ba, duk kin tsufa kin zagwanye, kadangarun bariki sun zuke miki ruwan kai da jinin jiki, amma har yanzu sheiɗan na zugaki na cewa kina da mamora ko? To wlh ki sani babu wata mamora da ta rage a jikinki face azaba da kika tana da wa kanki da kanki, ke da kanki idan zaki gayawa kanki gaskiya ki ajiye zancen sheiɗan a gefe, kin san cewa bai wuci taku biyu ya rage miki zuwa kabari ba, shekarunki nawa a duniyar nan? Kin taɓa waigawa ki duba a waƴan nan shekarun na baya da kika yi me kika aikata na alkhari? Wai ko dai kema kina ɗaya daga cikin waƴan da suke tunanin sun zo duniya kenan babu komawa? To idan ma kina ɗaya daga ciki ki sani dai duniya kam akwai ranar barinta, mutuwa gaskiya ce, yanzu ma tana iya ɗauke ki, bata jira sai an shirya, da a shirya da kar a shirya duk sai ta ɗauka idan lokacin ya yi, babu kuma uban da ya isa ya hanata ɗauka, to tun da sauran ni'ima ta numfashi da Ubangiji ya yi muku is better for you da ki tuba, ki tuba ki koma ga Allah, Allah gafurur rahim ne, zai karɓi tubanki!!".
A fusace ta juyo ta dawo cikin toilet ɗin, ranta a matukar ɓace ta ɗaga hannu zata zabga mata mari, nan take zuciyarta ya tuna mata da Hajiyar daɗi na dawowa gobe, hakan ce kuma tasa ta buɗe su, idan Hajiyar daɗi ta dawo da sami wani tabo a jikin su ukun nan, wato JEHAN, ADIVA, MARYAM, su da aka kawo sabbin, basu biya kuɗinsu ba, to sai ta yi wa su Zinariyar mummunar hukunci, dan kuwa ita bata ɗaukar asara, bata yarda da asara ko mai kankantar sa, shiyasa suka yi sauri tun yau suka buɗe su Jehan ɗin, zasu duba lafiyarsu da sauran abin da ya dace kafin hajiya ta iso ta same su lafiya, daga nan kuma su umarce su da kada su kuskura su gayawa hajiya abin da suka yi musu, idan ba haka ba wlh sai sun bi dare sun kashe su. BARIKI KENAN, BABU MUTUNCI KO KAƊAN.
Tuna hakan yasa bata bari Jehan ɗin ba, ta juya rai a ɓace ta koma cikin ɗakin tana jiran fitowarsu, da kyar Maryam da Adiva suka iya jan kafafunsu suka fito cikin ɗakin, ita kuma A'isha ko motsin kirki bata iya yi, komawa kusa da ita Jehan ta yi ta zauna, sai jiransu Zinariya take yi, amma shiru Jehan taki fitowa, daga karshe dai ta taso ta dawo cikin toilet ɗin, cike da bada umarni ta ce "Ke Jehan ki wuce mu tafi".
A kule rai a matukar ɓace ta ce "Babu in da zanje marasa imani kawai, wlh in dai baku ɗauki A'isha kun kaita cikin bedroom kun kwantar da ita a gadonta ba, to sai dai mu mutu ni da ita a nan!". Basu da zaɓi dole su fito da Aisha ba dan sun so ba, da farko basu yi niyar ko kallon in da take ba, amma da Jehan ta kafe akan sai sun fitar da ita zata fito ita ma, dan dole suka yi hakan dan gudun su yi laifi wajen Hajiya.