← Book details Akidata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 127

Sashe 3

Akidata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saleh yace  "ƙwarai na san wacece ita, yadda ta gaya maka hakane bata yafiya ga wanda yayi mata ƙarya ko yaci amanarta, duk yadda suke da shi kuwa, amma ai kai akwai alaƙa me matuƙar ƙarfi a tsakaninku, zata iya ɗaga maka ƙafa kuma kamata yayi ace kai da kanka ka gaya mata, karka bari taji a waje, idan kuwa ka kuskura ta samu labari a gurin wani akwai matsala, dan bata ƙi ka tafi prison ba kaima, tace an haɗa baki da kai za'a cuce ta, abun da nake ganin dai yafi shine ka sanar da ita kawai, hakan zefi "

"tabbas nasan bata yafiya ga wanda yaci amanarta, nikam Saleh me kayi mata wanda yasa ta kasa duba alkhairin ka se laifukanka? "

Saleh yayi murmushi yace " labari ne me tsawo Yusuf, kuma gaya maka labarin tamkar ƙara wani laifin ne akan laifi, amma ka bari idan tayi niyya zata iya gaya maka komai, nidai shawarata da kai, tun kuna nan ka gayamata waye kai"

Yusuf yaja ajiyar zuciya yace " Inajin tsoro Saleh, harga Allah ni fa ina son Widad ne tsakani da Allah, yanzu idan na gaya mata zata iya ƙina, a yanzu mu tana ƙasa tana dabo ne, dan itafa bata yadda akwai so ba, dan haka bani da tabbacin tana sona, kuma inzo in gaya mata wannan magana, abun ze lalace gaba ɗaya ne fa"

Saleh yace "haba namijin duniya, ai kai kana da jarumrtar da ka cancanci a sara maka, haka nan duka butulcin me butulci dole ya sarawa namijin ƙoƙarin da kayi akan Widad, ni kaina na fuskanci sonta kake, amma dole zata ɗaga maka ƙafa dan baka cancanci ta wulaƙanta ka ba, be cancanci ta manta da alkhairin da kayi maka ba, dukda yarinyar wata irin muguwar bahaguwa ce, amma kayi ƙoƙari kafin ku bar garin nan tasan abunda ake ciki "

Yusuf ya dafe kai yace " Subhanallah, ban san ta ina zan fara ba Saleh, ina tsoron abunda ze biyo baya, ni kome zata yi baze dameni ba, ni fargaba ta karta rabu dani ko tayi min wata mummunar fahimta "

" Yusuf kenan, da alama wannan ne karonka na farko na shiga soyayya ko?"

Yusuf ya girgiza kai yace " Na taɓa soyayya Saleh, har na sawa kaina bazan sake soyayya ba, katsam Widad ta shigo cikin rayuwata ba tare da na warke daga wancan ciwon dake zuciyata ba, kuma har nake jin cewa a yanzu inawa Widad son da banyi wa waccan yarinyar ba"

Saleh yace "lallai kana cikin Jarrabawa Yusuf, ina maka fatan Alkhairi tare da fatan Allah ya fitar da kai"

Sallamar Widad ce a É—akin ta katsesu, suka amsa mata gaba É—aya, fuskarta duk bushashiyar gasara, kanta babu É—ankwali goshinta duk gumi.

Ta kalli Saleh ha haÉ—e rai tace "Excuse us please"

Saleh yace "to" ya tashi ya fita ya bar É—akin.

Ta kalli Yusuf tace "ka zauna kana ta surutu, baka san lokacin salla yayi bane, har an fara aikowa ana tuna maka, kaje kaja salla"

Yusuf yace  "aini yanzu gaba ɗaya kunyar mutanen nake ji".

Widad tace "me kayi musu na kunya?"

Yusuf yace "tunda kika rungume ni a gabansu, indai suka ganni se inga suna wani sunkuyar da kai"

Ɗan guntun tsaki Widad tayi tace "to dana rungumeka a gaban su is it an abomination? Saɓo nayi kome?"

"to ai su basu saba ganin irin haka ba, is against their norms"

Widad tace "to su suka sani, ni wanka zanje inyi, kaje kayi sallar"

Yusuf yace "to bari inje in dawo in rama dukan da kika yi min da Asuba"

"ina nan ina jiranka kuwa, kasan dai na fika ƙarfi yanzu, kai sauro ya zuƙe maka ƙarfi".

"dole kice haka mana, tunda na baki jinina, dole kiyi ƙarfi ai"

Ta kalle shi tace "ji wata magana, jinin naka ma da bashi da kyau, duk ba wasu sinadarai a cikinsa, shine duk ka dameni da ka bani jini, to zan biya ka abunka"

Yusuf yayi dariya yace "kamar gaske"
Yai waje, yana fita ta kintsa ta É—au bokiti ta tafi taje tayi wanka.

Tana zaune tana shafa man zaitun a jikinta Yusuf ya dawo, ta bawa ƙofa baya, farar fatarta se ƙyalli take da ɗaukar ido, ga baƙin gashinta ya kwanta sosai a bayan ta, ƙasansa ya jiƙe da ruwan wanka, ba taji dawowar Yusuf ba se jinsa tayi zaune a kusa da ita, numfashinsa na sauka a jikinta.

Da sauri ta É—ago ta kalle shi tace "meye haka? Ya zaka zo ba ko sallama, ka zauna kana shinshinani"

Seda tasa Yusuf yayi dariyar dabe shirya yinta ba, yace "niba shinshinaki nake ba, se kace wani kare"

"to baga numfashinka nan inaji a jikina ba"

Beyi magana ba, ya kalli hannun ta data tsiyayo zaitun, ya zura nasa hannun akan nata, zaitun É—in wani duk ya zube, ya shiga shafa mata a jikinta.

Ji tayi tsaigar jikinta na tashi, É—an yamutse fuska tayi tace "Yoseef bana so, ka bari in shafa da kaina"

"Ni kuma ina so, ki bari in shafa miki"

Tsaki tayi ta ɗan ɗaga murya tace "nace maka bana so" tai maganar tana ƙoƙarin miƙewa, Amma Yusuf ya riƙeta ya hanata tashi, a hankali yace "yi haƙuri Widad, magana nake so muyi" yai maganar yana sauke numfashi.

Littafin kuÉ—i ne, kuyi magana ta wannan lambar domin siyan littafin
Nagode
07063065680
11/14/21, 6:09 PM - Ummee Musa: 48_49

Littafin kuɗi ne pay before you read please 🙏 🙏 🙏

HaÉ—e rai tayi tace "dan za muyi magana shine zaka dinga yimin wannan abun haka, ni bana so gaskiya karka sake yimin"

Maimakon yayi magana Shiru yayi ya sake ƙanƙameta sosai a jikinsa, ya kwantar da kansa a jikinta, ita kuwa mutsu mustu kawai take, so take taga ta ƙwace daga jikinsa, amma abu ya gagara, ya riƙeta sosai ga ƙarfinsu ba ɗaya ba.

A hasale Widad tace "Wai dan Allah Yoseef meye hakane?, ka cikani towel É—in jikina ze kwance fa? Nace maka bana so ka cikani dan Allah, wallahi gaba É—aya ka canza hali, kwanan nan sekai tayi min wasu abubuwa wanda bana so, kuma kana sane"

A hankali ya cika ta, ya kwanta akan katifar yayi shiru tare da lumshe idonsa.

Se kuma ta juya tana kallonsa tace "meye kuma?" ba tare da ya buÉ—e idonsa ba ya girgiza mata kai.

"to me zaka gayamin?"

"bakomai" ya bata amsa

"wani irin bakomai bayan kace magana zamuyi?"

Gabansa ne ya faɗi, yaga be kyautu yayi mata wannan zancen a wannan gaɓar ba data ɗau zafi, dan haka ya buɗe idonsa ya ɗan tsare ta da ido yace dama ba wata magana bace, ina son in sake gayamiki Ina sonki Widad "

Ha É—e rai tayi tace " kaga tasarmin daga kan katifa ta, tunda ba zaka dena wannan shirmen ba, kuma daga yau in ka san wannan shiritar zaka gayamin, karka sake cewa zakayi magana dani na gaya maka, dan bazan saurareka ba"

Yusuf yace "Maganar tawace shiririta? Queen ba shirita bace i mean it, kalmar so ba abun wasa bane ko imagination ba, please my Queen ki yarda ina sonki mana"

Banza tayi masa, ta ɗakko kayanta tana ƙoƙarin sakawa, ya juya mata baya don ta sa kayanta.
tayi ƙasa da muryarta cikin ƙunƙuni tace 'kaji da shi dai, kai ta mun wasu abubuwa amma idan zansa kaya seka wani juya, wai kai gaka na Allah, inma baka juya ba niba abunda ya dameni sa ka yana zanyi'

Bece mata komai ba se dai murmushi da yayi, se data gama sa kayan, ta yunƙura zata miƙe ya sake riƙeta, a fusace tayi niyyar yi masa rashin mutunci, amma ya rungumota ta kasa cewa komai jin ya haɗe bakin su.

Gaba ɗaya Yusuf yafi ƙarfinta, ta kasa gane kansa kwata kwata, kwanan nan se wasu ɗabi'u yake mata wanda bata gane kansu, tana ji tana gani seda yayi me isarsa sannan ya cika ta, ba zata iya ƙwace kanta ba.

Yana cikata bata kuma kallonsa ba, ba tace komai ba rai a matuƙar ɓace tayi waje, kallo ɗaya zaka yiwa fuskar ta kasan a fusace take, ta fita tsakar gida rana ta take, kowa yana ɗaki ta fita ta samu guri a ƙasan bishiya tayi zamanta.

Hakanan Yusuf ya dinga jin be kyauta ba abunda yayi, amma ya zeyi shima bayin kansa bane, mutum ne shima kuma me cikakkiyar lafiya, shi kansa yanzu ya fara É—ar É—ar na zama da Widad a guri É—aya, komai ze iya faruwa.

Barrister Khalil kam tunda yakoma gida yake tunanin hirar da sukayi da Nurat game da mahaifinta, tabbas mahaifin Nurat ba karamin hatsabibi bane ,ze iya aikata komai muddin burinsa ze cika ,amma yayi mamakin yadda Nurat tace masa da saka hannunsa a sace Daula da akayi,abun da mamaki matuka, nan ya shiga nazarin ta ina yakamata yayi wani abu? Amm muddin ya kuskura Alhaji Musa yasan yana wani yunkuri,ko kuma ya gane ya san wani abu akan abunda yake aiktawa,to tabbas ba abunda ze hanashi daukar mataki akansa,dan bashi da Imani sam.

Barrister Hafiz ma tunda ya koma gida yake tunanin batun da aka bijiro masa da shi akan dukiyar Daula,tabbas kudi abun sone,amma meze biyo baya idan suka amince akayi wann aika aika? Idan sukayi aikin nan tabbas zasu samu kudi,amma hatsarin dake cikin hakan shine abun dubawa, watakila idan shi nya amince ba lallai sauran lawyoyin su yadd ba,amm tabbas yana son kudi shima.

Ya yanke shawarar zefara tuntubarsu daya bayan daya yaji opinion din sauran akan lamarin abunda suka yanke shikenan.
  Ya tashi ya dau mukullin motarsa ya fice.

Anwar kuwa gaba daya yayi baki,ya rame saboda zaman gurin nan babu sauki sam, ga sauro ga rahsin kula, ga azabar wahala da ake gana musu akan lallai se sun fadi inda Daula yake, amsar sa dai dayace be san inda yake ba.

Yana zaune a inda suke ajiye yayi shiru yana tunani,s hi babban abunda yake damunsa shine waye ya sace Daula? Wanda ya sace shin yana iya kula dashi?maganinsa ma ko ana kula dashi a bashi oho? Yayi zurfi a duniyar tunani yaji an kira sunansa, a hankali ya daga kai, dan sandan yace

“ka taso kana da bako”
Chapter 3 · 0% Book details