Sashe 4
Abunda Ke Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dagata bangaren su taawure kuwa tunda tajanye hannun yaran ta suka bar filin wasa tafiya kawai sukeyi suna masu tsaga cikin jejin da zaibi dasu madaidacin rugarsu dake can can gefen babban rafin kauyen inda babn filin noman su da tsaunukan kiwon dabbobinsu yake kusa azagaye dasu, they are kind of isolated daga main mutanen kauyen ko abu zasu saya sai sun yi tafiya mai dan nisa suke isowa kasuwa kusan ince rugarsu ne karshe a kauyen kusa da hanyar barin gari gabaki daya, gabansu kuma babban ruwa da jejine me duhun gske dake zagaye su.
tafiya suke da sauri sauri tareda wani irin rauni da kuma fargaba acikin zuciyoyinsu, koina yay shiru dan kusan kowa a kauyen anacan fili wajen gagarimin wasa, cikin sassarfa da sauri taawure tariko hannun karamar yarta ayanah gam tana janta ahnkli nan inda bakajin karar komi a hanyar face sanyin iskan yammaci da kukan tsutsaye tareda dirar sautin ajiyan zuciyar taawure datake saukeshi akai akai jin raunattecen ajiyar zuciyar da ayanah takeja wanda yagama narkewa cikin tsoro da matsanancin damuwa. daga ita har mahaifyarsun a dame suke da tunanin irin hukuncin da juma zai zo gida ya dauka akan su da kuma inaayah.
ita kuwa inayahr ko ajikinta daf dasu take tafiyarta zucyarta karau dan tun basu karasa barin filin wasan bama tabi ta shanye hawayenta idonta yabi ya bushe tsabar wann taurin zuciyar da Allah ya bata wanda yasaka tuni ta iya hadiye duk wata damuwa da kukanta aciki. duk dama kowa cikinsu na jin dar dar da tunanon dawowar baban nasu gida ayau amma ita kam gaba gadi take tafiyatta da zucyarta daya.
sunyi tafiya na akalla mintina ashirin kafin suka kawo kofar madaidaicin rugarsu da gininsa yayi mugun jimawa sabida asali gidan gadone da wani uban gidan juma a harkan noma ya taba mallaka masa halak malak saboda tsbaar jajircewr sa a harkan kiwo da noma. duk da rugar ta jima saidai tsabar tsafta da tattali irinna taawure yasaka muhallin nasu yake da kyaun gani, nan suka tsaya a babban filin kofar gidan suna kan tattara buhuhunan da suka shanya wasu kayan abincinsu kmr tarugu, ganyen zobo kubewa, da gyada da wasu yan hatsi, inayah da kanwarta ayanah suka dukufa suna kan kwashewa taawure kuma tana zubawa acikin buhun tana dinkewa da allura da zaren buhu.
tsabar kawaici da kunya irinna bafulatanar usuli yasaka har iyanzu taawure bata budi baki tace uffan ma yayan nata akan abun da ya afku a fili ba, dake ma sunsaba da irin wann halintan ya saka koda wani abu yafaru inde batay musu magana ba suma sukeyin shiru saidai kawai kaga suna aikinsu da ladabi da kawaici.
gasu da hatsi,dabbobi da kaji amma diss din datti bazaka gani a tsakar gidan nasu ba koina an tandesa tass da tsintsiya yanayin yaran da uwarsu kadai kagani zakasan Allah ya zuba musu kwazo kunya da kuma sanyin tarbiya me tafe a jini.
bayan sun gama kwashe shauran abincin taawure da Ayanah ne agaba wajen kaiwa cikin ma'ajiya, ayayinda inaayah tay maza ta shiga ban daki, kai tsaye tayi tsarki ta taho tazauna akan dutsin dake kusa da madafi tahau alwala
Daga cikin daki kuwa suna shiga taawure ta cire mayafinta snn ta daga ido ta kalli yarta ayaanah dake rakube kan taburma ta rike saman kirjinta bata ko motsi, Tun haihuwar anayah suka fahimce cewa kamar tana famane da wani irin ciwo na raunin zuciya wanda baya tashi sai tana cikin halin tsoro ko tsananin baqin ciki da fargaba.
bayan mahaifyarsu arayuwarta babu abunda take kauna aranta kamar addarta inayah dan sun taso ne da wani irin kakkafar yarda da juna, shakuwa da kuma tausayin juna meyawa a tsakaninsu.
ganin yanayinta na laulayi yasa cikin sauri taawure ta durqusa kasa tajawo wani babban kwarya daga kasan kujera ta bude shi, wani tsaftacen jikon maganine aciki marmaza tasaka ludayi tahau deban ruwan maganin tana zubawa cikin karamin kwarya inda ko rabi baikai ba tamika mata da yaren babansu na buzanci tahau tursasa mata shi abaki kiyi bisimillahi Annayo am, karkiyi raunin zuciya maza kisha wnn zai saka kiji karfii kinji?..
adan ragwabe ayanah tamike zaune ta amshi kwaryan da ladabi tafara sha kenan saiga inayah ta shigo gabobinta duk a jike da ruwan alwala
suna hade ido kallo daya taawure tay mata kafin nan ta mike tsaye da tsoro a muryanta tana cewa
"ke kuma muje in rakaki hanya innari, kijeki ki buya a garin tudu harsai nazo na nemeki, bana son babanki ya dawo gidan nan da fushinki aransa ya zo yayi miki lahani ko ya tsinemiki kibi duniya in shiga uku..
kafin inayah ta amsa taga mahaifyarta har tajuya tahau daga katifarsu da akayishi da ciyawar tim tim hannunta na rawa rawa ta dauko mata jakar buhunta inda suke boye littafan karatunta na boko da islamiya da ta jima tana turata yi acan anguwar tudu inda suke kasuwanci ta saka yaranta karatu a boye batare da sanin mahaifinsu juma maharaozu ba.
jakar karatun ta fara mika mata danta boye shi acikin rigarta snn ta jawo kullin kayanta tahau nade matasu a tsuman zani tana gama kullawa ta dora mata shi akai, tsabar zafin zuciya 'bari 'bari kawai jikin inayah yake dan bataga wani dalilin da za'a boyeta ba,aganinta ai kare yar uwarta kawai tayi a fili, kawaici da darajar da take mugun bawa mahaifyrta yasaka batace komi ba dan babu abunda yake cimata tuwo a kwarya kamar irin mugun tsoron mahaifinsu da taga taawure takeyi agidan, wanda inda anbarta dashi da tuni takara dashi dan ji take ajininta kmr itadin mace me kmr maza.
turjewa tay ayayinda taawure ta wafco hannunta zata jawota waje, suna hade ido da dan taurin kai ta tsaya tanata kallon cikin idanunta batay mata yaren buzancin ba sai tay mata da fulatanci tana cewa 'ummah miyyasa kike tsoron abunda baba zai min dan na kare yar uwata ayaanah a fili ko dama so yake wancan katon banzan ya kasheta da sandanshi dan ya nuna musu baya kaunarmu? ummah inkina jin tsoronsa wata rana za'a kasheki ko akashe annayo a filin nan, kidubeta bata da kwarin gwiwa kuma wnn jikon naku da ake bata kinsan zai sakata bacci me nisa zai kashe mata zuciya bazatay karatu ko ibada ba umma inde ciwon zuciya ke damunta ai akwai malaman asbiti a tudu
rufe mata baki taawuree tay da sauri tun kafin wani yaji abubuwan datake ambata musmn ma batun asibiti da karatu
hankli tashe cikin tsawatar mata tace ya isa haka innarii yanxu ba lokacin magana bane, kituna dake kawai na dogara dan ranar da mahaifinku yasan nasakaku kuna karatu a tudu zai iya kasheni ko ya batar dani, innari kece mini, nasan zaki zama karfina anan gaba, nasan koda na mutu kece kawai zaki iya rike ayanah tsakanin ki da Allah koda bana duniya, in nabari yaxo ya tsine miki yau ni aka cuta duniya da lahira, kawai kije ki cigaba da karatunki a tudu, nayi miki alkwari bayan ya huce daga fushinsa, zanzo saida nono wata sati zan dawo dake gida, snn nayi alkwakri wnnan karon da kaina zanzo da anayah tudu itama ta cigaba da karatunta acan naji ance anyi mata nisa kudin natan ne bangama tarawa ba. tun kan innari ta amsa idanunta ya cika da ruwan hawaye ganin yadda jikin mahaifiyrsu yake bari sosai yanayinta cike da fargaba me ban tausayi da tsanani.
marmaza taawuren ta warware bakin zaninta ta ciro kudi da basu fi dari biyarba ta damka matasu duka a hannu tace" kirike wnn inkinje tudun kice ma goggo mei tuwo ina gaisheta, har da ma malaminku. ki kula da kanki Allah hokku barka am. inayah ta kasa cewa komi ganin yadda hankli da jikin mahairfyrsun gabaki daya yarikide dukkan hanklinta atashe yake sai leke leken waje take da tsoro daga ganinta kasan tana mugun tsorone kar ace juma ya dawo ya iskesu anan atare dqn bakaramin son yaranta takeyi ba.
hawaye kwalli daya ya sauka idon inaayah musmn da ta daga ido ta kalli mahaifayarsun snn ta kalli ayaanah dake kan kwance a tabarma ta kanannede kanta bata iya ko da motsi sabida jikon da aka bata tasha tuni ya sakata bacci..
tawuree na jan hannunta da kyar dai ta iya dauke idonta akan yar uwarta suka fice waje suna sauri sauri haka ta rakata har gaban babban rafi ta turata bisa hanyar tudu, ita kuma ta damke kayanta snn ta falfala da gudu tabi jejin, saida taga tay nisa snn ta dawo gida
taqumi tay ta zauna kurkusa da ayaanah dake kan bacci wasu maqudan hawaye na zuba mata ahnkli cikin tunanin safetyn yarta inayah, harcan saida aka kira sallan magrib snn ta tashe anayah sukayi marmaza sukayi sallolinsu suka ci abinci wanda dede lokacin ne aka taso daga wajen wasa...
fitila me kwai kawai ta kunna musu tay shiru tanajin ayanah tanata bitan karatun da addarta inayan ta koya mata game da sallah , tun suna zaune acikin dar dar din ganin shigowar juma gidan har dai suka hakura.
washe gari da asuban fari sukejin labarin cewa ashe baram baram aka tashi a filin wasa, sarkin buzaye dakansa yay jawabi akan tarbiya, yana mai kafa misali da rashin kunya da kuma tarbiya irinna inayah dahar ta karbi sanda a hannun namiji a filin wasa, dan haka tun anan juma maharozau yayi zuciya, sabida ance masa ya haifa musu y'ay'a mata marasa amfani ga cigaban kauyen snn kuma bai iya tarbiyatan dasu ba, acewar sarkin fulani in har innari ta sake musu tsaurin idon karban sanda a hannun namiji a fili zai saka matasa maza su giciye ta.
wayannn furucin yasaka juma tsananin fushi, bai dawo gidan sa ba ya wuce jeji dan tsabar zafin zuciya ma akan wata bishiyan mangwaro ya kwana
jin hakan bakaramin kara tsorota taawure yayi ba, dan tafi kowa sanin mugun zuciya da tsananin rashn son kaskanci irinna mijinta juma. dan da a raina mazantakarsa ko aci mutuncinsa a fili gara a maresa a fuska.
Juma Maharouzo ba asalin ɗan Dajin rini ba ne. Kakanninsa sun fito ne daga ƙauyen Maharouzo kusa da iyakar Tamesna wato yankin da ke tsakanin Nijar da Arewa maso Yammacin Najeriya.
tafiya suke da sauri sauri tareda wani irin rauni da kuma fargaba acikin zuciyoyinsu, koina yay shiru dan kusan kowa a kauyen anacan fili wajen gagarimin wasa, cikin sassarfa da sauri taawure tariko hannun karamar yarta ayanah gam tana janta ahnkli nan inda bakajin karar komi a hanyar face sanyin iskan yammaci da kukan tsutsaye tareda dirar sautin ajiyan zuciyar taawure datake saukeshi akai akai jin raunattecen ajiyar zuciyar da ayanah takeja wanda yagama narkewa cikin tsoro da matsanancin damuwa. daga ita har mahaifyarsun a dame suke da tunanin irin hukuncin da juma zai zo gida ya dauka akan su da kuma inaayah.
ita kuwa inayahr ko ajikinta daf dasu take tafiyarta zucyarta karau dan tun basu karasa barin filin wasan bama tabi ta shanye hawayenta idonta yabi ya bushe tsabar wann taurin zuciyar da Allah ya bata wanda yasaka tuni ta iya hadiye duk wata damuwa da kukanta aciki. duk dama kowa cikinsu na jin dar dar da tunanon dawowar baban nasu gida ayau amma ita kam gaba gadi take tafiyatta da zucyarta daya.
sunyi tafiya na akalla mintina ashirin kafin suka kawo kofar madaidaicin rugarsu da gininsa yayi mugun jimawa sabida asali gidan gadone da wani uban gidan juma a harkan noma ya taba mallaka masa halak malak saboda tsbaar jajircewr sa a harkan kiwo da noma. duk da rugar ta jima saidai tsabar tsafta da tattali irinna taawure yasaka muhallin nasu yake da kyaun gani, nan suka tsaya a babban filin kofar gidan suna kan tattara buhuhunan da suka shanya wasu kayan abincinsu kmr tarugu, ganyen zobo kubewa, da gyada da wasu yan hatsi, inayah da kanwarta ayanah suka dukufa suna kan kwashewa taawure kuma tana zubawa acikin buhun tana dinkewa da allura da zaren buhu.
tsabar kawaici da kunya irinna bafulatanar usuli yasaka har iyanzu taawure bata budi baki tace uffan ma yayan nata akan abun da ya afku a fili ba, dake ma sunsaba da irin wann halintan ya saka koda wani abu yafaru inde batay musu magana ba suma sukeyin shiru saidai kawai kaga suna aikinsu da ladabi da kawaici.
gasu da hatsi,dabbobi da kaji amma diss din datti bazaka gani a tsakar gidan nasu ba koina an tandesa tass da tsintsiya yanayin yaran da uwarsu kadai kagani zakasan Allah ya zuba musu kwazo kunya da kuma sanyin tarbiya me tafe a jini.
bayan sun gama kwashe shauran abincin taawure da Ayanah ne agaba wajen kaiwa cikin ma'ajiya, ayayinda inaayah tay maza ta shiga ban daki, kai tsaye tayi tsarki ta taho tazauna akan dutsin dake kusa da madafi tahau alwala
Daga cikin daki kuwa suna shiga taawure ta cire mayafinta snn ta daga ido ta kalli yarta ayaanah dake rakube kan taburma ta rike saman kirjinta bata ko motsi, Tun haihuwar anayah suka fahimce cewa kamar tana famane da wani irin ciwo na raunin zuciya wanda baya tashi sai tana cikin halin tsoro ko tsananin baqin ciki da fargaba.
bayan mahaifyarsu arayuwarta babu abunda take kauna aranta kamar addarta inayah dan sun taso ne da wani irin kakkafar yarda da juna, shakuwa da kuma tausayin juna meyawa a tsakaninsu.
ganin yanayinta na laulayi yasa cikin sauri taawure ta durqusa kasa tajawo wani babban kwarya daga kasan kujera ta bude shi, wani tsaftacen jikon maganine aciki marmaza tasaka ludayi tahau deban ruwan maganin tana zubawa cikin karamin kwarya inda ko rabi baikai ba tamika mata da yaren babansu na buzanci tahau tursasa mata shi abaki kiyi bisimillahi Annayo am, karkiyi raunin zuciya maza kisha wnn zai saka kiji karfii kinji?..
adan ragwabe ayanah tamike zaune ta amshi kwaryan da ladabi tafara sha kenan saiga inayah ta shigo gabobinta duk a jike da ruwan alwala
suna hade ido kallo daya taawure tay mata kafin nan ta mike tsaye da tsoro a muryanta tana cewa
"ke kuma muje in rakaki hanya innari, kijeki ki buya a garin tudu harsai nazo na nemeki, bana son babanki ya dawo gidan nan da fushinki aransa ya zo yayi miki lahani ko ya tsinemiki kibi duniya in shiga uku..
kafin inayah ta amsa taga mahaifyarta har tajuya tahau daga katifarsu da akayishi da ciyawar tim tim hannunta na rawa rawa ta dauko mata jakar buhunta inda suke boye littafan karatunta na boko da islamiya da ta jima tana turata yi acan anguwar tudu inda suke kasuwanci ta saka yaranta karatu a boye batare da sanin mahaifinsu juma maharaozu ba.
jakar karatun ta fara mika mata danta boye shi acikin rigarta snn ta jawo kullin kayanta tahau nade matasu a tsuman zani tana gama kullawa ta dora mata shi akai, tsabar zafin zuciya 'bari 'bari kawai jikin inayah yake dan bataga wani dalilin da za'a boyeta ba,aganinta ai kare yar uwarta kawai tayi a fili, kawaici da darajar da take mugun bawa mahaifyrta yasaka batace komi ba dan babu abunda yake cimata tuwo a kwarya kamar irin mugun tsoron mahaifinsu da taga taawure takeyi agidan, wanda inda anbarta dashi da tuni takara dashi dan ji take ajininta kmr itadin mace me kmr maza.
turjewa tay ayayinda taawure ta wafco hannunta zata jawota waje, suna hade ido da dan taurin kai ta tsaya tanata kallon cikin idanunta batay mata yaren buzancin ba sai tay mata da fulatanci tana cewa 'ummah miyyasa kike tsoron abunda baba zai min dan na kare yar uwata ayaanah a fili ko dama so yake wancan katon banzan ya kasheta da sandanshi dan ya nuna musu baya kaunarmu? ummah inkina jin tsoronsa wata rana za'a kasheki ko akashe annayo a filin nan, kidubeta bata da kwarin gwiwa kuma wnn jikon naku da ake bata kinsan zai sakata bacci me nisa zai kashe mata zuciya bazatay karatu ko ibada ba umma inde ciwon zuciya ke damunta ai akwai malaman asbiti a tudu
rufe mata baki taawuree tay da sauri tun kafin wani yaji abubuwan datake ambata musmn ma batun asibiti da karatu
hankli tashe cikin tsawatar mata tace ya isa haka innarii yanxu ba lokacin magana bane, kituna dake kawai na dogara dan ranar da mahaifinku yasan nasakaku kuna karatu a tudu zai iya kasheni ko ya batar dani, innari kece mini, nasan zaki zama karfina anan gaba, nasan koda na mutu kece kawai zaki iya rike ayanah tsakanin ki da Allah koda bana duniya, in nabari yaxo ya tsine miki yau ni aka cuta duniya da lahira, kawai kije ki cigaba da karatunki a tudu, nayi miki alkwari bayan ya huce daga fushinsa, zanzo saida nono wata sati zan dawo dake gida, snn nayi alkwakri wnnan karon da kaina zanzo da anayah tudu itama ta cigaba da karatunta acan naji ance anyi mata nisa kudin natan ne bangama tarawa ba. tun kan innari ta amsa idanunta ya cika da ruwan hawaye ganin yadda jikin mahaifiyrsu yake bari sosai yanayinta cike da fargaba me ban tausayi da tsanani.
marmaza taawuren ta warware bakin zaninta ta ciro kudi da basu fi dari biyarba ta damka matasu duka a hannu tace" kirike wnn inkinje tudun kice ma goggo mei tuwo ina gaisheta, har da ma malaminku. ki kula da kanki Allah hokku barka am. inayah ta kasa cewa komi ganin yadda hankli da jikin mahairfyrsun gabaki daya yarikide dukkan hanklinta atashe yake sai leke leken waje take da tsoro daga ganinta kasan tana mugun tsorone kar ace juma ya dawo ya iskesu anan atare dqn bakaramin son yaranta takeyi ba.
hawaye kwalli daya ya sauka idon inaayah musmn da ta daga ido ta kalli mahaifayarsun snn ta kalli ayaanah dake kan kwance a tabarma ta kanannede kanta bata iya ko da motsi sabida jikon da aka bata tasha tuni ya sakata bacci..
tawuree na jan hannunta da kyar dai ta iya dauke idonta akan yar uwarta suka fice waje suna sauri sauri haka ta rakata har gaban babban rafi ta turata bisa hanyar tudu, ita kuma ta damke kayanta snn ta falfala da gudu tabi jejin, saida taga tay nisa snn ta dawo gida
taqumi tay ta zauna kurkusa da ayaanah dake kan bacci wasu maqudan hawaye na zuba mata ahnkli cikin tunanin safetyn yarta inayah, harcan saida aka kira sallan magrib snn ta tashe anayah sukayi marmaza sukayi sallolinsu suka ci abinci wanda dede lokacin ne aka taso daga wajen wasa...
fitila me kwai kawai ta kunna musu tay shiru tanajin ayanah tanata bitan karatun da addarta inayan ta koya mata game da sallah , tun suna zaune acikin dar dar din ganin shigowar juma gidan har dai suka hakura.
washe gari da asuban fari sukejin labarin cewa ashe baram baram aka tashi a filin wasa, sarkin buzaye dakansa yay jawabi akan tarbiya, yana mai kafa misali da rashin kunya da kuma tarbiya irinna inayah dahar ta karbi sanda a hannun namiji a filin wasa, dan haka tun anan juma maharozau yayi zuciya, sabida ance masa ya haifa musu y'ay'a mata marasa amfani ga cigaban kauyen snn kuma bai iya tarbiyatan dasu ba, acewar sarkin fulani in har innari ta sake musu tsaurin idon karban sanda a hannun namiji a fili zai saka matasa maza su giciye ta.
wayannn furucin yasaka juma tsananin fushi, bai dawo gidan sa ba ya wuce jeji dan tsabar zafin zuciya ma akan wata bishiyan mangwaro ya kwana
jin hakan bakaramin kara tsorota taawure yayi ba, dan tafi kowa sanin mugun zuciya da tsananin rashn son kaskanci irinna mijinta juma. dan da a raina mazantakarsa ko aci mutuncinsa a fili gara a maresa a fuska.
Juma Maharouzo ba asalin ɗan Dajin rini ba ne. Kakanninsa sun fito ne daga ƙauyen Maharouzo kusa da iyakar Tamesna wato yankin da ke tsakanin Nijar da Arewa maso Yammacin Najeriya.