← Book details Akidata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 127

Sashe 76

Akidata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mummy tace " Haba Amal, kiyi haƙuri dan Allah, ai abun be tsawwala ba Autana, karaya kika samu a hannu se kwalba daya fasa miki goshi, Ai Alhaji Haruna yayi mana mutunci, shiya kawoki Asibitin nan"

Kawai Amal ta dinga kuka, ji tayi kamar ta shaƙe mahaifiyarta jin maganar da take, ya cuceta ya kassara rayuwarta, ya raba ta da mutuncinta, kuma ya kawota Asibiti yace hatsari tayi, ji tayi kamar zuciyarta ta tsaga ƙirjinta ta fito saboda azabar baƙinciki da takaici, tama rasa me zata yi, kawai ta fasa ihu ta fizge ruwan dake jikinta tayi jifa dashi, ta dinga wani uban ihu, da ƙyar aka kira likitoci, aka daddanneta akayi mata allurar bacci.

Mummy ta kalli likitan cike da damuwa tace "Doctor, wai dan Allah meyasa meta ne? Naga kamar ta haukace"

Likitan yace "A'a ba haukacewa tayi ba, stress ne da damuwa suka ɗan dameta amma insha Allah komai zezo da sauƙi, zamu sake mata hoton hannun, idan hali yayi a goben ma insha Allah zamu iyayi mata aikin, tunda Alhaji Haruna ya gama biyan komai, dama anan yake da family file "

Hajiya Halima tace
"shikenan, mungode nidai Alhamdilillah tunda ba wani abunne ya sameta ba"

Bayan sallar isha'i Yusuf ya shigo, ya tarar da Widad a kwance ta kunna fitila, tana ta saƙa maficinta daga nan inda take kwance, yai sallama ta amsa, yana zuwa ya kwanta a kanta.

Cikin Shagwaɓa tace "wayyo Allah na, Yuzarsef meye haka? Kana fa da nauyi seka danne min kan Babyna"

Yusuf yace "wainine nake da nauyi, ina wani Baby yake anan?"

Tace 'ba a nan mana" tai maganar tana nuna masa cikinta.

Yusuf yasa hannu ya danna cikin nata yace "Malama bakomai anan hanji, waye yace miki a nan É—a yake zama"

"wayyo Allah na, Yoseef yau cinzali kake ji, dan Allah ka dena danna min cikina, kar kasa in haifi ɗa da lotsatsen ƙeya mana"

Yace "Madam wannan cikin naki bakomai a ciki, inma akwai be zama mutum ba, amma duk kin ishi mutane, ke wannan idan cikin ya samu na shigesu, da langwai da Shagwaɓa"

Widad ta tura baki tace "Yuzarsef, da nace zan sakawa jaririna sunanka, amma na fasa tunda kana adawa da baybn nan nawa"

"Au da bazaki saka sunan Daddy ba, se sunana?"

"Eh mana sunanka zan samasa mana"

Yusuf yace "salon Daddy yace kinfi son mijinki akansa"

Tace "to ai dai É—ana ne naga, ko É—an Daddyn ne?"

"Iyee, ba kara ba kunya Baby, Allah ya shiryeki wallahi za'aga uwa mara kunya gaskiya"

Tace "eh naji É—in, ni É—agani karka samin É—a kuka"

Yusuf yace "iko se Allah, wai yanzu ke kin haƙiƙance ɗane a cikinki? Kwana nawa kika ƙara baki period ba?, ina shekaranjiya kika cemin mararki na ciwo baki period ɗinba?"

"Ai bezo ba tukuna, kwana biyar ya ƙara fa, Insha Allah ina da ciki"

Yusuf yace "mara kunya kawai" yai maganar tare da danna gefen mararta É—aya, wani irin ihu tayi haÉ—i da zillo, se hawaye, Yusuf ya bita da kallo yana nazarinta.

Cikin hawaye tace "Yusuf meye haka? Da zafi fa wallahi"

Yusuf yace "yi haƙuri, am sorry kinji babyna, yi haƙuri bazan sake ba insha Allah, abu nake son ji"

"Ni ƙyaleni, kawai se cin zalina kake, kuma bazan kwana da kai ba a katifata ba, tunda haka ka koma"

"Ke kin isa ki koreni daga kan katifar nan, ina nan tare zamu kwana semun samo Babyn Baby"

"Ni na samu Babyna in gaya maka, kuma sena rama abunda kayi min, ni wanka zanje inyi"

Yusuf yace "ina nan ina jiranki, kije kiyi wankan kizo kimin tausa inyi bacci"

"bazan ba" tai maganar tana hararasa, sannan ta miƙe ta fice daga ɗakin tana murmushi.

Haka suka kwana tare abunsu, cike da soyayya da ƙaunar juna, tana sake jin Yusuf a zuciyarta, bata jin zata iya rabuwa dashi.

Saleh kam iya azaba ya shata, su ciko bokiti su danna kansa a ciki, seya suma, banda wutar lantarki da suka dinga jona masa, ga ba Abinci babu ruwan sha, ya galabaita fiye da tunani, banda duka da suke masa da katakwaye, sun masa laga laga gaba ɗaya Saleh ya zama abun tausayi, ya galabaita ya lalace saboda azaba, suyita buga masa itace a ciki, kai da ƙirjinsa, ya dinga fidda jini ta baki da hancinsa, gaba ɗaya ya suma baya hayyacinsa a haka se da aka kwana uku, sannan suka yi waya suka sanar da Bukar, yace musu yana nan tafe zezo gidan da ake ajiye da Saleh yaji idan yayi laushi zuwa yanzu.

"Alhaji Bukar, kana sane da cewar mahaifinmu yazo har gidanmu ya saka hannu ya mareni?"

"Eh, naji na samu labarin zuwansa, amma ni sam ban san da zancen ya dakeki ba"

Ramlah tace "to ya saka hannu ya dakeni, bayan tsawon shekaru be san cina shana ko suturata ba, an gayamin cewar hatsabibine, dan haka sonake in nuna masa ya haifi wadda ta fishi hatsabiban ci"

Alhaji Bukar yace "Anya zakifi mahaifinku hatsabibanci kuwa? Amma me kike so ayi masa?"

"Sonake a nemo shi duk inda yake, a sauke masa hannun da ya mareni dashi"

"Amma fa naga mahaifinkine, idan kikayi haka baki kyauta ba"

"Naga dai shima ba mutumin kirki bane, koda bama tare dashi, labarin aika aikar dayayi duk na sani, dan haka rama cuta ga macuci ibadane, zan kawo ƙarshen iya shegensa, a sauke masa hannu nake buƙata"

Alhaju Bukar yace "kin samu yarinya, kije kin kwantar da hankalinki, za'ayi abunda ya dace, yadda kike so haka za'ayi ai".

Koda Amal ta sake farkawa ta ganta a Asibiti ta tabattar ba mafarki take ba, ta sake fashewa da kuka, ta tuna yadda suka yi da Alhaji Haruna, shikenan Ya kassara mata rayuwa, ya cuce ta, ya gama da ita, tinƙahon kowace mace shine budurcinta amma a banza wani tsohon najadu dabba ya kassara mata rayuwa, ya tarwatsa mata rayuwa ya cuceta, wasu irin zafafan Hawaye suka shiga yi mata sintiri a fuskar ta, tana tunanin me zata yiwa Alhaji Haruna ta huce, me zata yi masa wanda zesa ta huce, ita gaba ɗaya Yusuf ta tanadar wa kanta, saboda babu komai a zuciyar ta inba shiba, dole tayi wani abu wanda zaya rama abunda Alhaji Haruna yayi mata.

Ramlah ta kalleta tace "Amal wai wannan wani irin kukane haka? Ki saurarawa kanki mana, Allah ya taƙaita miki wahala baki mutu ba, kuma hannun be cire gaba ɗaya ba, amma se kuka kikeyi, ki kwantar da hankalinki dan Allah kiyi haƙuri.

Mummy da ta idar da salla tace " tayani gaya mata dai Ko zataji, tunda abun nan ya faru take kuka, na rasa kukan ubanme take haka? Ni kin kai masa takadda makuwa kafin abun ya faru?"

Banza tayi mata, ta ɗauke kanta ta cigaba da kukanta, Alhaji Haruna ne yai sallama, ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, hannunsa ɗauke da manyan ledoji, ya shigo suka gaisa da Mummy, yace " Ya jikin Auta kuwa? "

Mummy tace "Jiki da sauƙi, sedai se kuka take, taƙi yin shiru, kuma ga abun be tsawwala da yawa ba, karayace kuma ance yau za'a mata ɗori"

Alhaji Haruna ya zauna a gefen gadon yace "Auta ya jikin naki?"

Lallai mutumin nan ya cika gardin ɗan iska, ya mata wannan aika aika, sannan yazo wai yazo dubata, shiru tayi taƙi magana.

Hajiya Halima tace "Amal ba magana ake miki ba kika yi shiru? '

Alhaji Haruna yace "Halima ku É—an bamu guri dan Allah, zan mata magana"

Ba musu suka fice, sedai kallo Ramlah ta dinga binsa dashi na tuhuma.

Yace "Haba Baby, daga abu ya faru shikenan seki ɗaga hankalinki, haba Baby Amal, kiyi haƙuri kinji ai is not that painful, zaki warke kuma karayar nan is just an accident, zaki warke insha Allah, amma kidena kukan haka kinji"

Ji tayi kamar ya kunna wuta a zuciyarta, tabbas ds da makami seta kasheshi kome za'ayi mata ayi, ga mahaifiyarta sam batayi hankalin gane abunda ya faru ba.

Ganin tayi shiru, yasa ya janyo ya jikinsa yana faÉ—in "you make my day jiya, na daÉ—e ban samu mace kamarki ba, ki kwantar da hankalinki mucigaba da rayuwar mu babu wanda ze gane kinji"

Amal tai shiru, taƙi buɗe ido zuciyarta ta dinga tafasa, ganin tayi shiru batayi magana ba, yasa seda yayi shagalinsa sannan ya dunƙulo bandir ɗin kuɗi ya zube mata.

Seda yaje bakin ƙofa ze fita tace "idan ba'a gaɓa gwada maka kaidin mace ba, ka fara ƙirgawa daga yau zaka fara gani, wallahi Haruna sena maka abunda bazaka manta ba har abada, sena maka Baƙin tabon da yafi wanda kayi min, wallahi sena ƙulla maka makirin da duniya basu isa su kwance maka ba, zaka gane baka da wayo daga maina bazaka sake gwada akuyanci akan wata 'ya ba, ka saurareni....'

.
LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel É—ina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/21/21, 7:45 AM - Buhainat: LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel É—ina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

112_113

Alhaji Haruna yai murmushi irin na tsofaffin 'yan duniya sannan yace
Chapter 76 · 0% Book details