← Book details Akidata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 127

Sashe 65

Akidata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wataran suna sitting room ɗinsu Salma suna hira ita da Yusuf, ta sha ado se zabga ƙamshi take, suna ta taɗi ya miƙe ze tafi aka ɗauke wuta, aikuwa ta rungume shi tana kukan Shagwaɓa wai ita tsoron duhu take.

Yusuf yace "Salma ki cikani, kar wani yazo ya ganmu, amana mummunar fassara"

"Ni tsoro nakeji, tai maganar cikin Shagwaɓa tana sake kwanciya a jikinsa, ga wani ƙamshin turare da take yi, take jikin Yusuf ya fara tsuma, karo na farko daya rungumi mace a jikinsa, ya dinga jin wani irin yanayi yana bijiro masa, sheɗan na ƙoƙarin yi musu lalata, nan da nan yasa hannu ya raba Salma da jikinsa yai waje da saurin gaske.

Ko daya koma gida, ya sauya kaya ya kwanta ya kasa manta abunda ya faru, gaba ɗaya bacci ya ƙauracewa idonsa, tunani iri iri, a nan ya ƙara yadda da tabbas ya kai munzalin da lallai yana buƙatar mace a tare da shi, sedai waye ze tsaya masa, tunda harkar Aure dole seda uba, ko wakilansa.

Azumi ya gabato Yusuf yayi wa Salma siyayyar kayan Azumi, dana salla, Umma ba ruwanta da duk abunda ze siya ya kaiwa Salma, sema dai ta dinga yakamata ka ƙara kaza.

Ya haÉ—a sha tara ta arziki ya kaiwa Salma, Salma ta dinga murna tana godiya, Yusuf yana kashe mata kuÉ—i sosai.

Bayan kwana biyu mahaifinta yasa aka kira masa Yusuf, yace ya turo magabatansa ayi maganar Aure, tunda dai sun fuskanci juna, wahalar da yake ta isa haka.

Sedai Yusuf ya koma gida cike da zullumi a zuciyarsa, waze turo? Wa yake dashi banda Allah da Ummansa?

Bayan ya koma gida daya gayamata tayi murna, sedai itama kanta seda jikinta yayi sanyi, amma ta dake tace masa shikenan bakomai, Insha Allah za'a tura a tambayar masa, Yusuf be cikata da tambaya ba ya ƙyaleta.

Umma ta shirya ta tafi gurin Yaya É—an lami, ta gayamasa cewar dan Allah Yusuf ya samu yarinyar daze Aura ne, tana so ba dan ita ba su wuce masa gaba su tambayar masa Aure, Yaya É—anlami yace mata ai ba matsala, bakomai dan dai wannan, zasuyi zasuje su tambayar masa Aure.

Umma ta dawo gida tana ta murna tana farinciki, Yusuf ze Aure ze zama cikakken mutum shima kamar kowa.

Wataran ya dawo da yamma, daga gurin harkar furnitures ɗinsa, yazo ya tarar da cincirindon mutane a ƙofar gidansu, se gabansa ya faɗi ya zaci wani abune ya samu Ummansa, dan haka a guje ya ƙarasa cikin gidan yana ture mutane, yaje ya tarar da ita a zaune tana kuka, ga kayan daya saiwa Salma na Azumi dana salla, a baje a gabanta wasu mata suna cewa

"gayyar tsiya ashe bashi da uba, ya lallaɓo ze aurar mana 'ya, to Allah ya rufamana Asiri, seku koma gidan marasa iyaye inda aka ɗakkoshi, a ɗakko masa mata a can ba dai' yarmu ba, banda mutanen nan na kirki ne sunje sun gayamana, da haka zamu bawa mara uba 'ya, ai kema kin san bakiyiwa kanki adalci ba"

Yusuf ransa ya ɓaci, dan yau an masa tozarci mafi muni, dama abunda yake ta gudu kenan Umma takasa ganewa, maimakon a dawo masa da kayansa salin alin, shine seda aka tara wannan gayyar mutane sannan za' aci zarafinsa haka, kuma ma dan baƙin ciki akazo akasa mahaifiyarsa a gaba da cin mutunci kuma aka cika gidan kamar wanda sukai sata ko maita, cikin tsananin ɓacin rai da juriya, Yusuf ya kalli Matan yace "mun muku laifi, Allah ya baku haƙuri, tunda kun gama abunda zakuyi, zaku iya fita"

"Ai dole kace haka mana, tunda ka lallaɓo zakayi cuta, yarinya da samarinta na arziki amma zaka cuceta, yarinya 'yar dangi kyakkyawar gaske"

"Wallahi idan kika kuma gayamin maganar banza sena wanka miki mari, get out from here"

Yadda yayi maganar a fusace ne yasa jikinsu na rawa, sukayi waje dasu da gayyar mutanen da suka cika gidan, anata ƙananan maganganu, wai ashe duk girman kan nasa ma bashi da uba, yana taƙama da wannan kyan nasa yana hura hanci, ashe ma shegene.

Yusuf be cewa Umma komai ba, ya tattare kayan yaje ya ajiye, ya wuce É—akinsa ya kwanta, zuciyarsa na masa wani irin raÉ—aÉ—i mara misaltuwa.

Umma tasan ba kowa ne yaje ya gaya musu wannan maganar ba face su É—anlami, tayi danasanin zuwa ta samesu akan su wucewa Yusuf gaba akan harkar Aure, yanzu shikenan baza'a auri É—anta ba saboda wannan dalilin? Dukda tarin nagarta dayake da ita.

Tun daga ranar ko hanyar gidansu Salma ,Yusuf be ƙara biba, ba damar ya fita ko yazo wucewa se yaji ana yada masa da maganganu marasa daɗi, ya goge lambar Salma, da duk wani abu daya shafeta.

Sedai hakan ya zame masa tamkar wani ciwo a ransa, Yana kewarta saboda sun shaƙu sosai.

Wataran ya fito ze fita aiki ya ganta a ƙofar gidansu, ya ɗauke kai ze wuce amma ta sha gabansa tace "Gurinka nazo"

Yusuf ya kalleta yace "meyafaru sauri nake"

"Yusuf, ni kaina banji daɗin abunda akayi maka saboda ni ba, ban san haka abun yake ba, amma abun yafi ƙarfina ba yadda na iya, dan Allah kayi haƙuri, kuma ka bawa Umma haƙuri, ga katin ɗaurin Aurena nan, ina buƙatar addu'arka, kuma ina fatan ubangiji Allah ya baka wadda ta fini, komai da komai nagode da lokacin ka Yusuf "

Ta zira masa katin É—aurin Auren a gaban babur É—insa, ta juya tana share hawaye, shiba katin Aurenta nema ya dameshi ba, kukan da take ne ya bashi tausayi.

Gaba ɗaya ya rufe babin Salma a rayuwarsa, ya koma rayuwarsa sedai mikin nan baze taɓa barin zuciyarsa ba.

Yusuf yayi ajiyar zuciya sannan yace "ko wata biyu ba'ayi ba da abunda ya faru, aka bani aikin nan akanki, da farko nace ba zanyi ba, amma Abbas ya takurani, saboda wai ina da haƙuri, sedai ranar farko dana fara tozali dake, dukda isarki da izzarki, duk da jan aji da wulaƙancinki, se da naji zuciyata tayi bugun da bata taɓayin irinsa ba, ga kwarjininki yasa na kasa haɗa ido dake, ban shirya ba banyi tsammani ba na shiga kokawa da zuciyata akan Sonki da take, na nemi 'yar talakawa ma ban samu ba, saboda rashin asalina, ina ga ' ya kamarki, me Asali me dukiya gashi uwa uba naje a matsayin direba, se akanki na tabattar da Biyayya ce da shaƙuwa tasa na karɓi Salma a wancan lokacin, Amma wannan karon zuciyata ce da kanta ta zaɓi abunda take so, Widad bani da tabbas idan Dagaske Umma take na cewar, hatsari iyayena sukayi aka jefoni ta taga, nasan zata iya gayamin hakan dan hankalina ya kwanta, amma zance mafi yawa shine a gidan marayu aka ɗakkoni, Yanzu zaki yadda ki haɗa zuriya da mutum irina? Ki haihu dani alhalin bani da dangi se Allah se Ummana? Ni ba ina gudun haihuwa bane, nima ina fatan ganin jinina a duniya, amma kinji dalilina Auren nan kansa da mukayi a cikin zullumi nake Widad, ni dai nasan ina sonki amma bani da asalin da za'a nuna, nasan Ko Daddynki baze amince ba Widad, tuntuni nake zullumin gayamiki wannan labarin nawa, zaki zauna dani a haka?, ina sonki Widad, akanki na fara jin shauƙin soyayya, naji zan iya duk wata sadaukarwa saboda ke, dan Allah kar rashin iyayena yasa ki gujeni, ina sonki Widad ni kaina ina mamakin son da nake miki"

Ya ƙarasa maganar yana kuka, shaɓe shaɓe da hawaye kamar mace, Widad ta ƙanƙameshi itama tana kukan, ta rungumeshi kamar jariri a ƙirjinta, ta dinga shafa sumar kansa tana

"Am sorry Yoseef, am sorry kayi haƙuri please"

Kamar ta ƙara tunzura Yusuf, kuka yake sosai harda sheshsheƙa, da alama abun yana cin zuciyarsa.

Tana kuka take cewa "Yoseef dan Allah kayi haƙuri, ka dena kukan nan haka please"

Ya girgiza mata kai yace "ki ƙyaleni inyi inji sassauci a zuciyata Widad, ban taɓa yiwa wani kukan rayuwar da nayi ko na tashi a ciki ba seke, i need a shoulder to cry on, ƙyaleni inyi matata"

Widad ta rungumeshi tana kuka, tana tausayawa irin rayuwar da suka yi, dan daga ita har Yusuf kowa yaga rayuwa, kowa da irin ƙaddarar daya fuskanta a raguwarsa, amma na Yusuf ya ratsata sosai, ya bata tausayi matuƙa, ya wahala a rayuwarsa.

"zan rayu da kai a duk ya kake, zan karɓi kowane ƙalubale daze taso saboda kai, ina son Aurena Yoseef, ina son zama da kai, ba ruwana da waye kai, nagartar ka da gaskiyar ka sun wadatar dani, stop crying my Husband, nima ai kana gani ba dangin ne dani ba, daga Allah se Babana, duk dangin babu, dan haka ina so mu zama ɗaya mu samar da family nida kai, ka dena kuka mijina "

TAMMAT BI HAMDILLAH, NA KAMMALA KASHI NA BIYU ZAN SHIGA NA UKU, WANDA SHINE NA ƘARSHE DA YARDAR ALLAH

LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel É—ina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"
11/15/21, 4:53 PM - Buhainat: LITTAFIN KUÆŠI NE, DAN ALLAH KI SIYA KAFIN KI KARANTA BA DANNI BA DAN ALLAH, LITTAFI NA ÆŠAYA KYAUTA NE WANNAN NA SIYARWA NE
NORMAL GROUP ₦300
VIP ₦500 NE KITURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0009450228
JA'IZ BANK
AISHA ADAM
SE A TURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR
07063065680
IDAN KUMA KIN SIYA AMANACE KARKI FITARMIN DAN ALLAH 🙏🙏🙏

(Albishir ga masoya, ma'abota bibiyar litattaafaina, dama ta samu zaku fara samun litattaafaina na audio, akan YouTube channel É—ina me suna Cool Arewa TV
https://youtube.com/channel/UCD5vnvA5laU8ti4LLz2_QEg

Kuyi liking sannan ku danna subscribe, domin fara samun litattaafaina na audio, nagode sosai da ƙaunar ku gareni"

106_107

Yusuf ya sake ƙanƙame Widad yana cigaba da zubda hawaye.
Chapter 65 · 0% Book details