← Book details Akidata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 127

Sashe 56

Akidata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gwaggo ta fuskanci kamar sun kuma samun saɓani tsakanin ta da Yusuf, amma bata son taita mata shisshigi, dan haka ta ƙyaleta, dan gaba ɗaya walwalarta ta ragu, kusan ko san magana ma ba tayi, ko kayi maganar ma bata san abunda kake faɗa ba tana tunani.
Dan mamaki yakasa barin zuciyarta wai Yusuf ne yake gudun ta haihu dashi, ita iya tunaninta babu wani dalili daze sa yayi hakan sedai son zuciyarsa kawai.

Da daddare ya dawo tana kallonsa, bata kulashi ba dan ko sallamarsa ƙin Amsawa tayi, ta barmasa ɗakin gaba ɗaya ta koma tsakar gida inda aka baje tabarma ana hira.

Haka ya fito kamar maraya, yayi alwala ya tafi salla, ya dawo shiru shiru taƙi komawa ɗakin, har kusan ƙarfe goma na dare, ya fito yazo inda take dayake duk hirar nan ma da ake yi, ita ba wani magana take ba, sedai in anyi abun dariya ta ɗanyi murmushi, sam hankalinta baya kan hirar ta fitone kawai dan karma Yusuf yayi mata magana.

Tana jikin bango, babu haske a inda take zaune, yazo ya zauna a kusa da ita yayi ƙasa da muryarsa yace "My love, dan Allah kizo muje ɗaki mana, kin barni kamar maraya kin dawo nan kin zauna, dan Allah kiyi haƙuri kizo mu koma mana, kina da miji amma kizo zaman hira"

"Yoseef bana son sake jin kalamn nan naka na yaudara, wanda naji a bayama sun isa Allah ya amfana, kaje da can ai ba tare muke hirar ba"

"Widad kalaman nawane na yaudara?"

"bakaji bane in sake maimaitawa, kalaman yaudara da kake yaudara ta dasu na fara amince maka zaka butulcemin mana"

"Yi haƙuri dan Allah karki ɗaga murya mana, zomu je ɗaki muyi magana"

Widad tace "bazani ba, nace bazanje ba, ka ƙyaleni"

Yusuf ya sake marairaicewa yace "nasan haushina kikeji, a ƙule kike dani amma please and please am very sorry, kiyi haƙuri mu koma ɗaki"

Ƙarshe ma juya masa baya tayi, alamar idan ya gama ze iya tashi yayi gaba.
Abun duniya ya ishi Yusuf, haka ya tashi ya tafi ɗaki, jiki a sanyaye, ya dinga tunanin dama tun farko data fara zancen cikin, ba haka ya ɓullo mata ba, gashi ta birkice gaba ɗaya, tama ƙi saurararsa.

SE kusan sha É—aya da rabi, dabar hirara nan ta watse, kowa ya tashi ya tafi makwancinsa, Widad ma É—akinsu ta nufa, sedai tana zuwa ta tarar da Yusuf a zaune be kwanta ba.
Tazo ta tsallake shi ta shige abunta, tana ƙoƙarin canza kaya, Yusuf yace "Widad, akwai buƙatar ko sau ɗaya ki bani dama, in kare kaina yana da kyau kiji ta bakina kafin yanke hukunci"

"baka da ta cewa fa, ai labarin zuciya a tambayi fuska babu wani abu da zaka gayamin, fuskarka ta bayyana abunda ke cikin zuciyar ka, dan haka ka ƙyaleni kawai, bana san sake jin komai kawai ka rabu dani, kuma ɗane idan Allah ya bani kace ba naka bans, ni ima so kuma bana buƙatar taimakonka a rainon ɗana, da can baka san cikin ze shiga ba kake mu'amala dani, ko in an tashi bani ciki shawara za'ayi da kai? "

" Nace dai kiyi haƙuri please, zan gayamiki dalilina dan Allah, amma kiyi haƙuri ki dena wannan fushin"

"Se kuma kayi, kanka ake ji"

"Widad, Widad magana fa nake miki"

"kaga idan ka takurani wallahi zan fita ina kwana a waje, ka ƙyaleni"

Ya dinga binta da kallo harta kwanta abunta taja bargo ta rufe kanta.

Amal ce zaune tayi tagumi jugum, kamar an musu mutuwa tace "Mummy, yanzu idan kinje gurinsu Alhaji Haruna me zaki ce musu? Kuma ta ina za'a fara binciken inda ya tafi?"

Hajiya Halima tace " sanin gaibu se Allah Amal, zanje dai inga yadda zamuyi dasu ne kawai"

Ramlah tace "to yanzu idan aka ganshi Meza kiyi masa?"

Hajiya Halima tace "ubansa zanci da farko, sannan ince masa duk abunda aka gayamasa ƙaryane"

"Mummy, Yaya Anwar fa isa almost 30 years, he is not kid, tayaya zaki gayamasa haka ya yadda, idan kuma ba gaya masa akayi ba wani abu ya gani fa?"

"Waike Amal bakinki baya faÉ—ar alheri se sharrine, to rufen baki tunda bazaki faÉ—i abun alkhairi ba"

Ramlah tace "bahaka bane Mummy, yanzu idan kika je neman mafita gurinsu Alhaji Haruna, kina ganin suna ganin Asirinsu ze tonu idan suka ganshi zasu ƙyaleshi hakane? Karfa ki manta har yanzu babu wanda yake sa tabbas na Bala yana raye a kurkuku, saboda sun tsoron Asirinsu ya tonu ana cewa sunsa an kashe shi, kuma sun cigaba da aiki da Saleb, ba tare da yasan sun kashe ɗan uwansa ba, those people are evil, they are very dangerous fa"

"Na shiga uku ni Halima, yanzu ya zanyi wallahi duk cikinku ina sonku, babu wanda zan iya zuba ido inga ya cutu in haƙura, duk ni na haifeku ina ƙaunar ku"

Amal tace "mun sani Mummy, kiyi haƙuri ki kwantar da hankalinki a nemo mafita mana"

Isa megadi na zaune a bakin gate, riƙe da 'yar radionsa, yana ta fama ya kama stationsa amma se wani ɓurari take saboda rashin batur, ya dire radion yana zage zage da Tsinewa Hajiya Halima, ganin kuɗin batirin radio ma ya ga gareshi.

Jiya yi ana bugun gate ɗin da ƙarfi kamar za' a karya ƙofar, shi dai beji horn ɗin mota ba, dan baka ya miƙe a fusace yana bala'i yana masife yana cewa "wani jakin me wannan yake mana wannan bugun se kace gidan ubansa, kokuma wani ɗan fashi, mutum se kace gidan uabansa, ko yaya kuka buga anaji, muma za'a buɗe amma komai se mutane sun yi hauka, aikin banza iyayen maula kawai"

Haka ya ci gaba da surfa masifa, sannan ya buɗe gate ɗin, wani mutum ya gani a tsaye, da wani koɗaɗɗen yadinsa shara shara, hularsa ma tayi baƙi ƙirin saboda dauɗa wani zaburarre dashi kamar korarre, Isa ya ƙare masa kallo yace "mutane ba dai Jaraba ba, baka san an sace me gidan ba, dama shine yake baku, wannan mastiyaciyar me hannun jarirar ba'a ɓanɓararta jeka Allah ya baka haƙuri, an dema sadaka a gidan nan"

Mutumin yace "ba Sadaka nazo nema ba, gurin Halima nazo"

"au gatsal kake faɗar sunantaa? Allah yasa ta jika, tukuna ma a danginta ban taɓa ganin mutum kamarka yazo ba, daga ina ko kwatance akayi maka?"

"ba kwatance akayimin ba, kaje kace mata tayi baƙo, ita tasan waye"

Isa yace "shikenan, shigo daga ciki seka zauna akan benci, amma in turoka akayi a baka aikima, babu guri dan muma ba biyanmu take ba, mace ce hannu kamar kuturwa, tasan a bata amma bata san ta bayar ba"

Haka Isa ya cigaba da soki burutsunsa, yaje ya sanar da Hajiya Halima zuwan baƙon nan, amma ƙarshe seda ya fito da baƙin ciki da dana sanin zuwa sanar da saƙon nan.

Har kusan awa guda bata fito ba, Muratalah ne yaji tausayinsa ya bashi ruwa, dan da gani muyumin ya jigata kafin yazo, ita shaf tama manta da wani baƙo da akace tayi, ta shiryo tsaf abunta zata fita, har an ɗakko mata mota, Nura yace "Hajiya baƙonki fa"

A fusace ta juya zata yi masifa "wai wane jarababbem ne haka aka dameni dashi"

Muyumin yace "nine nan"

Tana waiwayawa ta zare ido ta dafe ƙirji tace "Na shiga uku, Shu'aibu!!!"

Abun duniya ya dami Yusuf, baccinma ya gagar ɗaukarsa, jin shiri yasa ya zata ko Widad tayi bacci, kwana biyu kenan basu kwanta manne da juna ba, duk yaji babu daɗi, a hankali ya lalaɓa yaje bayanta ya kwanta ya shiga bargon nata, ya rungumeta a jikinsa.

"Malam meye hakane? Ka lallaɓone kazo ka samu abunda kake so in anjima nace Allah ya bani ciki ka haɗe rai"?

Yusuf ya girgiza mata kai yace "Aa', É—umin jikinki nake son ji, dan Allah kimin afuwa Widad, ki saurareni please"

"Dan Allah nima ka ƙyaleni, wallahi bana son jin komai daga bakinka, lallaɓani zakayi in yarda da kai, in anjima kuma ka juyan baga"

"babu juya baya tsakanina dakw Widad, ina son ki fahimceni ne kawai, bari in baki labarin wani yaro"

Miƙewa take ƙoƙarin yi, tace "bana son ji, ka riƙe abunka"

"Dan Allah ki tsaya kiji, yana da mahimmanci sannan akwai darasin rayuwa a ciki"

Ganin bata da niyyar saurararsa yasa ya janyota jikinsa, ya rungumeta gam sosai yana ajiyar zuciya, a hankali taji ɓacin ran nata na raguwa, dan haka ta kwanta tayi shiru tana sauraren bugun zuciyarsa.

Yusuf ya nisa sannan yace "Labarin yaron nan zaki ji daÉ—insa sosai, bari in gayamiki abunda ya samu yaron.....

Mun kusa ƙarƙare part 2, idan part 2 kawai kika siya karki sake ayi 3 babu ke.

LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

98_99

"Akwai wani Mutum me suna  Bashir, shida matarsa me suna Jidda, wadda sukayi Auren soyayya, kusan shekara uku babu haihuwa, kin san yanayin ƙasar Hausa, abun ya kan zama abun damuwa koma gori ga matar da bata haihuwa.

Aka dinga ziga mutumin nan akan yaƙara Aure tunda bata haihuwa amma yaƙi, gashi babban ɗan Sanda yana matuƙar son matar nan tasa, yana da rufin Asirinsa dai dai gwargwado, matar nan tasa tana matuƙar kyautata masa shida 'yan uwansa dukda yadda suka tsaneta suka sata gaba, suna ganin komai ya samu akanta yake ƙarewa, gata da yawan larura Kasancewar tana da Athma, kuma genotype ɗinta AS ne, dan haka kusan kullum cikin rashin lafiya take da zaryar Asibiti, shi kuma yana jin tausayinta saboda mahaifiyarta bata raye, ga mahaifinta bashi da cikakkiyar lafiya shima.
Chapter 56 · 0% Book details